Showing 39001 words to 42000 words out of 138998 words

Chapter 14 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

740

Allah ya waye kuma ya aiko ganinki shine zaki mayar masa da kayansa? Wannan wace irin rayuwace Nawwara? Mi yake damunki? Wulaƙanta ɗan'adam? Kuma mutun kamar Mustapha yaron da babu wanda ya isa ya nuna masa ɗan yatsa amman har kike ƙoƙarin ci masa zarafi?”

Yanayin fuskarta da kuma lamanta na fahimci ranta ya ɓace sosai akan abunda na yi, ni kuma na marairaice mata kamar zanyi kuka.

“Inna kin san waye Mustapha ana yaba masa da neman matan banza, dan me zai kawo min abu na karɓa, bayan ban san manufarsa a kaina ba”

Ta ƙaraso kusa da ni

“Shiyasa na ke son ki lallaɓa da shi ku rabu lafiya, da baki watsa masa kayansa ba sai ki amsa ki masa godiya in yaso daga baya sai ki nemi ya rabu da ke”

“Zan kiyaye nan gaba”

Da wannan muka raba na nufi murhu na cigaba da hura wuta, ita kuma ta koma ɗaki tana cewa Sakina ta zo ta siyo mana ƙosai. Har na dama kumun tunani ɗaya ne a raina, na faɗawa Inna gaskiya game da Mustapha ko kuma na barwa cikina, idan ma na faɗawa Inna amfanin me zai mata? Idan kuma na bari ban faɗa ba ni amfanin me haka zai min?
Ina cikin wannan tunanin naji muryar Namiji yana sallama a ƙofar gidanmu, bayan naji tsayawar mota da kamar minti huɗu, dakan uku-uku gabana ya yi duk da ban san ko wanene ma. Ko da na bar gaban murhun Jamila har ta kai waje, sai gata ta dawo da sauri tana kirana.

“Anty wai ki zo ana kira a waje”

“Waye?”

“Wanine”

Mustapha na fara kawowa a raina, amman da shi ne ai Jamila ta sanshi da shine ai ba zata ce wani ba. Miƙewa na yi tsaye na tare da bokitin da na dama kunun na nufi ɗakin Inna na aje mata sannan na ɗauki Hijabinta na saka na nufi ƙofar gida gabana sai faɗuwa yake musamman da na yi arba da mutumen dake sanye da rigar kamfanin da kuma hularsu, tun kamin na masa sallama shi ya fara min tare da faɗin sunana.

“Khadija Musa Kafinta”

“Sunana ne”

“Zaki saka hannu a nan sai na baki saƙon da aka aiko miki”

“Bana da buƙata ka mayarda saƙon, kuma ka faɗawa shugabanku ya dakatar duk wani saƙo da suke aiko min bana da buƙata”

Sakin baki mutumen ya yi yana kallona, kamin ya barshi tsaye a gurin nayi shigewata, zuciyata cike da tunanin abunda ke cikin saƙon a lokacin na riƙa da na sanin ƙin karɓa da na yi domin sosai na so naga abunda aka rubuta, sai dai kuma ta wani babin bana da buƙatar duk wani abu daya dangancin Jibril idan har na saka masa fuska tabbas zai sake nuna wasa da ni kamar yadda ya yi a baya.

Wani mugun murmushi na samu kaina da yi lokacin da na tuna hawayen da na gani a fuskar Jibril, ashe zai iya zubar da ƙwalla saboda ganina har ya riƙa hannuna ya shafa a fuskarsa, mace da ya ce kashe yafi ta daraja a gunsa, lallai akwai babban labari a cikin hawayensa, domin ba kasafai Jibril ya ke nadama akan abunda ya aikata ba.

“Kee... Lafiya kike murmushi ke kaɗai kuma?”

Tambayar da tayi min ta dawo dani daga duniyar tunanin da na tafi har na yi dariya na matsa kusa da ita na rumgumeta.

“Ina sonki sosai Mamana”

“Waye ya zo yanzun kuma?”

“Daga kamfanin da nake aiki ne, suka aiko saƙo amman ban karɓa ba”

“Saboda me?”

“Nasan babu komai a ciki sai wulaƙanci”

“Ai da kin karɓa kin duba wata ƙila zai miki amfani”

“Ya riga ya tafi”

“Allah ya kyauta”

Sai duk muka amsa da Amin. Bayan mun gama karyawa, su Sakina suka shirya suka tafi makaranta tare da Noor, sai dai gabana nata faɗuwa saboda ina ganin kamar wani abu zai faru da ɗana. Sai da suka je makarantar suka dawo sannan hankalina ya kwanta.

Can da yamma sai ga Jidda ta shigo gidanmu da manyan ledoji, daman ta saba a duk lokacin da nake rashin lafiya sai ta riƙo min wani abu take zuwa gidanmu dubani, sai dai abunda ya ban mamaki siyayar da ta yi min ta fi ƙarfin Jidda duk da nasan sun fimu rufin asiri. Bayan sun gama gaisawa da Inna ta ƙasaro inda nake zaune ta dire min ledojin tana zolayata kamar yadda ta saba.

“Gawa ta ƙi rame, kin ƙi ki mutu mu ci gado”

“Mutuwata ba yanzu ba yarinya sai ke da danjinku kaf kun ƙare”

Sai duk muka saka dariya har Inna dake ninkar kayan da na wanke ɗazu na su Jamila. Mun sha fira sosai da Jidda daga bisani na tambayeta inda ta samo wannan kayan domin ita kanta tasan na san wannan kayan yafi ƙarfinta, bata ɓoye min komai ba ta faɗa min daman can Jidda bata ɓoye min komai.

“Wallahi Mustapha ne ya kawo ya ce idan zanje na riƙa miki wannan, wai kar nake hannu sake, daman ina ta tunanin abunda zan riƙo miki dan bani da kuɗi kuma bana son zuwa haka nan”

“Daman kuna waya da shi?”

“A'a ɗazu dai ne ya zo yake tambayata jikinki kuma ya bani number wayarsa wai idan zanje dubiyarki na faɗa masa, shine fa ya kwaso min wannan kayan”

Bana son Jidda ta zargi wani abu, hakan yasa ban ƙara masa wata tambayar ba, sai kawai muka ɗauko wata firar. Sai da aka kira sallah magariba sannan na rakata ƙofar gida ta wuce tana mintar rashin adalci na mai kamfanin da nake aiki, domin na labarta masa cewar ya koreni.

Tun daga wannan ranar kullum sai Mustapha ya aiko da saƙon a gidanmu da sunan ganin lafiyar jikina, wasiƙar gurin aiki kam kullum sai tazo gidanmu bayan ta waya da ake aiko min, tun Inna na lallaɓa na koma aikin har ta gaji ta zuba min ido domin ta fahimci ba zan koma ɗin ba, na kan faɗa mata ni bana son aiki a kamfanin ne saboda dokokin kamfanin. Bilal ma ya yi mamaki matuƙa ji da ganin yadda kamfanin yake neman na koma aikin bayan ance an koreni, shi da kansa yake faɗa min ko da harkar kasuwanci kanfanin zai ƙulla da kai da zai ci riba matuƙar suka koreka ba zasu nemeka ba balle kuma ma'aikaci, babu irin tambayar da bai min ba akan ko nasan wanine a kanfanin amman na nuna masa ni bansan kowa ba har ma na yi masa iƙirarin cewar ai na fada cewar ban yafe Haƙƙina ba wata ƙila shiyasa suke son na dawo aikin.

Sam ban taɓa ɗaukar lamarin Mustapha azimun ba ne sai yau da mahaifiyarsa ta zo dubani, ita kanta Inna mamaki ya cikata kuma ta ɗan tsorata da lamarin kamar yadda nima nake ta almarar abun tare da tunanin abunda yake ƙoƙarin aikatawa. Kana ganinta kasan zuwan cilas ne domin ƙyamar gidanmu take sosai, zama na sai ya gagareta sai wani kallon gidan take a hankaɗe a tsaye ta yi min ya jiki ni kuma na bawa banza ajiyarta har sai da Inna ta amsa ta tana ta ƙoƙarin kareni, saboda ta tsarku da yadda na share Hajiyar a tsaye ko gefenta ban kalla ba balle har na iya gaisheta.

“Iska ne da ita abubuwan ne sai a hankali”

Ta taɓe baki tana gyara tsayuwar gilashin idonta.

“Daman Son ne ya faɗa min akwai yarinyar da kai asibiti yana son na zo na dubata, ni zan wuce”

Ko sakon biyar bata ƙara a gidanmu ba ta fice tana wani irin taku na ƙasaita Inna ta bita tana masa godiya, ni kuma na bita da harara, daman ba zan lissafata a cikin mutane mn da suka mana gaisuwar Habiba ko Baba ba duk da bana iya tantance kowa da kowa amman da tazo da dole wasu zasu ganta ko da ba ni ba, gashi tsanar ɗanta ya dasa nin tsanarta musamman yanzu dana fahimcin bana sha'awar mutane irinmu.
Inna na dawowa daga rakiyarta ta cire takalmin ta buga min a kai, kana ta nuna ni da shi tana faɗin

“Allah ya canja miki wannan baƙin halin da ya taso miki, ai ba ita kika kunyata ba ni kika kunyata”

Tana faɗar haka ta nufi ɗaki ranta a ɓace, rabon da Inna ta ɗauki wani abu ta dakeni tun ina junior high school lokacin da na zo wani hutu, amman yau gashi ranta ya ɓace har ta buga min takalme a kai saboda ɓacin rai. Tashi na yi na bita ɗaki na bata haƙuri tare da shaida mata ba zan sake sannan muka shirya da ita har ma tayi min bitar zaman da mutane da kuma taka tsantsan na ka samu ka rabu da kowa lafiya.

Haka muka zauna muna ta fira har su Noor suka dawo daga makarantar allo na tura masa karantunsa ya wanke allon yana ta murna wai malaminsu ya ce ya iya idan yaje gida ya wanke allo gobe yi masa wani rubutun. Bayan sallah magariba Bilal ya sallamomin kamar yadda ya saba sai dai yau sallamar tasa ta musammance domin firar kansa yake min wai mutane nata maganar ya kamata ya yi aure har da ƴan gidansu, ni dai murmushi kawai nake inda kuma ya kamata na yi dariya sai nayi dariya, har muka rabu beji wata kalma da yake zato daga bakina ba, hasalima ban barshi ya daɗe kamar yadda ya saba ba ganin inda akalar labarinsa ya dosa a yau.

Misalin tara da rabi muka kulle gidanmu bayan mun gama fira da Bilal, na bawa Sakina ta kai min wayata maƙota saboda na samu caji, sai na alwalar na shigo ɗakin Inna na yi sallah isha'i, sannan na shiga na gyarawa su Sakina gurin kwanansu, ni kuma na dawo ɗakin Inna domin a yanzu na daina barinta tana kwana ita kaɗai.
Saman gado muka haye ni da Inna Noor na bayana daman duk inda nake kwana a nan yake kwanan, na yi matashin kai da fillon Habiba kamar yadda na saba sannan na yi Noor addu'ah bayan wacce ya karanta ta shiga bachi, ni ma na yi muka kwanta cike da aminci da salama.

Can cikin bachi naji Inna na tashina a hankali, ina buɗe ido hankalina ya tashi sosai, sakamakon jin ana ƙoƙarin buɗe ƙofar gidanmu da muka ji ana yi, ashe nice bachi ya lula da ni sosai ban ji ba har sai da aka tasheni su Sakina da Jamila kan tuni suka ji har sunyo ɗakinku sun ta ɓoya bayan Inna suna kuka, Noor ma yana ƙanƙame da Inna jikinsa sai rawa yake.

“Ku shige ƙarƙashin gado”

Inna ta faɗa kaɗan-kaɗan, ni kan araina na ce wane irin ƙarƙashin gado kuma ƙarƙashin gadon da itace ne muka saka a ƙasa ni da Habiba, saboda a samu yabuɗaɗɗiyar katifar ta tsaya. Kamin mu yi wani unƙuri sai dirowar mutane muka ji cikin ɗakinmu, daman ƙofar ɗakin ta cire ta can farkon shigowa gidace kawai ta rage muke rufe gidan da ita. Fitila mai haske sosai ɗayansu ya dallo min ba shiri na rumtse ido jikina na rawa na rumgume Inna ina saki fitsari abunka da mai mugun tsoro...



TO SU WAYE KUMA WAƊANNAN😨😱
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


2⃣4⃣

Sakina da Jamila ne suka saka da Noor ne suka ihu ganin bindiga nikan dabam idanuwana a rufe suke addu'a kawai nake karantowa.

“Ku yi mana shiru..”

Ɗaya daga cikinsu ya faɗa a tsawace cikin wata murya mai kamar doro, sai duk suka yi tsif kamar babu su a gurin.

“Dan Allah dan Annabi karku cutar min da yara ku yi haƙuri”

Shine abunda Inna take ta roƙo muryarta na rawa alamar tsoro yana tare da ita.

“Ki kwantar da hankalinki ba zamu miki komai ba ba zamu taɓa kowa na ki ba, kuɗi muke so ko abun kuɗi”

Jin wannan yasa na sassauta riƙon da nayi wa Inna na buɗe ido tare da ɗagowa na kalli fuskokin waɗannan mutane da suka zo neman kuɗi a gidanmu, ina ɗagowa ɗayan ya dalla min fitila a ido gashi ba shiri na sake rumtse ido.

Ɗan abunda Inna ta san tana da shi na canji taje ta ɗauko ta kawo musu jikinta sai rawa yake tana faɗin

“Shikenan na ke dashi a gidan nan Wallahi ba muda komai mu talakawa ne”

“Kina da ɗan kunnen zinari ko azurfa?”

“Wallahi bamu da shi”

Ta bashi amsa ciki kuka mai cike da tsoro. Ban sake jin sun ce komai ba sai kawai na jin nayi suna da bincikar kayan da ke ɗakin wasu kuma suka nufi ɗakinmu wacan dake waje suna bincika, hakan ya bani damar buɗe idona a karo na biyu na kalli mutun huɗu da suke ɗakin suna mana bincike, daga ganinsu manyan ɓarayi ne domin ɗauke suƙe da manyan bindigogi fuskarsu sanye da fuska irin ta manyan ƴan fashin nan dukansu danye suke da baƙar riga da jean banƙi.

Mun ga ikon Allah a wannan ranar domin komai sai da suka bincike, sam basu yarda bamu da komai ba, har tufafinmu sai da suka bincika suka tsince masu kyau, ragowar shinkafar da ta rage mana mana dafawa har da ita suka haɗa, wani abun ɗaure kai har da tukunyar da muke dafa abincin sannan suka ce duk mu rufe idonmu kuma mu kwanta, sannan suka fice suna cewa duk wanda ya ɗago sai sun halbeshi. Ni dai ba buɗe ido ba ko motsi ban sake yi ba har na kusan minti talati saboda kawai tsoro.

A daren babu wanda ya sake runtsawa daga ni har Inna da Sakina, Jamila da Noor ne kawai suka yi bachi, Noor ma sai da na rumgumeshi. Abu ɗaya ne ya tsaya min a rai har garin Allah ya waye, miyasa basu shiga gidan manyan masu kuɗi ba sai gidanmu? Beside waɗanne irin ɓarayi ne ma da zasu ɗauki tsofin sutura da ragowar shinkafa da ƴan canjin da basu kai dubu biyu ba da sunan sata da alama mu fa manyan ɓarayi ne ba ƙananan ba.

‘Turosu aka yi’

Shine abunda zuciyata take ta yawan nanata min, sai dai kuma waya turo su?
Washe gari mutane suka yi ta shigowa suna mana jaje tare da fatar allah ya tsare gaba ciki har da ƴan babban gida, sai dai wannan besa ɗayansu ya yi tunanin cewa mu koma can ba, duk kuwa da kasancewar rayuwarmu tana cikin hatsari saboda suna ganin idan muka koma zama tare da su lalurar mu ce zata hau kansu, kai tirrr da wasu ƴan'uwa!

Da yamma Jidda ta zo ita da mamanta suna jajanta mana take labarta min abunda ake faɗi a unguwa, wai gurin dai suka zo har wasu na cewa ba zasu rasa min fyaɗe ba sai dai ba zan faɗa ba, maganar ta ɓata min rai daman nasan dole mutane su zargi haka ganin bamu da Komai kuma ace sun zo gidanmu.

Baba Sulaiman ne ya kira mai gyara ya gyara mana tsohon ganbun na ƙofar gida da mutane suƙa ɓalle suka shigo. Tun da yamma muka bar gidan saboda ƴan'uwan Inna da suka sha kai akan sai dai mu dawo can da zama, ranar a tudun wada muka kwana gangaren tallatu sayin salamatu mai tuwo. Sun nuna mana mana kulawa sosai aka wuni ana firar ta nan na fahimcin Inna ma ta gano turosu aka yi, sai dai ita ta allaƙa abun ne ga Mustapha har take min faɗan wai na lallaɓa mu rabu lafiya da shi.

Bayan sallah isha'i Bilal ya kirani na kwatanta masa inda nake, ko minti arba'in ba a ƙara ba sai gashi ya iso tudun wada, na fito titi na shigo da shi cikin lungun na mu. Gaisawace first abunda muka fara yi sai yasa na kira masa Inna ya gaisheta tare da yi mata jaje sannan ya ce an gidansu suna gaisheta. Bayan Inna ta shige ya dawo kaina sai bugun cikina yake yana ta son ya ji idan sun min wani na san wannan ba zai rasa nasaba da maganganun mutane da yake ji ba.

“Kaima ka yarda da abunda mutane duke faɗa kenan”

Ajiyar zuciya ya sauke ya gyara tsayuwarsa ya ce.

“Yarda ta da rashin yardata duka suna gurinki, Wallahi komai kika faɗa min zan yarda da shi Nawancy”

“Idan har ka yarda da ni toh ka yarda da duk abunda zan faɗa maka, Wallahi basu min komai ba ko hannuna basu riƙa ba, babu wanda suka taɓa a gidanmu”

Sanyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke tare da jinginawa jikin iccen tarbejiya dake ƙofar gidan yana hamdala.


“Allah na gode maka, Wallahi Nawancy da sun taɓa ki ban san yadda zan yi ba ban san iya halin da zan shigaba”

“Da ba zaka iya aurena ba ko?”

Hakan yasa shi ɗagowa daga jinginen da yake da sauri yana kallona fuskarsa da ɗauke da murmushi.

“Nawancyta da gaske kike maganar nan da kika yi?”

Ya tambaya yana matsowa kusa da ni kamar zai haɗa numfashinsa da nawa, hanzarin matsawa baya nake sai ya yi caraf ya cafke min hannun yana cigaba da matsosa kusa da ni.

“Kin san waye ni babu abunda zan miki, kawai ina son na tabbatar ne, Wallahi Nawancy i'm ever ready to marry you dan Allah ki taimaka min”

“Mutane fa zasu gani”

Na faɗa a tsawalle ina kawar da fuskata, sai na yi sa'a ya sake ni, ina ganin hakan na juya da gudu na shige gida.
Babu irin kiran da be min ba ta waya amman na ƙi ɗagawa har ya gaji ya tafiyarsa.
Kwanan mu biyu a can muka dawo gida saboda tsallawa da muka yi saboda gidan gidan taro ne babu sakewa sosai, ga yaran gidan basa da ragowa a gaban idona suke buge Noor ba damar nayi magana ace na yi rashin ta ido su kuma ba zasu iya yi ma yaransu magana ba.
Ranar da muka dawo ma mutane sun ta zuwa yi mana jaje mutanen da basu samu zuwa mana washe garin da abun ya faru ba, saƙon kamfani kan kamar ƙa'ida ko da muka dawo mun tarar da wasiƙa biyu wacce aka kawo yau ita ce ta uku ban da ta waya da nake ta karɓa ko wace safiya da kuma yammaci.
Bayan na gama gyare-gyaren gida na shinfida tabarma na zauna tsakar gida ina ta nazarin abubuwan rayuwa ciki har da wannan abun da ya same mu, da kuma maganar ƴan sanda da suka yi mana izgilanci amman shiru har yau babu dpo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login