Showing 51001 words to 54000 words out of 138998 words

Chapter 18 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

738

ta kai BQ, mu kuma suka kawo mana abinci da abin sha.


Cikin sati ɗaya muka sake da ƴan gidan kasancewarsu mutane da suka san darajar ɗan'adam tun daga Hajiyar gidan har yaranta, Ƴaƴanta maza biyu manya sannan mata uku ɗayar tana aure sauran biyu kuma a lokacin suna karatune, sai ƴar ƙaramar ƴarta Salima, wacce ta kasance ta shida a cikin yaranta takwas.

Shaƙuwa sosai da sosai ta shiga tsakanina da Salima, har ta kai zuwa makaranta ne boko ne kawai yake rabamu, kasancewar ni bana zuwa bokon sai dai islamiya Alhaji Dahiru wato mahaifinta ya sakani Islamiyarsu.
Duk ƙarshen wata Baba yake zuwa gida duba Hajiya, wani lokacin kuma sai dai ya yi mata aike a haka muka kwashe shakara ɗaya a gidan Tsohon ambasadan nigeria a ƙasar London, muka zama kamar ƴan gida, shaƙuwa sosai ke ƙara shiga tsakanina da Salima, da kuma Babban yayanta Jamal, shi yake koya min karatu duk da ba a sani makaranta ba a lokacin, Jamal mutum ne mai son jama'a da far'a, har ta kai idan be ganni ba sai ya aika an kirani, bayan ya gama koya min karatu sai ya ce na yi masa gatana, ba laifi a lokacin na iya zuba gatana har da wacce ba'a taɓa yi ba, haka zai zauna ya yi ta saureren shirme na wani lokacin har da Hajiyarsu. Shi ya fara yaba ƙwazo na sai ya yi ma mahaifinsu magana aka sakani a makarantarsu Salima, na kashe kuɗi sosai gurin samo transfer dake nuna daga wata makarantar na ke, sannan aka samu sa'a aka sakani aji ɗaya da Salima, Habiba kuma aka sakata wata maƙarantar wacce ƙannen Salima suke yi.

Tare muke zuwa mu dawo, mu tafi islamiya tare, wasa-wasa sai na tattara kayana suka na koma ɗakinta da zama, a lokacin Inna na da cikin Sakina, komai a iri ɗaya muke da Salima bana da ƙawa sai ita itama bata da ƙawa sai ni, idan ba a ganta ba sai an tambayeni haka itama.
Ta ɓangaren Jamal kuma soyayyace mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu duk a lokacin ban san miye so ba, na kan samu kaina da tunaninsa da kuma rashin jindaɗi a duk lokacin da baya gida.
Muna daf da ƙare makarantar secondary school ni da Salima Hajiya ta samu labarin cewa Baba gadi yake a wani gida, babu irin bala'in da bata mushi ba cikin har da zance zata tsine masa gidan be dawo ba, wai Inna zata kaishi ta baro yana biye zancen mace. A dole tasa Baba ya tattara ya koma gida sai dai be zauna gidan ba sai ya kama haya kusa da su inda muke zaune har yanzu.

Ni kuma a aka barni nan da sunan idan na gama zana jarabarwar za a maidani gida, bayan mun gama jarabarwa ta fito ta yi kyau, a lokacin ne ɗan wani mai kuɗi ya fito neman auren Salima, Alhaji Dahiru ya yi na'am ya sallama masa bisa sharaɗin zai jirata ta yi karatu na gaba, a lokacin shi kansa yaron be kammala karatunsa da yake ba.

Bayan sati ɗaya da faruwar haka sai Ya Jamal ya fara min zancen aure, ni kuma ina ta tsoro saboda ina ganin kamar iyayensa ba zasu yarda ba, sai na nuna masa bana son shi, duk abunda muke a tsakaninmu ne iyayensa basu sani ba, har Salima ma tada zame min jinin jiki ban taɓa labarta mata ba, shi ma kuma be taɓa nunawa kowa ba.
Bayan takadun mu sun fito sai Alhaji Dahiru wanda muke kira da Daddy ya turo mu gida ni da Salima, bayan ya cika mana bayan mota da abinci, a lokacin an haifi Sakina har ta soma wayo.

Watan mu ɗaya muka garin Abuja saboda sabo sai zaman sokoto ya yi ma Salima wuya, ni kan ban so haka ba, sai dai babu yadda zan yi tun da mun zo tare dole mu koma tare, bayan mun koma sa sati ɗaya na sake dowa, Alhaji Dahiru ne yasa ka Ya Jamal ya rakoni har gida, sai dai wannan karon tafiyar Jirgi muka yi saboda Ya Jamal ya ce ba zai iya bin mota ba zuwa sokoto.

Kwanansa ɗaya ya koma, ni kuma na zauna a nan har na tsawon wata uku a lokacin Mahaifina yana sana'ar siyar da itace a ƙofar gida, wata rana mu cinye ribar wata rana kuma Allah ya buɗo mana, haka muke ta faɗi tashin rayuwa ga masu neman aurena sai fitowa suke. Kwatsan Alhaji Dahiru ya kira ya ce a sanar min ya samo mana gurbin karatun lafiya a ƙasar burtaniya wato London, cikin sati ɗaya na shirya na koma Abuja, duk wani shirye-shirye ina can aka yi shi, bayan kamar wata ɗaya da ƴan ƙwanaki aka kammala komai, sai da na koma gida na yi bankwana da su Inna a lokacin ne Yakunbo ta so tanani zuwa saboda a ganinta kamar za a siyar da ni ne ko wani abu makamancin haka.

Kamar na mafarki na fara karatu a City, University of London, a ƙasar da ban taɓa mafarkin zuwa ba, ƙasar da nake ji a labarai da kuma jaridu, burtaniya ƙasar turawa ce wacce bata da matsatsi akan addinin kowa a wacan lokacin, ba ko yaushe nake irin shigarsu ba wato shigar ƙananan kaya, nafi saka doguwar rigar atamfa ko abaya sai na samu ƙaramin ɗankwali ko hula na yi rolling kaina da shi.

Ɗakin mu ɗaya da Salima da kuma wata tsohuwar ɗaliba makarantar wato Farida, wacce ƴar asalin hijar bauchi ce, cikin ƙanƙanen lokaci muka saba da Farida duk da kasancewar ba gurin karatun mu ɗaya ba. Ranar da muka fara zuwa lab wani babban likita muka tarar ɗan Nijeria dan asalin garin Kaduna, wato Doctor Jibril Bashir Makama, sai da ya fara gabatar mana da kansa sannan na soma bamu darasi tare da nuna mana wasu abubuwan a zahiri.
Tun da idona suka sauka akansa sai ya tafi da imani da duk wani tunani da natsuwata, Jibril na da kyau da ba zaka iya tantanshi aa cikin ƴaƴan turawa ko larabawa, fatarsa fara ce fes ga shi da tsaye hancinsa ya sauko a ƙasan hancin an yanka masa madaidaicin baki, fuskarsa na ɗan faɗi, yana da manyan ido sai dai ba fararene ba, suna da surkin ja ƙaɗan, a gefen wuyansa tattoo ɗin taurara ne aka jera masa har cikin bayansa.

Hankalina baya kan abunda yake ƙoyar da mu yana kansa, duk wani ƙyabtawar idonsa ƙirgawa nake, ina haɗɗace yadda bakinsa yake motsi da turansa da yake watsowa kamar baturen burtaniya, duk bayan daƙiƙu sai na lumshe ido saboda ƙamshin turarensa da ya cika lab ɗin. Murmushi nake masa ba tare da na san ina yi ba, har sai da ya katsa min tsawa.

“You deaf...”

A firgice na dawo hayyacina cike da kunya, ƙasa-ƙasa na ke kallon wata abokiyar karatuna Katherine Williams wace ke sonim dariya ita da wasu da dake kusa da ni.
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


2⃣9⃣

Tun daga lokacin bana da tunani sai na shi, mafarkina ma nasa ne, duk wani abu da zai kusantar da ni gareshi na kanyi ƙoƙarin aikatashi, duk hanyar da zan ganshi ita na ke bi, duk da na lura da babu ruwansa da sha'anin kula wasu matan na daban hakan yasa na fara tunanin ko yana da mata ne.
Salima kanta ta lura da yadda nake ta rawar jiki da son ayi zancesa, idan kuma wata macen ta kalleshi sai naji kamar naje na shaƙeta, a gurin Salima na ke samun labarinsa, kasancewar ta sanshi farin sani wai ɗan abokin Daddy ne, na yi mamakin da ban san shi ba duk tsawon zaman da na yi a gidan, duk da kasancewar na san Mahaifinsa amman ban taɓa kawowa zuciyata cewar shine ɗansa ba, sai dai duk wani mummunan hali nashi na wulaƙanci da rashin son mutane ta hanyar Farida na ke jinsa saboda ta rigamu zuwa makarantar duk wani abu da ya danganceshi ta san shi sosai.

Salima ce take labarta min cewar Jibril shine ɗa na uku a gurin Mahaifinsa, kuma ɗa na farko a gurin mahaifiyarsa kasancewarta Amarya, yana da Step mother wacce ita ce ke da ƴaƴa da yawa kuma ita ta riƙashi a hannunta ya tashi, a gurin haihuwarsa Allah ya karɓi ran mahaifiyarsa wannan yasa mahaifinsa yake sonsa kuma yake tausayinsa domin ko da Jibril ya buɗe ido be san mahaifiyarsa ba sai step mother.

Wata ranar da muka yi practicing akan thigh surgery, ya yaba min sosai kuma ya nuna jindaɗinsa akan yadda na maida hankali sosai, a ranar kasa bachi nayi saboda farinciki duk bayan minti ɗaya zuwa biyu uku fuskarsa na ke gani.
Hakan yasa na ƙara maida hankali akan karatuna, da muka samu hutu sai muka soma shirin ziyarar gida kasancewar dkanmu munyi marmarin gida saboda haka muna samun hutun muka shirya muka dawo gida.
Bayan mun dawo Abuja da kwana biyu na fara shirye-shiryen zuwa gida sokoto domin ganin iyayena, ranar da anje gurin kitso na dawo sai Daddy ya aiko yana kirana.

A ɓangaransa na sameshi tare da Momi Aisha wato Hajiyarmu, da sallama na shiga bayan na gaishesu sai na maida kaina ƙasa ina wasa da carpet zuciyata cike da son jin dalilin kiran nawa, da farko na yi tunanin akan tafiyata ne sokoto ko kuma karatu.

‘Wata ƙila zai ce na haƙura har sai mun sake samun wani hutun ne ko kuma wani abun’

Haka na yi ta saƙe-saƙe na kamin na ji abunda Daddy yake faɗa.

“Nawwara ko akwai wani wanda kike so? Ko kuma iyayenki suke son haɗa ki da shi?”

Na yi mamakin da ya yi min wannan tambayar, a take Jamal ya faɗo min a raina na fara tunanin ko ya faɗawa Daddy wani abun ne, ko shiyasa tun da na zo ban ganshi ba. Cikin natsuwa da ladabi na ɗaga kai na kalleshi na ce

“A'a babu Daddy”

“Mashallah”

Ya faɗa yana sauke ajiyar zuciyar da ke nuna ya jidaɗin hakan, ya gyara zamansa yana fuskanta ta sannan ya ce

“Alhaji Bashir Makama aminane a tare muka taso tare muke duk wani abu da ya shafi siyasa ko kasuwanci, sai dai shi be cika zama a garin Abuja ba shiyasa ba ki wayeshi sosai ba, yafi zama Kaduna wato mahaifarsa sai kuma garuruwan da yake gabatar da kasuwancinsa.
Few days ago mun tattaunada shi akan ɗansa, yana son haɗa zuri'a da ni, ni kuma na duba a cikin ƴaƴana na ga babu wacce ta dace da shi sai ke, na yi hakan ne ba dan komai ba sai dan sama miki rayuwa mai kyau da nagarta, na san idan har kika auri ɗansa zaki ji daɗi sosai, saboda yaron yana da aiki ba irin ƴaƴan masu kuɗin nan ba ne shashashu kuma yana son yaronsa sosai, matsalar sa ɗaya baya son zaman da yake a waje kuma baya son yarinyar da yake tare da ita”

Sosai na ji babu daɗi duk da bani da wanda zan iya fitar a lokacin na ce gashi shi nake so, amman hakan yasa ni jin babu daɗi, sai dai ban yarda na nuna masa ba domin na san ba zai min abunda zai cutar da ni ba.

“Ai kin san Alhaji Bashir ko? Ɗan sa da yake waje yana aiki, ta hanyarsa ma Daddy mu ya samo muku gurbin karatun, ba zaki rasa sanin Jibril ba dan ance makarantar ku yake koyarwa, kuma a can zamu zauna sai kin gama karatun sannan ku dawo gida gaba ɗaya”

Wannan karon Momy ce take maganar da ta kwantar min da hankali kuma ta saka ni farinciki, cikin nuna tsantsar ladabi na ɗago na kalli Daddy na ce

“Ba zaka taɓa yi min abunda zai cutar da ni ba, ni kuma ba zan taɓa butulce maka ba, ko wuta ka kunna kace naje na shiga zan iya shiga na ƙone kaina balle aure, fatana Allaj yasa haka shine alheri”

Ya ji daɗin farucina har ma yasa min albarka shi da Momy sannan na taso zuciyata cike da farinciki fal na dawo sashenmu, jikin har rawa yake na labartawa Salima abunda ake ciki, ita ma tayi farinciki sosai sai da nayi mata alƙawari karta faɗawa kowa kuma karta nunawa Daddy ina sonsa, ita kuma ta yi min alƙwarin haka.

Bayan kwana ɗaya muka yi shirin zuwa sokoto ni da Salima wannan karon ma jirgi muka bi, Inna ta yi farinciki ganin sosai ni kaina ban san na canja ba sai a wannan lokacin na yi mamaki da Inna ta ƙara haihuwa ba tare da ƙara wasu shekaru biyar ba, kuma ace har anyi sunan Jamila ba a faɗa min ba.
Dare muke rayawa ni da Salima muna labarta Inna da Baba rayuwar waje, Habiba kan ta shige cikina tare muke kwana a shinfiɗa ɗaya, a wannan lokacin ne na samu damar ziyarar abokaina da muka taso tare ciki wasu kuma da muka yi makarantar islamiya da boko a tare kamin tafiyata Abuja, cikin har da Zinatu da Baraka da kuma Jidda a lokacin duka muna unguwa ɗaya kamin su Zinatu su koma kware road gawon nama.

Wasu basa yarda ina karatu a waje saboda suna ganin mahaifina ba kowa bane, kuma ba kowa ne mai arziki ba ne zai iya yi mana yadda Daddy ya yi mana. Inna ta labarta min yadda ake ta tsigumi a unguwarmu wai saboda kwaɗayin abun duniya zai siyar da mutuncin ƴarsa ya yarda naje na yi karatu bayan na secondry da aka ce na yi, a cewarsu wai yaƙi ya yi min aure jira yaƙe sai na gama karatun sai mai kuɗi ya zo ya aureni.

Ni kaina maganar bata min daɗi ba kuma daman nasan za a samu haka, mutane ba zasu taimakeka idan kuma wani ya tallafawa rayuwarka sai koma gefe suna zagi da ganin hakan be dace ba.
Sai da muka yi sati biyu a sokoto ana sauran kwana uku mu koma Abuja, Baba ya shigo ya same ni a ɗaki a lokacin ina ni kaɗai ya soma labarta min maganar da Daddy ya yi masa, ganin na ƙi cewa komai yasa ya kira Inna suka sakani a gaba akan ina son haka ko bana so domin shi ba zai yarda ayi min auren dole ba.

Ni kuma na yi shiru ban amsa ba, hakan ne ya tabbatar masa da ina so ɗin kamar yadda Annabi ya faɗa shirun budurwa shine amsarta.

“Amman yasan ke ba ƴar Alhaji ba ce ko? Saboda bana son ayi abu daga baya ya dawo na rashin daɗi”

“Wallahi Baba ban sani ba, amman na san ba zai rasa faɗa masa ba”

“Idan ma be faɗa masa ba ni zan buƙaci.ya faɗa masa, ƙara yasan ko wacece gudun kar sai anyi abu wani abu ya biyo daga baya, kuma ina son yasan mu talakawa ne iyayenki ba masu kuɗi ba, idan ya ji zai iya aurenki a haka walillahil hamdu idan kuma ya ce ƴar mai kuɗi yaƙe so sai mu jira Allah ya kawo miki na gari”

“Hakan shi yafi Allah ya zaɓa miki alheri”

Cewar Inna, ni dai ban ce komai ba, Allah kawai na ke roƙo ya zaɓa min abunda ya fi alheri. Bayan mun koma Abuja Momy take faɗa min wai cikin satin nan Jibril ɗin zai dawo dan haka na shirya tarbonsa a kowane lokaci, a lokacin hutunmu sauran sati uku ya ƙare.
Shiru-shiru Jibril be zo ba, da sunan ganin matar da zai aura, hakan ya tabbatar min da cewar shi ma baya son auren wata ƙila shi ma an masa yadda aka min ne, wato haɗi.

A week later Momi ta ce na shirya ni da Salima zamu je area 1 gurin abokin Daddy mu ƙarɓo saƙo, duk kalar tufafin da na saka sai Momy tace ba su yi ba naje na canja, kuma ni kawai take cewa ba da Salima ba, daga ƙarshe sai ta shigo ɗakinmu da kanta ta zaɓa min tufafin da zan saka kuma tasa na canja kwaliyar fuskata na feshe jikina da turare sannan ta kira direba ta ce ya kaimu.

Na samu kaina da faɗuwar gaba sanin gidansu Jibril ne zamu je, sai dai ko da wasa ban kawowa raina cewar zan je mu gaisa ba ne, iya abunda na zata zamuje karɓo saƙo ne wata ƙila yana nan shiyasa take son na yi kwalliya ta yadda ko da ya ganni ba zai raina ni ba, amman abun mamaki bayan mun isa gidan mun gaisa da Hajiya Zainab Step mother ɗinsa sai aka nuna min wani falo wai na shiga zamu gaisa da Jibril.

Na ji babu daɗi duk da kasancewar ina sonshi amman sai nake ganin kamar hakan be dace ba, shi da yake namiji ya kasa zuwa ya ganni sai ni da nake mace za a ce naje mu gaisaz, ba zan iya mata musu ba tunda ita a tunaninta Momy ta faɗa min haka tun gida.

Da sallama na shiga muryata can ƙasa-ƙasa, amman be amsa min ba kuma be ɗago ya kalleni yana ta aikin dannar wayarsa fuskarsa a haɗe kamar baƙin hadari, his perfume make me feel comfortable har na zauna duk da be min izinin zaman ba.
From head to toe ya kalleni sannan ya jinginar da kansa yana taɓe baki ya ce

“Ke kuma haka tarbiyar gidanku take? Mata su suke zuwa fira da kansu? What kind of woman are you, kin cika arha da yawa gaskiya abun har cikin gida”

“Ni ma ba a faɗa min da kai zan gana ba, saƙo aka ce min zan karɓa shiyasa yazo da ko mayafina baka isa ka gani a gidan nan ba”

Ba bashi amsa kai tsaye, sai ya tashi zaune yana taɓe baki tare da cigaba da kallona.

“Really? Kuma kika ci kwalliya haka? Kina tunanin zan ga kyauki ne ko? Mutumen da yake son ki zai yaba kyauki, amman ba ni ba dan ni kamar baƙin maciji nake ganin ki, ki taimaki rayuwata baiwar Allah ki ce baki so na, Wallahi zan biyaki ko nawa kike so”

“Kai miyasa ba zaka taimaki rayuwata ka faɗawa mahaifinka cewar baka so na ba”

Still bakinsa a mere ya miƙe tsaye yana zuba hannayensa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login