Showing 87001 words to 90000 words out of 138998 words

Chapter 30 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

746

mutunci ta ya zaki wulakanta babban mutum kamar Jibril a gaban mutane”

“Babu ruwanka karka saka min baki a nan”

Jibril ya share hawayen da suka ki tsaya masa ya nufi gurin Noor sai ta tsaya masa tsawa hawaye na zuba a idanuwanta.

“Karka taba min yaro”

Rike shi Doc Ismail ya yi ya ce da Nurses din su wuce da Noor, a gurin Nawwara ta zube kasa saboda jirin da ya dibeta, Doc Ismail ne ya kira wasu Nurse suka kamata suka mayar da kin da ta baro. Hakan ya bawa Jibril damar shiga dakin da aka kai Noor. Ko da ya shiga ya samu Nurses din suna daurashi saman gadon sannan suka saka masa robar jini daya. Fita suka yi daga dakin baya sun gama komai sai Jibril ya karasa inda yake ya durkusa kasan guiwowinsa gurin gadon wasu sabbin hawaye suna zubo masa.

Ko da bachi yake ya farka ya kalli Noor yasan dan sa ne, fuskarsa ce shinfide a fuskar Noor babu inda Noor ya rage shi da komai, hannu ya kai ya rika hannun Noor sai yaji wani irinsa ya shiga hannunsa jini ya hadu da jini Noor din ma da be san inda hankalinsa yake ba sai da ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi.
Kuka Sosai jibril ke yi irin kukan da aka san mata da yinsa, sai kuma yaja hannun Noor ya kai a fuskarsa ya lumshe ido, yana ta goga hannun a fuskarsa, sannan ya yi masa kiss sai kuma ya soma shinshinar hannun kamar zai cinyeshi.

“Am sorry Son, ka yafe min na wulakanta akan haukana, mahaifinka ya tuba ya gane kuskurensa na yi nadama, ban san miya shiga kaina ba ban san miyasa na aikata ba, am really sorry for what i did, please forgive me”

Ya kara fashewa da kuka har numfashinsa na son tsayawa, shigowar Doc Ismail ne yasa shi tsagaita kukan ya dago ya kalleshi.

“Wai miyake faruwa ne? Miye alakar ka da wacan matar ne? Na san dai wannan ba dan ka ba ne ko?”

Tambayar da Doc Ismail ya yi masa kenan.

“Dana ne, ita kuma mata ce”

Daga haka Doc Ismail be kara cewa komai ba, yasan Jibril baya cikin yanayin da zai iya yi masa bayanin komai a yanzu, after that be kama ya saka kanshi akan matsalar iyali ba. Juyawa ya yi ya fice zuciyarsa cike da mamaki bakinsa kuma gumde da tambayoyi.


NAWWARA POV.

Ban san iya awanin da na dauka a sume ma ba, ina farkowa na ji goshina ya cika da nauyi har bana iya gani sosai.

“Sannu”

Muryar Inna ce take gaisheni sai na gyada mata kai dan bana iya magana a wannan lokacin, na dade ina kallon silin sannan idanuwana suka dawo daidai har ya kalleta.

“Ina Noor?”

“Yana can an kaishi wani dakin”

Sai a yanzu na tuno da abunda ya faru, ashe fa wannan suma ta biyu ce na yi.

“Inna miyasa kike bari Jibril ya zo har ya ga Noor”

“Ba zan iya ce miki ga dalilin zuwansa ba, ban kuma san ta ina ya ji ba, nima na tafi neman jini ko da na dawo na tarar ya bada jininsa kuma ya sa an canja miki daki an dawo da ke a nan, shi kuma yasa aka kai shi dakunen nan masu tsada”

Na yi sauri sauka saman gado duk da ina jin jikina kamar babu gwari sosai. na fita daga dakin na mike hanya har na isa manyan dakunan, na bude na farko ba shi bane na biyu ma haka na uku hudu biyar haka na bi dakunan sai da na kai daki na bakwai ina turawa sai na hango Noor kwance Jibril kuma zaune saman kujera ya dora kansa gurin jikin Noor hannun Noor kuma a saman kansa dayan hannunsa kuma na sanye cikin na Jibril.

Ban damu da na rufe kofar ba na karasa kusa da gadon cike da tausayin halin da Noor yake ciki, ina tsayawa dai dai kan Jibril sai ya bude idanuwansa da suka kumbura suka ja a hankali ya kalleni, sai kuma ya lumshe.

“Jibril tashi ka fita”

Na fada a tsawace, sai ya bude ido ya yi ma hannun Noor kiss sai ya sake shi, na yi zaton tsaye zai tashi sai kawai na ga ya zube kasan gwuiwowinsa ya fashe da kuka yana hade hannayensa.

“Ki dubi girman Allah Nawwara, ki sassautawa zuciyarki dan Allah ki yafe min, Wallahi na canja dabi'u da halayya duka na canja ki ceci raina kuma ki ceci ran yarona ki taimakeni ki yafe min ba ni da wani buri da ya wuce na ki da na wannan dan nawa, please Nawwara for the sake of our Son ki hakura mu sake sabuwar rayuwa, zuciyata na cike da kuna ina bakincikin abunda na yi muku, kaina a kasa yake ki taimaka min ki bani damar da zan gyara laifina, ba ni buri sai na ki, ki min masauki a gefen zuciyarki dan Allah Nawwara”

Hawaye na zuba a idanuwansa yake min wannan rokon da ya soma karyar da zuciyata, nima na fara hawaye.

“Bata lokacinka kawai kake Jibril, ka fitar da ni a ranka ka manta da ni a duniyarka, kai ba tsarata ba ne, na rumtse ido daga kallo duk wani abu da ya shafi rayuwata”

“Ji ceci rai Nawwara, idan yanzu na fadi na mutu ke ce sila, ki taimaka ko dan dan mu”

“Dan mu? Ko da na? Dan da ka ce ba naka ba ne? Ka wulakanta ni saboda cikinsa? Dan da tun da ka turo ni gidanmu ba ka taba saka kafarka ka zo duba shi ba? Dan da baka san cin sa ba baka san shansa ba? Dan da baka san ya rayuwarsa ta ke ciki ba? Dan da ka kasa yankawa ragon suna kasa a ka kirashi da shege? Mahaifina shi ya yanka masa rago ya saka masa suna, yanzu har kana da bakin da zaka kira shi da danka? Kana da idon da zaka zo rana tsaka ka kalleshi kuma ka fada masa kai ne mahaifinsa? Ta wace fuskar zai kalleka? Taya zai kiraka Uba?”

Tun da na soma magana ya rumtse ido ya matse hannayensa da ke hade guri daya yana cizo baki, da alama maganar tawa bata masa dadi, sai kuma ya dago fuskarsa da ta yi ja ya kalleni.

“Fada min abunda zan yi wanda zai sa ki yafe min, fada min tafarkin da zan bi Noor ya karbe ni a matsayin ubansa? Taimakeni Nawwara, ki tausayawa rayuwata zan yi komai kike so am ready to die for you”

“Ka wuce sanina Jibril, kaje ka nemi matar da zata so ka ta aureka ta haifa maka yaya, shawara daya zan baka kaje ka yi abunda zai taimaki rayuwarka ina maka fatar samun irin matar da kake so Allah baka sa'a”

Mikewa ya yi tsaye ya fice cike da nauyin kafafu, ba tare da ya share hawayen da ke fuskarsa ba. Ni kuma na zauna kusa da dana ina kukan da ban san na minene ba, tausayin da na ko kuma rayuwar da na cinci kaina a ciki.?


Bayan sallah isha'i Jidda da mahaifiyarta suka zo duba Noor, daman tun da magariba wasu daga cikin mutanen babban gida suka zo duba shi. Bayan fitarsu sai ga Bilal ya shigo hannayensa da ledoji har gudu hudu har kuma lokacin Noor be farka ba gaba daya hankakina ya tashi duk da likitan ya fada min zai dauki tsawon lokaci yana bachin. Kallo daya na yi ma Bilal na kawar da fuskata, bana ganin komai sai wacan abun da ya faru shekaranjiya wani irin kishi da bakinciki sai suka taro min har na ji kamar na dauki wukar da aka aje ta yanka lemu na daba masa a kirji.
Da Inna ya fara gaisawa sannan ya gaishe da wata abokiyar Inna suka gaisa da Sakina, sai duk suka tashi suka ba mu guri, daya ya zama daga ni sai shi sai kuma Noor da baya cikin hayyacinsa.

“Nawancy... Wallahi ba abunda kike tunani ba... ”

Hannu na daga masa

“Kai ko Zinatu ko wani abu da ya shafi rayuwarku a yanzu be dame ni ba”

“I know i shouldn't, ya jikin Noor?”

“Da sauki”

“Allah ya kara sauki”

“Amin”

Bayan wannan bata maganar bata sake shiga tsakanin mu, da ya gaji da zama ne ya mike tsaye ya karasa kusa a Noor cike da nuna kulawa ya duba shi sannan ya kalleni ya ce

“An kama wadanda ya kade sa?”

“Ya gudu, amman mutane sun ce da gangan mutumen ya yi cikinsa da mota ya kadesa, kuma likitan ya ce min Noor ya karye a hannu”

Na fada ina fashewa da kuka.

“Sorry a wani waje ne?”

“Sun taso makaranta ne, mutunen ya gudu”

“Amman Mahaifinaa ya sani?”

Wani kallo na watsa masa na sakar masa idanuwana ina ta kallon fuskarsa cike da tsanar furucinsa.

“I mean Jibril”

“Kaima kana cikin mutanen da je ganin laifina akan Jibril ko?”

Yayi saurin komawa ya zauna.

“No ba hakan na ke nufi ba, Jibril ya wulakanta ki Nawancy kuma ya cancanci ko wane irin sakamako daga gareki, Wallahi ko ke ce baki da gaskiya i will support you ballantama kina da gaskiya, kawai bana son abubuwa su miki yawa ne, tunani a yanzu ba na ki ba ne, ki sassautawa zuciyarki, kuma ki rika neman shawara akan abunda ya shige miki duhu”

Na share hawayena na maida idanuwana gurin da na, sai na cinkayo muryarsa yana fadin.

“Ni kaina ban san ranar birthday dina yayi ba, sai a Facebook, su suka turo Zinatu kuma friend dita ce a fb few weeks ago ta turo min friend request na yi accepting ba tare da tunanin komai ba, ta yi min happy birthday tun ana saura kwana daya na yi birthday na, ina tunanin ta nan ta gane xan yi birthday a ranar har ta siyo wannan cake din, ina zaune ta shigo da shi ta kira abokan aikina ban ma san ta kira ki ba sai da na ganki office din”

“Mi zai sa ta yi haka? Daman can tana son ka?”

“Gaisuwa bata taba shiga tsakanin da Zinatu ba, idan har kiga na mun hadu sai idan aiki zamu yi, ina tunanin ta yi hakan ne saboda ta shiga tsakaninmu ko kuma...”

Sai ya yi shiru be karasa ba.

“Ko kuma me? Jibril ne ya sata ko? Zai iya saboda mugu ne”

“Ni dai iya abunda na ke son ki sani, ba zan taba cin amanarki ba”

“Amman miyasa ka yi blocking din number ta? Kuma ina ta tura maka sako baka min reply”

“Saboda na baki damar yin tunani da zuciyarki, ina ganin kamar ina kan hanyar da ba zata bulle ba ne, zuwan Jibril a karo na biyu cikin rayuwarki ya karyamin kuzari, bana son na shiga tsakanin farincikinki da kuma tunaninki, bana son na yi abunda zai raba hankalinki gida biyu, na yi hakan ne saboda na daga miki kafa kuma na samawa rayuwata mafita saboda bana so na rasa a take, zuciyata na raya min kamar ba zan aureki ba Nawancy, kin ki bani damar da zan ga magabatanki kuma gashi Jibril zai yi duk abunda zai yi wajen ganin ya mallakeki”

Tausayinsa ya kamani, duk da kasancewar ni ma ina tausayin kaina.

“Kokarin mallakata yake Bilal kai kuma tuni ka malleke zuciyata, idan har Nawwara bata auri Bilal ba to ban cancanci auren ko wane irin namiji ba a duniyar nan, na fara rayuwa sau daya sai kuma na mutu, kai ne ka dawo da ni duniyar da mutane suke rayuwa, ka yi nasarar canjani daga mutum mutume zuwa mutum wacce ta san mi ake nufi da rayuwa, na rayu a lokacin da rayuwa take da muhimmanci a gareni, sai Jibril ya kashe min ruhi kuma ya kona shi ya maidashi toka ya shekarda da shi ya bi iska, kai ne mutumen da ka hada tokar ruhina ka tattarata ta sake zama cikakken ruhi na maida shi a cikina, har zuciya ta bude ta kamu da son ka.

Kai ne kadai mutumen da nake so Bilal kai ne mafarkina, burina idan har ka ga ban aureka ba ka tabbatar gawata ce ta ke magana ba ni ba”

Lumshe ido ya yi ya hade yawu sannan ya bude kamar dai be yarda da ni ba, sai ya mike tsaye yana fadin.

“Idan kina bukatar wani abun ki fada min, ko ki kirani, ina son ki san da wannan Nawancy ina sonki sosai ina kaunarki kauna ta hakika”

Da kallo na bishi har ya fice, sannan na juyo ina share hawayena na kalli Noor da ke motsi.




_______________________________

I dedicate this chapter to my wattpad people 😘😘😘
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @KhadeejaCandy


4⃣4⃣

Bayan fitar Bilal su Inna suka shigo tare da Mama Turai wato Yayar Inna wacce suke uwa daya uba daya. Inna ta zauna saman tabarma ita kuma ta zauna saman kujerar da ke gefen gadon ta Kalli Noor sannan ta kalleni ta ce.

“Innarki ta labarta min komai, kuma abunda kike ba ki kyautawa, tun da har ya tuba ya dawo ya nemi ganin dansa ai sai ki bashi dama, ke yanzu in ban da Allah ya nufa ko hanya kin isa ki hada da babban mutun kamar wannan balle har ya zo yana rokonki? In wani ne karbe dansa zai yi da karfi ya barki nan, kin samu ya dawo yana neman yafiyarki kina ta masa wasa da kwakwalwa kamar karamin yaro”

Na tada kai na kalleta.

“Ke ma laifina kike gani ko Mama Turai?”

“Ai dole na ga laifinki, mutumen arziki irin wannan mai kudi haka, ai sai ki bashi dama ko arzikin nasa ku tatsa ni Wallahi da yana son yata da na aura masa mu ga karshen iskanci”

“Amman yanzu har kun manta irin cin mutuncin da cin zarafi da ya yi min?”

“Yanzu ba ya dawo ya tuba ba? Ai Allah ma mukan masa laifi ya yafe mana balle ke da wani be san da zamanki a duniya ba, ke kikan irin laifin da kike yi ma Allah ne?”

Idanuwa sun cika da kwalla saboda na san babu wanda zai fahimce balle ya goya min baya, ni kadai na ke jin abunda na ke ji wata kila saboda ni Jibril ya yi ma abun ba kowa ba. Wannan karon Inna ce ta dora da

“Idan har sakamakon Ubangiji kike so tau ko ya kamata ki mika lamurranki gurinsa, ba yin kanki ba ne Allah ne ya jarrabeshi da sonki kuma ya saka masa nadamar abunda ya yi saboda ya jarrabeshi, ki yanzu ba jindadinki ba ne mutumen da ya ce Noor ba dan sa ba ne yanzu har yake risina miki kasa yana neman ki hada shi da dansa? Allah yana son masu yafiya, kuma ba a rama cuta da cuta sai dai a maye cuta da alheri, ina ji miki tsoron kar wannan abun ya dawo kanki, kuma da Noor ya girma ya nemi ubansa ai kara ya girma da Ubansa”

Ganin yadda na ke sharar kwalla yasa Inna ta taso ta dafa.

“Na san ya cutar da ke yata amman karki mata shi ma Allah ba zai barshi ba, kuma ba kisan halin da ya shiga ba kamin ya gane cewar ke alheri ce a gareshi, ba dan Jibril yana da arkizi na ke son ki yafe masa ba, sai dan hakan zai wanke ki daga zargin da duniya take miki, kuma Noor zai samu rayuwa mai kyau, ke kuma zaki samu damar gina taki rayuwar a gidan aurenki idan kika auri wanda kike so”

Bani da wani zabin na yafiya ga Jibril saboda yadda Inna take son na yafe masa din, na kan yi kokarin yin abunda duk mahaifiyata take so ko kuwa abun nan baya min dadi, ba dan komai ba sai dan na san ba zata cutar da ni ba, kuma yarda Allah tana tare da yarda iyaye, na yi ma uwar wasu biyayya ma balle tawa uwar wacce ta dauki ciki ta yi nakuda ta haifeni ta raineni na girma, hakika bana da wani farinciki sai na mahaifiyata.

“Zan yafe masa Inna matukar yafe masa din zai faranta ranki, zan yafe masa”

“Na jidadi Allah ya miki albarka kema ya baki yayan da zasu yi miki biyayya”

Ajiyar zuciya na sauke na share hawayen da ke min zuba ina kallon Mama Turai da ke wasar baki.

“Haba ko ke fa, amman ace zuciya kamar ta kafiran farko, Allah ya shiga ya tsakaninku ai mun fi son a shirya”

“Dan na yafe masa ba yana nufin zan aureshi ba ne, dan Allah karku tirsasamin yin wani abun daban kuma”

“Babu wanda zai tirsasa miki, wata rana ke da kanki zaki karanta mana sirrin zuciyarki”

Cewar Inna, ni kuma na kalleta na ce

“Zuciyata bata da wani sirrin bayan wanda ke zahiri ke kanki kin san babu wanda na ke so bayan Bilal, be kamata ki zargeni da son wani bayan shi ba”

Sai  Mama Turai ta taso ta karaso kusa da ni tasa hannunta ta tallafo fuskata yadda zan fuskanceta.

“Tausayin Bilal kike Nawwara amman asalin son yana gurin Baban Noor, ke kanki ba ki san abunda ke damunki ba a yanzu, kina tausayin Bilal amman ba za ki iya aurensa ba, kaddarar da ta hada ku ba zata iya bari ku yi aure ba, saboda ke makwafin RAI BIYU ce a gurin Baban Noor idan babu ke koda ya samu Noor rayuwarsa bata kammaluba, haka ma Noor kina matsayin RAI BIYU a gunsa matsayin uwa kuma uba, babu rabon Bilal a jikinki shiyasa kika kasa bashi dama, Baban Noor kuma be da rabo a jikin kowa ce mace sai ke shiyasa kaddara ta sake hada ku kuma zuciyarsa ta kasa barinsa zama lafiya har sai ya nemo mata yar'uwata, ke ma kuma baren zuciyarki yana gurin Noor da Babansa wannan yasa har gobe ba zaki iya amsa kanki a matsayin cikakiyar mace mai jin kanta a mace ba, kika kasa bawa kowa damar sake aurenki gashi Baban Noor ya dawo.

Wani baya auren matar wani Nawwara, da kika auri Faruk baki haihu da shi ba ya mutu ya barki saboda Baban Noor ya samu damar sake aurenki, ko da kin haihu da Faruk sai kin fito saboda kaddara ta yi niyar hadaki da tsohon mijinki Nawwara, kurciya ce take cin ki ke kanki yanzu baki san abunda kike so ba, da yanzu za a daura miki aure da Bilal da ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login