Showing 63001 words to 66000 words out of 138998 words
yadda yake amsa masa kamar baya maraba da mutane, sai dai be nuna masa komai ba ya ɗora akan abunda ya kawo shi.
“Na zo ne akan wani gida da yake guiwa, wanda ka siya ta hannun Malam Haruna”
“Me gidan ya yi maka?”
“Be min komai ba, ance min ka siye gidan ne milion ɗaya ni kuma zan baka 1.5 million ka mallaka min gidan”
Jibril ya yi murmushi tare da kwantawa saman kujerarsa yana lilo tare da wani shegen murmushi.
“Waya faɗa maka ni na siya gidan?”
“Malam Haruna ne ya faɗa min, naje gunsa ina son na siye gidan sai yace min wani ne ya siya sunansa Jibril, amman ya ce be san waye Jibril ɗin ba, yaro ne ko babban na buƙaci gani ka, yace bashi da number ka sai da ta wanda suka yi cinikin domin ya bar number akan idan mutunen gidan su tashi a faɗa masa, na buƙaci ya bani number wanda suka yi cinikin ne sai ya bani number wannan Siraj ɗin, ni kuma na kirashi sai ya yi min bayanin ba shi ya siye gidan ba kai ka siya kuma shi baya da wani abu da zai yi sai dai na yi magana da kai”
Hannu Jibril ya kai yana wasa da wata ƙwallo da ake saman teburinsa mai ruwan zinari wance aka ɗora saman wani abu mai kama da turmi.
“Amman miyasa zaka siya gidan har 1.5 million?”
“Saboda kai da ka siye gidan ka bawa waɗanda suke cikin gidan kwanaki su tashi, that's why na ke son siye musu gidan”
Siraj ya haɗa ido da Jibril sannan ya kalli Mustapha ya ce
“Kana da alaƙa da ƴan gidan ne da har zaka siye gidan da kuɗi da yawa haka, gidan da be wuce dubu ɗari shida ba?”
Mustapha ya watsa masa wani shegen kallo tare saboda yadda yaga sun maida shi ƙaramin yaro.
“Mr gida na zo siye ba bincikar alaƙata da ƴan gidan na zo ku min ba”
Jibril ya yi murmushi yana ciagaba da juyawa saman kujerar.
“Come on tell me boy maybe i can help”
Mustapha ya maida dubansa gurin Jibril jin irin isgilancin da yake masa, yanzu kan zuciyarsa ta fara raya masa akwai dalilin da ya sa Jibril ya siye gidan.
“Ban girmi ka karani boy ba? Name what ever you want zan baka am not here to play a game”
Jibril ya miƙe tsaye yana dariyar ƙeta ya nufi gurin window sa yana faɗin.
“In banda kai daƙiƙi ne baka taɓa tsayawa ka yi tunani ba, baka taɓa tambayar kanka dalilin da yasa ka na siye wannan gidan ba? Taya zan zuba har milion ɗaya na siye gidan dubu ɗari biyar sannan ka zo ka ce na fansar maka ni ba a min wasa da kuɗi sai dai ni na yi ma wasu wasa! Mu kamfaninmu baya siye da siyar da gidaje ni ma kuma ba sana'a ta ba ce, so wannan gidan akwai dalilin da yasa na siye shi, so walk out of my office ba zan siyar ba”
Mustapha ya tashi tsaye yana murmushi.
“Zuciya na raya min ka siye gidan nan ne saboda wata manufa is that the reason yasa ka basu lokacin tashi? Kuɗin ka be amfane ka ba Mr Billionaire, tun da har zuciyarka zata raya maka siye gidan talakawa kuma ka takura musu bayan kasan babu su da inda zasu koma me suka maka ne?”
Jibril ya ƙyalƙyale da dariya daga inda yake tsaye ba tare da ya juyo ba ya ce.
“Na siye gidan ne saboda na isa na siya, ni mijin Nawwara ne idan ma akan ta kake wahalar da kanka so ka daina yaudarar kanka”
Mustapha ya yi murmushi tare da zuba hannayensa aljihu.
“Her ex-husband dai Nawwara bata da wani miji a yanzu”
Jibril ya juyo yana kallon Mustapha murmushin da ke fuskarsa yana dusashewa, can kuma sai ya fara dariya.
“Yeah yeah it Funny am laughing, amman bari na faɗa maka wani abu ka bar irin wannan wasan i don't play when it comes to Nawwara”
Mustapha ya nufo kamar yadda Jibril yake doso inda yake.
“Kana son zaka saketa? Ƙarya so kake mata tun da har ka iya siye gidan da suke ciki dan kawai ka takura mata, a haka ake so? Ko dai jikinta kake so ne huh? Da nine na samu damar auren Nawwara ko ƙuda ba zan bari ya taɓa ba balle har ya kai ga na saketa ko da kuwa kullum ruwan zafi take zuba min a jiki, but look at yourself ka yi arzikin aureta amman ka saketa ooph so sad maybe rabona ce shiyasa ka saketa”
Cewar Mustapha yana wani abu da fuska kamar mai magana da ƙaramin yaro yana murmushi, cikin zafin rai Jibril ya kai masa bugu a fuska ya sake kai masa wani a gefen baki, cikin zafin nama Mustapha ya ɗago zai rama sai Siraj ya yi saurin riƙeshi ya jashi baya, hakan ya bawa Jibril ƙara kai amsa wani dukan a baki sai jini ya fara zuba.
“Abraham”
Siraj ya ƙwalawa PA ɗin Jibril kira sai gashi cikin ɗakin da sauri.
“Riƙe min wannan”
Da sauri ya Siraj ya saku Mustapha ya nufi Jibril ya riƙe shi yana faɗin.
“Take him out”
Ganin Abraham ɗin ba zai iya fitar da shi shi kaɗai ba, yasa Siraj ya saki Jibril ya nufi Mustapha suka fitar da shi tare.
Juyowa Jibril ya yi ya nufi teburinsa ya buge System ɗin da ke saman ta faɗi ƙasa.
“I need to see her, we need to talk zan bata haƙuri zan yi komai akan ta, ba zan bari wani ya ɗauki muhallin na a zuciyarta ba”
Komawa ya yi gaban teburin ya ɗauki wayarsa ya danna number Abbah, yawo ya riƙa yi cikin office ɗin zuciyarsa na mugun bugawa, a ƙarshe ya samu tsayawa jikin window saboda Abbah ya yi picking.
“Afternoon Abbah”
“Afternoon Jibril ya aiki?”
“Alhamdulillah, Abbah we need talk”
“About?”
“Nawwara Abbah na gano inda take”
“Ai nasan zaka gano inda take, shiyasa na ce ban yafe maka kaje ƙofar gidansu da sunan neman gafararta ba, kai yanzu dan baka da kunya sai kaje ƙofar gidansu har ka iya haɗa ido da ita? Mu muka zaɓa maka ita lokacin da zaka aureta ka butulce ma umarninmu ka ce kai ba haka ba yanzu kun rabu miye na bibiyar yarinyar mutane?”
“Na tuba Abbah Wallahi na tuba”
Ya duƙa har ƙasa kamar yana gaban Abbah.
“No ban yarda ba”
“Abbah ko dan na nemi gafararta ba, ina da buƙatar na tambayi abunda yake cikin maybe ta haihu, you know how i love to see my carbon copy Abbah kasan yadda na ke son haihuwa”
“Sai ka ƙara aure ka yi haƙuri har Allah ya baka”
“Abbah kasan na yi aure ba ɗaya ba amman Allah be bani haihuwa ba, taya Allah zai bani haihuwa bayan na yi masa butulci”
“Sai ka yi haƙuri"
Abbah na faɗar haka ya aje wayar. Sai Jibril ya miƙe tsaye yana cizon lips ya wulgarda wayar ƙasa iya kar ƙarfinsa, kamar mahaukaci ya fara bugun ginar gurin da duka hannayensa har sai da jini ya fitowa ko wannensu sannan yaja baya yana haƙi.
Zinatu ce ta shigo office ɗin da sauri hankalinta tashe ta doso inda Jibril ya ke.
“Miya same ka haka?”
Zata taɓashi sai ya yi baya yana ɗaga mata ɗayan hannunsa.
“Don't touch me, na yi ma kaina alƙawarin ba zan sake taɓa wata mace ba sai Nawwara, wata mace kuma ba zata sake taɓa ni sai ita”
Mutuwar tsaye ta yi a gurin ta, kamin ta juyo ta kalli Siraj da ya shigo yanzu.
“Miya faru kuma? Zinatu go and call doctor please”
Kainta kaɗa sannan ta juya ta fice jikinta a sanyaye. Siraj ya nufo Jibril yana faɗin
“Be kamata ka tada hankalinka akan wannan gayen ba”
“You don't know what Love is you have no idea how i feel so karka faɗa min wannan maganar”
“Ina ƙoƙarin faɗa maka wannan gayen be isa ya ƙwace Nawwara daga hannunka ba har sai idan kai ka so”
“Kasheshi zan yi Siraj babu wanda ya isa ya so Nawwara sai ni kaɗai ne wanda Nawwara zata so sai ni”
Siraj ya kai hannu ya dafa ƙirjinsa.
“Baka buƙatar kashe shi, sai idan kasheshi zaka yi da ranshi babu wanda ya isa ya yi gasa da kai Jibril sai idan ka so”
Wata kujerar da ke gefe Jirbil ya nufa ya zauna yana ta sauke ajiyar zuciya, wani haushi yake ji da baƙincikin da be shaƙe Mustapha ba.
*** *** ***
Misalin huɗu da rabi ina zaune tsakar gida ni da Inna muna tattauna abunda ya faru a ɗazu. Kamar daga sama sai muka ji sallamar Zinatu daman na ji tsayar mota a waje sai dai ban ɗauka mai motar nan zata shigo ba.
Na yi mamakin yadda na ganta fuska a sake kamar ba ita, cike da walwala ta gai da Inna sannan ta kai min duka irin na wasa.
“Ke ƴar gari gurinki na zo”
Cike da mamaki na tashi ina dariya na nufi ɗakinmu sai ta biyoni, bayan ta zauna saman katifar mu sai na fita na ɗebo mata ruwa na dire mata gabanta.
Sai ta ɗauke ruwan ta maiyar gefe ta fuskance ni ta ce.
“Nawwara ranar da kika mari Ogan mu, abun ya ban mamaki, abu na biyu kuma ya matsa akan yana son ki dawo aiki wai sai ya mugun wulaƙantaki, shine na ke son na san wace irin gaba ce a tsakaninku har haka duk da yake na ji ya kiraki da matarsa amman abun ya ɗaure min kai”
Murmushi na yi a zuciyata ina cewa ki ce gulma ce ta kawo ki kenan. A fili kuma sai na ce
“Babu wata alaƙa fa, kawai ya taɓa hannuna ne ni kuma bana son yadda maza suke taɓa ni shiyasa na mare shi”
“Amman miyasa ya kira ki matarsa?”
Ido na ƙura mata ina ta tunanin abunda zan ce mata, ban sani ba ko shine ya aikota ko kuma ta zo ta san wani abun ne.
“Shi ya kamata ki yi ma wannan tambayar, ai na yi zaton ke ɗin budurwarce ko ƙanwar da har kika yi unƙurin rama marin da na masa”
Ɗan murmushi ta yi.
“Nawwara kenan, ai ban za ci akwai wata alaƙa tsakaninki da shi ba shiyasa na yi hakan domin be kamata ki mari babban mutun kamar shi ba”
“Gaskiya ne, ke ma be kamata ace kin biyo ƴar talaka har gida kina bugun cikinta ba”
Miƙewa ta yi tsaye tana cigaba da murmushi ta dafa ni.
“Anyway daman na zo ne akan na baki shawara akan karki yarda ki koma aikin nan domin kuwa Jibril na shirya wulaƙantaki ba kaɗan ba”
Har ta juya sai kuma ta juyo ta kalleni
“Da ni ce ke ba zan taɓa yarda na haɗa ido da mutumen da ya wulaƙanta ni ba balle har ya kirani kariwa kuma na yarda na kula shi, Wallahi ba ayi irin wannan mijin ba”
“Sai kuma aka yi rashin sa'ah zuciyar Nawwara da ta Zinatu ba iri ɗaya ba ce”
“Ai ba zasu taɓa zama ɗaya ba har a bada ni dai shawara ce kawai na baki domin bana son ya cutar da ke”
“Tau na gode Ummu ta gaida Aisha”
Daga haka ta juya ta fice, ni ɗauki ruwan da bata sha ba na fice da su daman na san ba zata sha ba tun da ƙyamarmu take.
MUSTAPHA POV.
Gudu ya ke kamar zai tashi saman ko da ya iso gida kamar baya cikin hayyacinsa saboda ɓacin rai. Shi kansa be san iya adadin horn ɗin da ya yi ba kamin a buɗe masa gate, abunda ya tashi hankalin Hajiya ta fito a firgice tana kallon yadda ya faka mota kamar wani mahaukaci.
“Son what happen to you?”
Ta faɗa tare da nufar inda yake tana kallon fuskarsa hankalinta a tashe.
“Wani ne ya yi min haka saboda Nawwara Mom”
Hannayenta biyu ta kai ta riƙe fuskarsa tana kallon yadda gefen bakinsa ya soma kunbura ga fuskarsa ma tayi ja sosai abunka da mai farar fata.
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
*Dedicated to My Asmee ❤*
JIBRIL POV.
Bayan an gama wanke masa hannun aka bashi wani magani da zai sha, sannan likitan ya ɗauki box ɗinsa ya fice daga office ɗin zuwa chemist ɗin dake kamfanin kasancewar yana aiki a ciki ne.
“Siraj ka sake aikawa yarinyar da saƙo ko kuma ka kirata”
“Ya kamata mu bata time Jibril, idan har kana son Nawwarar nan ta yi aiki tare da kai kuma ta yarda ta yi aikin dole ne sai ka nuna mata cewar kai ma Namiji ne, rayuwarka ta baya dole sai ta fara aikin a kanta ya yadda zata gamsu aikinne dai kuka yi ba wani abu ba, matuƙar ka ce zaka kwanta ta hau ta takaka zata yi maka abunda baka tsammani kuma daga ƙarshe mu zo bamu samu abunda muke so ba”
Shiru ya yi tana nazarin kalaman Siraj yasan yana da gaskiya wani ɓangaren, a halin yanzu ya san Nawwara ba zata taɓa yarda ta yafe masa kai tsaye ba, kuma taya zata gane ya canja da gaske yana sonta idan har kusance ba idan kuma har be bi shawarar Siraj ba yasan babu kusanci a tsakaninsu domin zata yi ta nesantarsa ne.
Ganin Yadda Jibril ya natsu ya bawa Siraj damar cigaba da bayaninsa.
“I zuwa yanzu ya kamata mu dakata daga tura mata da saƙon neman ta dawo aiki ko kuma kiran da kake mata mu ɗaga mata ƙafa na ɗan wani lokaci”
“Baka san yadda na ke ji ba Siraj idan naji sunan yarinyar nan ji na ke kamar na runtse ido na buɗe na ganta a gabana, Siraj ina neman duk wata hanya da zan nuna mata da gaske na gyaru kuma ina sonta, abu na ƙarshe ba zan bari wannan wawan ya shiga zuciyarta ba”
“Ka yi haƙuri da sannu komai zai wuce, ka bata ɗan lokaci kaɗan, amman fa dole sai ka zama namiji domin ba zai yiyu ta riƙa maka wannan cin kashin ba”
“Idan kuma bata dawo ba fa?”
“Zata dawo na tabbatar zata dawo saboda tana tunanin ɗaukar fansar abunda ka yi mata ta hanyar wulaƙanta a gaban ma'aikanta, ai ta yi na ɗaya ka ƙyaleta dole zata yi ƙoƙarin yin na biyu har zuwa adadin da take ganin zata gallaza maka, idan kuma ba ta dawo ba sai mu bi wata hanyar ta dabam”
Ya saka hannunshi aljihi ya ciro ƙaramin hoto ya miƙawa Jibril.
“Ga wannan Abraham ya bani wai Nawwara ta manta shi lokacin da ta shigo office ɗin nan, ina tunanin yana da muhimmanci sosai a gareta”
Hannu Jibril ya miƙa ya karɓa yana duba, yasan ba Nawwarsa ba ce amman wacce ke cikin hoton tana kamada ita sosai, ajiyar zuciya ya sauke ƙana ya ce.
“Idan har Nawwara ta furta kalmar so gurin wannan yaron ko? Ba makawa kisa ya tabbata akansa”
Miƙewa ya yi tsaye ya fice daga office ɗin maganganun Mustapha na ɗazu suna ta masa yawo akai, yanzu kan bashi da babban maƙiyi kamar Mustapha domin duk mai son Nawwara a gurinsa maƙiyinsa ne indai namiji ne.
MUSTAPHA POV.
“Sai yaushe zaka ga ne Nawwara nan ba ajin ka ba ce Son? Dan me zaka bar wani ya yi maka haka akan macen da ko a mafarki be kamata ta zama budurwarka ba balle matarka ba, na je ɗazu na ma mahaifiyarta jan kunne akan karta sake bari ƴarta ta kula ka idan ma wani maganin ne tau ta yi gaggawar karyashi”
Ya janye hannayenta dake fuskarsa ya riƙe yana nuna mata tsantsar damuwa a fuskarsa.
“Haba Mom a maimakon ki taimaka min gurin neman soyayyarta sai kuma ki ɓata abun? Kin ce kina so na miyasa ba zaki so abunda na ke so ba? Wallahi yarinyar nan bata min komai ba, kawai Allah ya ɗauki sonta ne ya ɗora min dan ya jarrabe, dubi ki ga fuskata kin san dalilin da yasa na dawo gida yanzu? Saboda na nuna miki wannan abun ki san ba ni kaɗai na ke son Nawwara ba, kuma ki taimaka min wajen neman yafiyarta da soyayyarta, na je gurin wanda ya siye gidan da suke ciki ne akan ya fansar min amman sai yake nuna min kamar ya fini son Nawwara saboda shi mahaukaci, ni kuma na yi alƙawari ba zan taɓa bari ya auri Nawwara ba, ba zan hanata Nawwara son wanda zuciyarta take ƙauna ba, amman ba zata taɓa zaman aure da wani ba sai ni, saboda ta haka ne kawai zan iya gane cewar ta yafe min”
Hawaye ya fito a idanuwan Mahaifiyarsa ta yi mutuwar tsaye a gurin tana kallonshi.
“Shikenan sun gama juye min kan yaro, s8n gama da kai Mustapha ba zaka taɓa jin abunda zan faɗa maka ba”
“Ke kuma ba zaki taɓa gane abunda na ke nufi ba...!”
Yana kaiwa nan ya sake mata hannu ya nufi part ɗinsa.
*** *** ***
Bayan na aje ruwan da bata sha, sai tambayarta da kuma abunda ta faɗa min ya dawo min a rai, ya aka yi ta san Jibril ya wulaƙanta har haka? Ko dai shi ya faɗa mata ne? Idan har shi ya faɗa mata wannan yana nufin shi ya turota kenan? Amman taya zai turo ta bani shawara akn karna koma aikin kuma.
“Lafiya kuwa Zinatu ta zo?”
Ya ɗago daga tunanin da na ke na kalli Inna ina ƙirƙiro murmushi tare da nufar inda take zaune na zauna.
“Ba komai ta zo ne akan aikin nan wai yau ban je ba na faɗa mata se gobe shine wai bata son ina wasa da aikin ne”
“Nawwara be kamata ace kina ɓoye min wani abu ba, ni fa mahaifiyarki ce, bana son noƙe-noƙen nan da kike haka kuka yi ke da Habiba har ta Allah ta kasance”
Rumgumata na yi ina murmushi.
“Wallahi Inna maganar aikice ta zo ta bani shawara, babu wani abu kin ji na rantse miki”
Hakan yasa hankalinta ya kwanta, ni kuma na zari Hijabi na nufi gidansu Jidda.
A tsakar gidansu na sameta kwance saman tabarma ta yi rufa da zane da alama bata jindaɗi duk ta rame kamar ba ita ba. Da mahaifiyarta muka fara gaisawa sannan na nufi inda take hankali a tashe, hannu na kai na taɓa jikinta sai na jishi da ɗan ɗumi.
“Tun yaushe ne baki da