Showing 96001 words to 99000 words out of 138998 words
Kowa ya sa rai mu za a bawa kwangilar nan amman saboda sakacinka komai ya lalace”
“Abbah kasan ba guri daya hankalina yake a yanzu ba”
“Fine ka mikawa Siraj ragamar kamfanin nan, a duk lokacin da ka dawo cikin hayyacinka sai ka kamfanin ya dawo hannunka, amman ba zai yiyu muyi ta hasara hakan nan kawai ba”
“Okay Abbah nima hakan zai fi min an gaskiya bana cikin kwanciyar hankali a yanzu”
“Ai kai ka jawa kanka komai saboda baka jin magana, da gaskiyar Hajiya (step mother dinsa) da take cewa na rika kyaleka duk da gangan kake komai”
Ajiyar zuciya Jibril ya sauke be sake cewa komai ba, yana ta sauraren fadan da Abbah ke masa, kamin daga bisani ya kashe wayar.
“Oh Allahna kai kadaine gatana”
Ya furta yana shafa fuskarsa. Siraj dake gefensa ya dashi
“Ka kwamtar da hankalinka Jibril komai zai wuce, matsalar ka kawai kana sakewa Nawwara ne da yawa, be kamata ace tana maka irin wannan cin mutuncin ba”
“Idan bata min wannan cin mutuncin Siraj ba zan taba gane cewar tana so na ba, kuma a duk lokacin da ta yi fushi ta kan fadi kalmar da zata amfaneni, jiya ma ta fadi kalmar wani Faruk wanda na fada maka maybe tsohon mijinta ne”
“Ba lallai ya zama tsohon mijinta ba Jibril ina ta nanata maka, maybe wani dan uwanta ne ko makocinsu, ni abunda na ke ganin ya fi kawai ka ka fitar da kudi sai a nemo wani wanda zai aureta ana daura auren sai ya saketa kaga shikenan sai kai kuma ka aureta hankali kwance zuciya zaune, sai a nemo wani talaka mai neman na kansa ko da tsoho ne Nawwara ta aura”
“Amman dai kai wawa ne Siraj, taya zan bari Nawwara ta auri wani? Ai itama ba zata taba yarda ta auri wani dan ta fito ta aureni ba, and ba zan iya barin kowa ya kwanta kusa da ita ba saboda har yanzu ita iyalina ce, duk wanda ya kwanta gado daya da matata sai na hora shi, ballantana kaddara ta kaishi ya kusanceta ko waye mutuwa kawai ta dace da shi”
“No Man no ba ina nufin ya aureta ba ya kwana da ita ba, ana daura auren zai saketa shikenan fa, idan kuma kana jinnrashin natsuwar hakan sai ka nemi wanda yake kusa da kai wadda ba zai musa maka ba sai ya aureta”
“Zan yi tunani akai, amman ina son ka bincika min gaskiya magana akan auren nan, and Abbah ya ce na mika maka ragamar kamfanin nan yanzu”
“What...?”
Ya amsa da karfi zuciyarsa kuma cike da farinciki.
“Saboda mai?”
“Ba komai kawai ina ganin kamar akwai wanda yake tsegunta ma Abbah wani abun ne akan kamfanin da kuma rayuwata, saboda kwanaki ma yayi ta min fada akan wai ina shan cocaine yanzu kuma yana fada akan kwangilar gobnatin taraiya da muka rasa ta gina gidaje, wai an fada masa ko takardar kamfaninmu bamu tura ba”
“Gaskiya akwai wanda yake labarta masa wani abu akai, amman gaskiya ni ba zan iya daukar ragamar kamfanin nan ba, taya kai za ace ka aje abu ni kuma sai ace na dauka? Gaskiya ba zai yiyu ba”
“No no he trust you ne, ai kasan Abbah idan be yarda da mutum ba ba zai saka shi a arkar kasuwancinsa ba, ni ma da be yarda da ni ba ai da ba zai kawo nan a wannan kamfanin ba, so karka bashi kunya kawai ka yi aikin nan nima zaka taimakamin domin zan samu na kula da Nawwara”
“Zan yi tunani a kai”
“Ba wani tunani sai ka karba”
Siraj ya tashi tsaye yana nuna kamar be jidadin abun ba, alhalin kasan zuciyarsa farinciki ne kawai da murna.
“Zan tafi xan sa ayi bincike akan Nawwara din”
“Thank you so Friend Allah ya bar mu tare”
“Amin akwai hoda idan...”
“Hodar nan tana daya daga cikin abunda Nawwara ta tsana, ina ta kokarin daina shanta ina son na zama mutumen kirki Siraj, ina da yaro a yanzu kuma ina son Nawwara ta dawo rayuwata dole ne wani halin za a zubar da shi”
Tabe baki Siraj ya yi.
“Nawwara dai Nawwara, ga Zinatu tana son ka amman hankalinka yana gurin wacce bata ganin tausayinka”
“Ka tafi kawai zai fi maka, bana son kana min maganar kowa ban da Nawwara”
Ya fice yana wani sunsun da kai. Yana fita Jibril ya kira Rabi ta waya yana fada mata abunda yake son ta yi.
“Bincike na ke son ki min akan Nawwara saboda na san Siraj ba zai samu dama ba a yanzu saboda shi ne new ceo din ku yanzu”
“New ceo Sir? Why ka bar garin ne?”
“No Abbah ya bukaci a bashi ni akwai abunda na ke, ki bincika sosai please”
“Okay Sir amman miye alakarka da ita saboda na san irin binciken da zan yi”
“She's my wife, my ex-wife mother of my only Son”
“Okay Sir zan yi komai inshallah”
Sai ya kashe wayar ya mike tsaye ya shiga bathroom, in 40 minutes ya shirya ya fito ya nufi asibitin zuciyarsa cike da zumudin ganin dansa.
Tunda ya shigo cikin aaibitin ake ta gaishe shi har ya isa sashen da Noor yake be riko masa komai ba, saboda yasa a rika kawo masa abincin da abun tabawa daga wani kasaitaccen restaurant sau uku a rana.
Yana tura kofar dakin ya shiga, sai ya nemi farincikin da ke zuciyarsa da fuskarsa ya rasa, saboda ganin Bilal da ya yi zaune saman hospital bed din rumgume da Noor da ya shige jikinsa sosai ya labe kamar mai bachi.
“What are you doing here?”
Ya tambaya kamar be san inda Bilal ya fito ba. Uffan Bilal be ce masa ba ya yi kokarin sauke Noor daga jikinsa sai Noor ya kara lake masa wanda hakan ya bata ran Jibril.
“Uncle Bilal zan bi ka”
“Aa baka ganin baka da lafiya? Kana bukatar kulawa idan ka ji sauki da kaina xan zo na daukeka na kaina gida sai muje yawo ka ji”
Ya gyada masa kai yana kuka.
“Uncle Bilal zaka dawo anjima ko?”
“Eh zan dawo”
“Tau ka zo min da Momy”
“Zata zo, aiki take yi shiyasa bata zo ba”
Sai da Bilal ya shafa kansa sannan ya fita sai Jibril ya bishi a bakin kofar dakin ya jefa masa wata magana.
“Nawwara bata fada maka karka sake zuwa ganin Noor ba”
“Bata fada min ba”
“To ni na fada maka”
Bilal ya kalleshi ta kyau sannan ya ce.
“Look Jibril duk abunda na ke maka a kamfani ina yi maka ne sabida you're my boss a gurin kuma ina aikine dole duk abunda ka ce na bi, a waje ma ina respecting dinka so karka zubar da girmanka”
“Karka soma fada min wata maganar banza a nan, daga Nawwara har Noor mallakina ne”
“Noor ne kawai Mallakinka, amman Nawwara ba mallakinka ba ce, ka bar ganin kana da duka ba komai kudi yake siya ba, rashin arziki kuma ba shi zaisa takala ya wofintar da kanta a raina shi ba, ka taka a hankali”
Sai kawai Jibril ya yi dariya ya juya ya koma ciki. A ranar ya sha fama da Noor kamin Inna ta zo saboda Noor na ganin kamar Nawwara ba zata sake zuwa gurin ba, a ranar ya saka cewar kar securities din su sake bawa kowa damar ganin dansa in ban da Inna sai kuma wanda Inna ta fito da kanta ta zo da shigo da shi.
Da dare ya koma gida jikinsa agajewa ba dan kuma ya yi wani aikin ba sai dan tunanin da ke zuciyarsa ne ya saukar masa da gajiya. A lokacin ne Rabi ta kira shi take labarta masa abunda ta samo kamin fa kara bincike.
“Sir Nawwara ta auri miji biyu bayan baban Noor da auri wani Faruk amman ya rasu, sai dai mutane suna zargin cewa aurenta na fari ba aure ta yi ba saboda an boye abun kuma sai ta dawo gida da ciki”
Ya dan yi Jimm kamar ba zai ce komai ba.
“Ina kika ji wannan”
“A wani gidan makotansu ne na ji, saboda na nuna musu yayana yana son ya aureta ita kuma ta boye masa tace budurwa ce”
“Thank you, akwai wani abun da ya kamata na sani ne bayan wannan”
“Babu amman nace suna fama da talauci sosai, Babanta ya rasu saboda sukan da police suka masa akan sun kamashi ya yi sata wacce matar da yayanta suke cewa wai ba gaskiya bane, wasu kuma ce gaskiya ne, yar uwarta kuma ta rasu wacce ta fi so a cikin kananeta, zan fadada bincike nan har sai idan na kammala sannan zan labarta maka komai”
“Na gode, na san ba aikinki bane amman na gode, ki turo min account number dinki”
“Okay Sir thank you”
Yana sauke wayar sai duk jikinsa ya yi sanyi, wani irin tausayin Nawwara ya rufe shi. Ranar kwana ya yi da tunaninta da kuma tunanin irin wahalar da ta fuskanta gidansa. Washe gari sun da safe ya shirya ya nufi asibitin dan yana son ya yi breakfast tare da Noor, sai ya samu Nawwara bakin kofar harabar da zata sadata da dakin an hanata shiga, tana ganinshi ta sauke kanta kasa har sai da ya karaso kusa da ita.
“Nawwara da yanzu ban dawo rayuwar Noor ba, haka za ki yi ta masa bitar maratun na ko?”
“Akwai sama ko kasa da abunda ya kamata na karanta masa ne bayan abunda ya faru? Kana da sa'a Jibril komai kake so kana samu, na raini da na rana daya ya zo ya zama naka”
Ya cije lebensa na kasa ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce
“Kina ganin kamar darin duniya ne abunda kawai nake so? Ba shi ne kadai gata ba Nawwara, matukar babu ke babu Noor ina jin kamar rayuwata bata da amfani a duniyar nan, ni taimake ni Nawwara ki bani damar da zan zama silar farincikinki”
Ta tada kai ta kalleshi da idanuwata dake cike da kwalla.
“Idan na yafe maka zaka daina shiga sabgata?”
“Zan daina matukar za ki daina shiga rayuwar da na....!”
[11/8, 9:37 PM] +234 703 352 5246: *RAI BIYU...♥🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
4⃣7⃣
Na yi murmushin mamaki ganin irin karfin halin Jibril, lallai maza basa da kunya yanxu har yana da bakin da zai ce min wai sai idan zan rabo da dansa? Ni zai kalli tsabar idanuwana ya ce min haka?
“Ba zaki iya rabuwa da Noor ba, ni kuma ba zan iya rabuwa da ke ba, ba kuma zan daina neman ki yafe min ba”
“Zan iya shiga?”
Na tambaya ina kallon security da ya tare kofar, sai ya kalli security ya ce
“Bata hanya ta wuce matata ce”
Da sauri ya janye min ya bude min kofa, ni kuma na shiga ina murmushin jin ya kira ni da matarsa lallai iska na wahalar da mai kayan kara. Ina gaba yana bina ba dan na san inda dakunan suke ba daman can Inna ce ta kwatantamin, har na wuce dakin sai ya kira da sunan da be taba kirana ba har na dauka cewar ba da ni yake ba
“Mrs Makama”
Ganin ban waigo ba yasa ya kara da cewar
“A nan dakin yake”
Juyowa na yi na dawo na shiga kofar da ya bude min, a yanayin yadda dakin Noor yake sai ka rantse da Allah ba cikin asibiti ba ne, ya kawata masa dakin da teddys ga wani madaidaicin plasma dake lake gurin freezer din dakin. Noor na ganina ya yi saurin saukowa saman gado ya doso inda na ke sai muka rumgume juna.
“Momy miyasa baki zo ba jiya da wata jiya kamin jiya?”
Dariya na yi na shafa kansa.
“Tan ba ga Daddynka yana kula da kai ba?”
Ta da kai ya yi ya kalli Jibril.
“Momy da gaske shine Babana?”
“Ee mana ba ga kamaninka nan kana ganin a fuskarsa ba?”
“Amman Babana Faruk fa?”
Daukarsa na yi na dora saman hospital bed din sai nima na zauna, Jibril kuma ya zauna a kujerar da ke fuskantarmu, sai na kama hannayen Noor na ce
“Baba Faruk ya rike ka kamar dansa, saboda a lokacin Babanka baya nan ya yi tafiya zuwa gurin karatu wata kasar, kuma baya son ace maka baya nan shiyasa ya fadawa Baba Faruk cewar ya ce shine mahaifinka kamin ya dawo”
“Miyasa Inna ta mareki saboda shi?”
“Saboda na boye maka gaskiya tun farko ban fada maka ba sai yanzu, tana ganin kamar ba zaka fahimta ba”
“Miyasa kika ce Uncle dina ne sai kuma yanzu kika ce shine Babana kuma?”
Yanzu kan ban san mi zan kara ce masa ba kuma, jin na yi shiru ban amsa masa ba yasa ya kara aiko min da wata tambayar.
“Ko dai da Baba Faruk ya rasu sai wannan ya dawo?”
“Aa kamin na auri Faruk na fara auren Babanka sai kaddarar aure ta raba mu, ya tafi karatu wata kasar sai Faruk ya aureni kai kuma ya rika ka kamar dansa saboda yana so na kuma ya san kimata, amman ba shine asalin mahaifinka ba, wannan shine mahaifinka na gaskiya shiyasa ake kiranka da Muhammad Jibril ba Muhammad Faruk ba”
Ya yi shiru kamar mai tunani sai kuma ya yi murmushin da ya bayyana hakoransa.
“Momy na gane, yanzu Babana be rasu ba kenan?”
“Gashi a gabanka kana gani, kuma yana son ka sosai kai har ma ya fi ni son ka”
Na fada ina nuna masa Jibril
Murmushi Noor ya yi sosai ga dukan alamun yaji dadin haka, sai na rika shi ya sauka saman gadon ya nufi inda Jibril yake yana ta kallonsa.
“Kuma fuskarmu guda ko Momy?”
“To ai shine mahaifinka shiyasa kuka yi kama, kaga ai baku yi kama da Baba Faruk ba ko kun yi kama?”
“A'a”
Sai Jibril ya daukeshi ya dora saman cinyoyinsa ya rumgume yana sauke ajiyar zuciya.
“Thank you so much Dear”
Ya fada yana kallona fuskarsa na nuna jindadin da ke cikin ransa. Tun daga ranar na ke ta kokari wajen kawarda duk wani abu da zuciyata take nuna min, hakan ba karamin faranta ran Jibril da Inna ya yi, ni ko farincikina farincikin mahaifita da kuma da na, sati daya da muka a asibiti ya isa ya samarda wani kudi na littafin soyayyar uba da da tsakanin Jibril da Noor, saosai da sosai Noor yake son babansa yana shiga jikinsa wani lokacin haka zai kyaleni ya yi ta sha'aninsa shi da mahaifinsa, Jibril kuma kamar ya cinye shi yake ji cikin kwana biyu ya yayatawa duniya cewar yana da, abun mamaki har Abbah sai da ya zo ganinsa yan uwansa ma wadanda suke uba daya sai da suka zo, abokaninsa na nesa da na kusa suna ta zuwa ganin Noor saboda ya fada musu dansa ya kare a gabana wasu ke cewa daman wai kana da? Mun samu alheri sosai domin duk abunda ka bawa Noor Jibril baya dauka ni yake barwa, sai dai wani abun da yake bani mamaki duk cikin masu nan ban taba ganin Siraj ba duk kuwa da kasancewar ba ko yaushe na ke tare da Noor ba, amman a yadda nake ganin abotarsu ya kamata ace Siraj gana zuwa ko da be zo kullum ba ya zo ko da sau hudu ne a sati. Ranar da Noor ya kwana takwas a asibitin na bukaci a sallamemu amman sai ya ki, ni kuma ba dan komai na ke son komawa gida ba sai dan Bilal saboda kwana biyu nan na rasa gane kansa ya kasa fahimtata yawan zuwa da nake asibiti jinyar Noor yana ganin kamar wata sabuwar soyayyace ke kulluwa tsakanin da Jibril.
A ranar da muka fara zuwa kotu zama na farko na sha kuka a ranar saboda ya tuna min da mahaifina da kuma Habiba, na yabawa Dpo sosai domin ya nuna kulawa akan case din ga kuma police din da alkali ya bada ikon tsarewa har zama na gaba, wani abun da ya bani mamakin matar da ta ce Mahaifinmu ya yi mata sata tana da yanayi da Siraj sosai kuma ita ba ce a tsareta ba saboda tana da kudi ko kuma tana da daurin gindi ko kuma dan tana da kokarin kare kanta cewar ba ita ta saka su ba oho. Ni dai har muka fito daga cikin kotun ban daina harararta ba ita kuma bata daina kallona ba.
Tare muka fito da Inna da Sakina, sai Jidda da Bilal da kuma yan uwan Baba da na Inna, kowa da abunda yake fada ni dai ban ce komai ba, har muka shiga Napep muka dawo gida. Muna shigowa gida Jidda take labarta min cewar Mustapha ba shi da lafiya jiya aka kai shi asibitinsu Jibril.
“Miya ke damunsa?”
“Ke kika damunsa Nawwara”
“Kamar ya? Ai na ce na yafe masa”
Ta yi shiru bata sake cewa komai ba.
“Kinje kin duba shi?”
“Ina tsoron mahaifansa”
“Mai tsoro baya zama gwanin Jidda matukar kika saka tsoro a zuciyarki Mustapha ba zai taba fahimtar cewar kina son shi ba”
Ta kalleni da sauri.
“Waya ce ina son sa? Mustapha da yake son ki sai kuma ace ni ina son sa?”
“Ba fada min aka yi ba, a idanuwanki na karanta”
“Baki min adalci ba Nawwara baki san komai a kaina ba”
Ya mike tsaye a fusace ta fice, ni kuma na bita da kallon mamaki domin ban ga abun daga hankali a cikin wannan maganar ba.
Tashi na yi soma dora girki muna ta firar yadda zaman kotun ya wakana ni da Inna, da dare sai ga Bilal ya kirani a waya wai na fito yana kofar gida.
Na yi mamakin jin hakan saboda kwana biyu ya dauke min kafa daga zuwa fira ko da kuwa ni na bukaci hakan sai dai mu gaisa a waya, na dauri aniyar sakashi farinciki a yau ko da kuwa ba da niyar hakan ya taho ba, dan haka na dauki kayan kwaliyata na dandasa kwaliya mai kyau na feshe jikina da turaren da Jibril ya aiko min cikin kayan da ya siyo min kwanaki, na dauki gown din atamfa da take cikin kayan da Jibril ya aiko min na saka, ni kaina na san na yi kyau a wannan dare, Inna ma kallona kawai ta yi tayi murmushi, nima na fice ina murmushi.
A yanayin yadda na tararda shi yasa ni jin babu dadi, domin kuwa fuskarsa babu annuri jikinsa kamar a sanyaye, bayan na masa sallama sai ya amsa min idonsa akaina kamar zai cinyeni.
“Nawancy kin yi kyau”
“Dan kai kadai na yi ta