Showing 123001 words to 126000 words out of 138998 words

Chapter 42 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

766

mutanen duniya ai”

Tayi min wani kallo sai kuma ta mike tsaye tare da daukar jakarta ta yi min sallama ta fice. Inna ta zo ta zauna kusa da ni tana fadin

“Ki yi hankali da wannan ma domin kin san ba yarinyar arziki ba ce”

“Na sani Inna amman Allah ya fita kuma shi zai tsare mu”

“Haka ne”

Firar Siraj muka bijiro da ita, a nan nake labarta Inna wasu abubuwa da bata sani a lokacin da ina aiki tare da shi, mun dade muna fira mutane kuma nata shigowa suna mana barka da dawowa ga Noor a tsakar gida yana da game da dayar wayar Jibril daya bar masa ya buga game kamin ya karba.

Bayan sallah magariba Bilal ya kira ni i was very surprised da na ga kiransa domin rabon daya kirani har na manta, gabana ne ya shiga faduwa sosai sai kuma tsoro ya kamani kamar ba zan daga ba sai kuma na daure na dauka, na yi tunanin wata maganar zai fada min sai ya ce min gashi nan kofar gida na fito.

Sai da na canja Hijab din da ke jikina sannan na sanar da Inna itama kanta ta yi mamaki, ni dai jikina a sanyaye na fito. Sai na same shi a daidai inda ya saba tsayuwa yana jingine da ginin gidanmu sanye da kananan kaya.

“Assalamu Alaikum ”

Sai ya dago ya kalleni, sai kuma ya yi murmushi.

“Kin tsorata ko sarkin tsoro?”

Na yi shiru ban ce masa komai ba, sai ya sauke ajiyar zuciya ya ce

“Ki yi hakuri da duka abubuwan da suka faru, na so naje ganin Noor asibiti sai dai ban samu dama ba, saboda Mama ta furta cewar bata yafe min ba idan na taka asibiti ganin Noor ke ko waya na kira na tambaya jikinsa bata yafe min ba, wannan dalilin ne ya hanani zuwa ganinsa”

“Ba komai, Mama tana hujja ai nima kuma ban kyauta ba”

“Babu abunda kika na rashin kyautawa, face fifita son Jibril akan nawa da kika yi”

“Haba Bilal karka dauki zigar mutane mana duk wanda ya fada maka haka ya yi maka karya”

“Ba fada min aka yi ba, gani na yi da idona”

“Babu abunda ka gani Bilal kawai kana son ka yi amfani da wata damar ne ka ci min fuska”

Sai ya gyara tsayuwarsa ya kalleni

“Ki rantse min da Allah a yanzu nan babu son Jibril a zuciyarki!”

Sakin baki na yi ina kallonsa sai idanuwa suka cika da hawaye, na kasa karyata kaina balle kuma na karyata shi, Allah yake son na rantse da shi taya zan yi rantsuwa akan abunda ba ni da tabbaci ni kaina a yanzu ba zan iya cewa akwai son Jibril a zuciya ko babu abu.

“Kin gani? Kina son shi har gobe Nawwara, dan haka karki yaudari kanki, wannan dalili yasa na ke jin kamar ba zan iya aurenki ba saboda zuciyarki tana gurin Jibril ko da na aureki gangar jikinki kawai na aura”

“Wannan ne kawai dalilin?”

Na tambaya hawaye na bin fuskata.

“Ba wannan ne kawai ba, mahaifiya bata son ki Nawwara kowa ma a gidanmu baya son ki sai ni, wani lokacin abunda iyaye basa so babu alheri a cikinsa, and ko na aureki ba zamu taba jindadin zaman aure ba abubuwa za su yi ta faruwa wadanda ba zasu mana dadi ba.

Ban yarda Jibril ya fini son ki ba, amman na yarda son ki yafi yima Jibril illa sama da ni, Nawwara Jibril yana da ciwon zuciya wanda zata iya bugawa a kowa lokaci ta rasa ransa kuma ke kadaice maganin wannan ciwon nasa, na san zakiyi mamakin inda na ji ko? Na samu labarin ne ta hanyar abokan aikinmu da muka yi aiki a kamfaninsa tare, idan na aureki a yanzu na shiga tsakaninki da muradin zuciyarki kuma na shiga tsakanin Noor da Jibril na raba masa hankali gida biyu,

Last two weeks da suka wuce Jibril ya kirani muka hadu a Shukura Hotel da shi, kin san abunda ya yi min? Gafarata ya nema akan abubuwan da suka faru kuma ya rokeni da na rike masa dansa amana kuma na tarbiyantar da shi, da za ayi gasar son ki Nawwara da ni zan zama gwani kuma zakara, amman a wannan lokacin sai da na raina kaina saboda tausayin Jibril da ya kamani, saboda ya canja Nawwara saboda ke mutumen da baya kallon kowa da kima amman har ya nemi ya yafe masa kuma na masa alkawarin ba zan bari komai ya samu dansa ba, har ma ya yi ikirarin mayarda ni aikina, but yanzu idan baki aureshi ba kin san irin halin da zai shiga? Wata kila rayuwarsa marar kyau zai koma yi, kuma Noor ma ba zai ji dadi ba domin a yanzu ya saba da mahaifinsa, ya kamata ace shi ma yasan dadin mahaifa kamar ko wane da,

Dukan abunda Jibril ya yi miki abaya ya yi ne a cikin jahilci yanxu kuma ya dawo yana neman yafiyarki ya kamata ki yafe masa he deserved a second chance so that ya gyara duka laifin da kuskuren da ya yi, kuma shi ya fi cancanta da ya zauna da ke a yanzu saboda ya goge miki zargin da duniya take miki, kuma zaki samu ingattaciyar rayuwa ke da iyayenki wacce ni ba zan iya baki ita a yanzu ba, ko da zan iya baki sai nan gaba amman shi yana da abun duniya wanda ya kamata ace kema kin jidadi kuma kin more hakurin da kika yi,

Abu na karshe da zan fada miki shine, dukan mu ran mu a hannu Allah yake, amman masu ciwo irin na Jibril basa dadewa a duniya, kuma Jibril be da wanda zai iya tsawata masa a yanzu sai mahaifin da bashi da lokacinsa, ga jarabasar cin amanar da Siraj yayi masa wannan kadai ya isa yasa ki tausaya masa, ina son ki Nawwara amman son da nake miki na ki samu farinciki ne bana na aureki ba yan uwana da iyayena su saki a gaba, kuma ina son ki auri Jibril ko dan saboda Siraj da Zinatu, domin idan baki aureshi ba mamaki ya auri Zinatu wanda baki san iya abunda hakan zai haifar ba”

Hawaye nake babu kakkautawa kamar yadda shi ma yake.

“Kar tausayin wani yasa ka cutar da kanka kuma ka cutar da ni Wallahi ina son ka Bilal ina sonka sosai”

“Na san kina so na, amman ko mun yi aure zamu yi ta samun matsala ne kawai Nawwara, kuma ina da kishi sosai ba lallai ne muji dadin zaman aure ba, na san yanzu ba zaki fahimta ba, amman a nan gaba kadan zaki gane gata ne na yi miki kuma na yi ma kaina, ni dai zan bi zabin iyayena wanda ina tunanin Allah zai bani wacce zan so siye da ke saboda na yi ma iyayena biyayya, kuma in da rabon na aureki sai kiga na aure ki din gaba”

Durkusa na yi a gurin na hade hannayena ina rokonsa

“Ka yi ma Allah da annabi ka aureni Bilal zan iya jure duk wani cin fuska da wulakanci da zaka min ko na yan'uwanka Wallahi ina son ka, Bilal sauran fa sati biyu da kwana uku ayi auren nan dan Allah karka janye, kuma ko da ka fasa aurena ba zan taba auren Jibril ba, igiyar aure ba zata sake shiga tsakani na da Jibril ba”

“Idan har baki auri Jibril ba Nawwara to son da kike min na karya ne...!”


Ya fada a tsawace sannan ya share hawayensa ya yi tafiyarsa abunsa ya bar nan ina aikin kuka. Da kuka na shigo gida ina labartawa Inna abunda Bilal ya yi min sai tasa salati tana mamaki karfi hali irin nasa. Misalin tara da rabi Jibril ya kirani a waya wai gashi nan kofar gida ya siyowa Noor abu, a lokacin idanuwa sun kumbura kaina kuma yana mugun ciwo saboda kukan da nayi, nasan ba dan ni ya zo ba, amman ina da bukatar magana da shi saboda abunda ya faru tsakanina da Bilal hakan yasa na fito a lokacin yana tsaye shi da Noor yana bare masa ayaba.

“Noor shiga gida”

Na fada cikin muryata dake nuna na yi kuka har na gaji, ba musu Noor ya taka a hankali ya shigo cikin gida, ni kuma na kalli Jibril na ce

“Rokon Bilal ka yi ka ce karya aureni ko?”

“Miya kawo wannan maganar kuma?”

“Ban sani ba, duk abunda ka yi be isheka ba sai ka saka Bilal a gaba ka rokeshi”

“Wallahi ban rokeshi ba Nawwara, ni dai na masa magana ne akan ya rike min Noor da amana a matsayinsa na wanda zai aureki kuma na nemi yafiyarsa akan abunda ya faru daga karshe kuma na ce zan maidashi aikinsa ya ce min baya so yayi applying wani gurin sai dai idan wani abun ya fada miki daban wanda ba wannan ba”

Na dafe kaina ina kuka.

“Ki yi Hakuri Nawwara ban san haka zai bata miki rai ba da ban yi ba, nasan komai nayi a gurinki bana gwaninta”

Ya fada da muryarsa mai nuna tsantsan nadamarsa. Kasa ce masa komai na yi sai ya juyo na dawo cikin gida cike da zazzafan zazzabi.



MUSTAPHA POV.

Har yau har gobe son Nawwara na nan cikin zuciyarsa, sai dai ba kamar da ba, yana son ya auri Jidda ne kawai saboda Iayayen sun ki yarda da Nawwara kuma yana jin Jidda zata maye masa gurbin Nawwara ko ba komai hakan zai kara wanke shi a idon Nawwara ta yarda zata yarda ya canja har abada, kuma yasan hakan zai kara kusancinsa gareta, a tunaninsa idan ya auri Jidda hakan zai yi ma Nawwara zafi kasancewar aminiyarta ce, kuma yana yawan ayyanawa a ransa cewar ko Nawwara tana kasa giɗa sai ya aureta amana dai ko da ta tsufa ne dan shi har gobe be cire rai daga aurenta ba.

Momynsa ta yaba da Jidda ganin ita budurwa ce kuma ba a mata irin shaidar da ake yi ma Nawwara cewar ta haifi shege, mahaifinsa ma ya yaba da ita duk kuwa da kasancesar ba ita ya so ya aura ba, amman ganin ita ce zabinsa a dole ya amince da ita.
Ba zai ce baya son Jidda ba iya abunda ya sani yafi son Nawwara da Jidda sau dubu ma ba dari ba, irin soyayyar da Jidda ke nuna masa ne ma yasa yanzu ya maida hankali sosai a gurinta har manyan suka shigo cikin, duk da kasancewar ba a saka ranar auren ba iyayensa sunje sunga iyayen Jidda kuma an tsaida magana akan cewar satin sama za a yi musu engaged.
Duk irin shakuwa da so da kauna da ya shiga tsakaminsu har yau Jidda bata taba labarta Nawwara komai ba, ba dan kuma tana son boye mata din ba, sai dan tana nuna kamar ba zata kalli abun ta fuskar daya dace ba, tana ganin kamar Nawwara zata zargeta cin amanarta duk kuwa da kasancesar ta san cewar Nawwara bata son Mustapha amman bata san ta wace fuskar zata kalli alakarsu ba.
[11/17, 12:17 PM] Farar Mace...: *RAI BIYU...♥🖤*

Wattpad @KhadeejaCandy


5⃣7⃣

JIBRIL POV.

Cike da bacin rai ya isa gida, abunda ya kasa ganewa miyasa Nawwara ta kasa sakewa da shi ne miyasa abu kadan zata rika ganin laifinsa, sai yaushe zata fahimci irin son da yake mata? Yaushe zata gane duk wani kalami marar dadi daga gareta yana taba masa zuciya, har sai yaushe Nawwara zata fara sanin ciwonsa?

“O.... Ya Allah”

Ya jefar da keys dinsa ya fadi zaune saman kujera yana sauke ajiyar zuciya. Can Bilal ya fado masa a rai sai ya maida laifin a kansa daman baya son ganin laifin Nawwara, yana da bukatar jin ta bakinsa da haka dole ne ya kirashi, wayarsa dake aljihu ya ciro ya nemo number Bilal ya aika masa da kira, ta dade tana ringing kamin ya dauka.

“Hello”

“Bilal a Maganganun da muka yi a akwai wata magana dana fada maka wacce bata kamata ba ne?”

“Babu”

“Dan me zaka je ka samu Nawwara ka fada mata mun yi magana? Ba dan kowa ya sani yasa na kiraka ba sai dan ganin da na yi hakan ya dace”

“Nima dacewar na gani shiyasa na aikata abunda na aikata, na fada na fasa aurenta ne kuma gobe zan tura a karbo min kayan aurena da na kai gidansu shine kawai abunda ya tada mata hankali take ganin laifin”

Jibril yay saurin mikewa tsaye, maganar ta zo masa a baibai ya fasa aurenta as how shi ba ko dazun da Nawwara take ta kuka tana masa bala'i be tsaya ya tantance takamaimain dalilin da yasa ta haka ba, kawai abunda ya fi ji maganar sa da Bilal da yayi kuma ta ji.

“Ban fahimce ka ba?”

“Na fasa aurenta na ce, hakan yasa tayi tunanin ko kaine ka yi min wani abu sai na fada mata haduwarmu”

“Am amman miyasa ka fassa aurenta?”

“Saboda mahaifiyata bata son auren”

Yana fadar hakan ya kashe wayar be jira ya kara jin abunda Jibril zai ce ba. Farinciki ne da bakinciki suka zo masa a lokaci daya. Ya fasa aurenta yasa shi farinciki but what if shine dalilin fasa auren? Hakan zai sa Nawwara ta kara tsanarshi, bayan haka yasan Bilal yana son Nawwara idan shine yake kokarin aurenta kuma sai wani ya kwace masa ita ya zai ji?

“Amman kuma ai mahaifiyarsa yace da Bilal yana da niyar fasa auren Nawwara saboda da da tuni yayi, ina tunanin abunda ya faru ne yasa mahaifiyarsa ta hana ya aureta”

Ya furta a fili sai ya fadi zaune saman sofa ya lumshe ido.

“Wow da ace zan ganki matar nan da na miki kyauta mai tsoka”

Can kuma ya bude ido.

“I hope you're not fooling me, no he's not ai da Nawwara ba zata yi kuka ba har tana zargina”

Shi kadai yake ta maganarsa ransa fari fal ba zaka ce shine ya dawo gidan da bacin rai ba. Mikewa ya yi tsaye yana ji a ransa cewar addu'arsu ce Allah ya amsa kuma gana ganin he deserved happiness again tun da rayuwarsa ba mai tsawo ba ce. Wayarsa ce dake kan sofa ta yi ringing sai ya juyo da sauri.

“Nawwara”

Ya furta gabansa har bugawa yake da karfi, yana daukar wayar ya ga number Abbah lumshe ido ya yi.

“Oucccc am such a fool taya Nawwara zata kirani yanzu ba bayan fushi take da ni”

Bude idonsa ya yi ya danna picking ya kara a kunne.

“Hello Abbah”

“Jibril kana lafiya?”

“Lafiya kalau Abbah ya Abuja”

“Al-hamdulillah ya Noor yaushe zaka shigo”

“Da dai cikin satin nan ne amman yanzu ban sani ba gaskiya”

“Ya dai kamata kasa lokaci ka zo”

“Wani abun ne?”

“Akwai maganar da ya kamata mu yi”

“Ba zamu iya yi ta waya ba?”

“Magana ce mai muhimmanci zai fi kyau idan kana nan zaka fi fahimtar abun”

“Idan magana mai muhimmanci ce ka fada min a waya dan bana tunanin zuwa yanzu”

“Magana ce akan aurenka Jibril be kamata kana zaune haka nan ba, yarinyar nan da keke so aure zata yi,  zama haka ba ba zai maka ba, na sha baka dama ka fitar da wacce kake so sai ka ce sai Nawwara kuma yanzu gashi yarinyar nan aure zata yi, dole ne idan ta yi aure zaka karbo dan ka dan ba zamu barshi can ba, babu yadda zaka yi ta gujeka kuma ta zauna da danka, na san ka yi kuskure kuma ka zalinceta amman ai an bata hakuri so dole ne ka nemi matar aure wacce zata rike maka yaronka”

“Haka ne Abbah amman har yanzu ba a daura mata aure ba ba lallai ne ta auri yaron da yake son ta ba”

“Wai kai ba zaka cire ranka a gareta? Yanzu dai mun yi magana da Hajiya (Step Mother din shi) akwai wata yarsa margayi Alhaji Dahiru wato Salima wacce ta fito sai kaje ka gani idan kana sonta ba zamu cilasta maka ba, amman fa bazawara ce yaranta hudu sai dai duka yaran suna hannun Babansu”

“No Abbah wanda zai auri Nawwara ya fasa aurenta saboda mahaifiyarsa ta hana just saboda abubuwan da suka faru tsakanin mu, shine sai Nawwara ta bada damar na tura nawa magabatan”

Abbah ya dan yi shiru kamin ya ce

“Jibril ka tabbata?”

“Yes Abba, jiya take fada min haka kuma kasan yadda na ke son ta Abbah, ni yanzu abunda na ke so da kai kasa rana cikin satin nan ka zo ku ga iyayenta”

“Jibril ka tabbata”

“Yes Abbah”

“Shikenan zan samu iyayenka na nan mu yi magana”

“Thank You”

Daga haka Abbah ya kashe wayar, sai Jibril ya yi murmushi.

“Idan ma karya ne Bilal yake ai idan Abbah ya zo dole familynta zasu fada masa gaskiya”

Ya fada kana na nufi kitchen dan hada kansa tea.


NAWWARA POV.

Na ci kuka sosai a daren nan, na kasa yarda da abunda Bilal ya fada min na san yana so na dan me mahaifiyarsa zata shiga tsakaninmu? Miyasa idanuwan wasu suke rufewa su kasa fahimtar komai sai kansu. Washe gari da asuba bayan na gama sallah na dauki qur'ane na karanta Yasin wato zuciyar qur'ane, Suratul Yasin tana da fa'idodi da yawa ga musamman ga mutumen da yake cikin matsala da damuwa ta matsalar mijin matukar ka karanta sau goma sha biyar zama daya idan ya gama ya roke Allah bukatarsa idan da hali sai mutum ya yi sadaka, ba ni da halin karanta Yasin sha biyar hakan yasa na karanta ta sau daya na karanta Ayatul Kursiyo dari domin ita ma tana da nata fa'idan sosai kuma idan Allah ya amsa maka kamar yankan wuka yake, bayan na gama na roki Allah ya zaba min abunda duk yafi zama alheri a rayuwata, sannan na aika Jamila ta siyo min kosai na yi sadaka, a lokacin Sakina har ta shirya mana abun kari sun yi breakfast ni ce kawai ban ci komai ba tun tashina.

Dakin Inna na shiga na gaishe ta a lokacin Sakina ta gama shiryawa ita da Jamila suka kama hanyar makaranta, bayan sun fice Inna ta kalleni ta ce.

“Nawwara ki yi hakuri da yadda rayuwa ta zo miki, kuma ki yarda duk abunda Allah ya zaba miki shi yafi zama alheri a gareki, ni dai ina nan ina ta yi miki addu'a, dan haka ki daina sa kanki a damuwa, tashi kije ki zuba abinci ki ci”

Na tada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login