Showing 45001 words to 48000 words out of 138998 words
ba Mahaifiyarsa ce ta siye ruwan ba shine dai ya siya ya yi mata kamfen, taya ma zata siya mana ruwa haka kawai.
Bayan mai ruwan ya gama juyewa na koma na cigaba da wanke-wankena zuciyata na ta shauƙin begen Bilal, alƙairinsa nake ta tunawa da kuma irin son da yake yi ma Noor da kulawar da yake bamu, lallai idan har rayuwarsa zata kasance a haka har abada to kuwa matarsa ta yi dacen mijin da zai taimaka mata ta tashiga aljanna, domin ni kan nasan ba ajina bane domin babu yadda za'ayi mahaifiyarsa ta barshi ya auri bayan ta yi iƙirarin wayo kawai nake masa wai na yi aure har biyu kuma da yaro kuma na ce zan auri ɗanta shi da yake saurayi ƴan uwansa ma basa so mahaifinsa ne kawai be ce komai ba shi ma kuma ina tunanin baya ra'ayin haka.
‘Amman tun da shi yana son ki ina ruwanki? Ai da shi zaki zauna ba da iyayenshi ba’
Wata zuciyar ta tambayeni, har ga Allah idan har na ƙi auren Bilal saboda iyayensa zai iya ɗaukar na yi masa butulci ne kawai domin shi baya la'akari da wannan shi di kullum maganar ɗaya ai shi dai yana so na, na san ko da na aureshi ba zai taɓa bari kowa ya wulaƙantani ba kuma zai maida Noor kamar ɗansa.
Haka nake ta saƙe-saƙe na ina aikin har na gama na shiga wanka na fito ina ta tunanin alfanun auren Bilal domin ni dai har yau ban hango wata illa auren Bilal ba idan har iyayensa zasu amince ya aureni ɗin, sai dai kawai na shirya fuskarta familynsa masu uban yawa da cecekuce.
Abaya na saka na ɗauki ɗankwalin abayar na yafa akai na, na saka baƙaƙen talkami sai dai fuskata bata da wata kwalliya domin ko hoda ban shafa ba bayan man da shafa, na ɗauki jar jakata na saka wayata a ciki na nufi ɗakin Inna, ina shiga sai na sameta har yanzu tana bachi, daman na san za a rina tunda jiya ta raya dare da tunanin Habiba a duk lokacin da na farko zaune na ke ganinta saman carpet ta rafka tagumi nasan wannan ba zai rasa nasaba da maganar da na faɗa mata ba jiya lokacin da Mustapha ya zo. Tashin na ta ya zame min dole ne domin bana son na je aiki ba tare da ta sani ba, dan haka na taɓata a hankali na tasheta har ta buɗe ido sannan na faɗa mata zan tafi, addu'a tayi min da fatan nasara ni kuma na fice ina amsawa da Amin.
Kamar ni ake jiran an fito sai na samu motar kamfaninsu Jibril a tsaye direban yana neman yaron da zai aika, yana ganina ya yi saurin fitowa cikin ladabi ya miƙa min wasiƙar ni kuma na karɓa ina wani shu'umin murmushi na yi sighing sannan ya wuce ni kuma na jefa takardar a jakata na kama hanyar zuwa gurin aikin.
Ko da na isa bakin gate ɗin kamfanin, ƙarfe tara ta yi har da rabi, da fari guards ɗin dake bakin gate ɗin sun tareni a da na nuna musu id cart ɗina da ya rage ban ƙone ba a cikin kayan aikim kamfanin sai suka bani dama na shiga bayan sun tambayeni dalilin saka Uniform ɗin sai nan faɗa musu uniform ɗin ya ƙone ne, da na shiga kamfanin sai na nufi gurin da aka tanada domin aje wasu abubuwan da mutun yake shigowa da su wato wani ɗan katon cabinets ne da aka tana domin ma'aikatan gurin su riƙa aje komai na su idan sun rufe sai su tafi ta makullin. Wayata da jakata na aje bayan na kulle na nufi reception na rubuta sunana da kuma lokacin da na shigo sannan na yi musu complain ɗin bana da uniform sai suka ce na wuce kawai.
Da kunnena na ji lokacin da ɗayan yake sanar da zuwana a telephone da halshen nasara wato turanci.
Yadda na tarar da gurin ya tabbatar min da wata ta fanshe a aikin, domin alamu sun nuna wata ta yi mopping ɗin kamin zuwana. Amman hakan be dame ni ba na ɓa ɗaure mayafin abayata a kaina na ɗauki bokiti da mop na fara aikina mutane dake ta kai kawo a gurin na ta kallona domin sun san an yi mopping ɗin gurin ni kima na zo ina ƙara yi.
Irin ƙamshin turaren da naji lokacin da muka zo tare Bilal irinsa na ƙara ji a wannan karon, ƙamshin turaren dana tsana a duniya wanda ke haddasa min ciwon kai a duk lokacin da na jishi.
Ko da wasa ban yarda na juya ta baya da nufin ganin mai ƙamshin ba, duk da jikina ya bani akwai mutun tsaye a bayana. Mutane dake gurin da waɗanda zirga-zirga na ga duk sun fice ɗaga gurin kamar ƙyabtawar ido wata ƙila da kai ya yi musu magana da su fita domin ni ban ji kalma ko ɗaya ba, kawai dai na hango yadda duk suke shiga natsuwarsu daga bisani kuma naga sun tashi sun fice da sauri kamar wanɗanda aka kora.
Hakan yasa na juyo sai idanuwana suka sauka cikin nasa, hakan yasa ni haɗe fuska kamar baƙin hadari, na wulgarda abunda ke hannuna na nufi ƙofar fita, sai ya biyoni da sauri yana kiran sunana. Juyowa na yi a fusace ina jiran jin dalilin kiran sunan, shi kuma ya gagara cewa komai bakinsa sai rawa yake idonsa na yawo saman fuskata. Ganin ba shi da abun cewa yasa na juya na cigaba da tafiya lifted na nufa shi kuma yana biye da ni sai kiran sunana yake mutane dake gurin kowa yaja baya ganin ya nufo lifted waɗanda suke cikin office's kuma na kallonmu kasancewar duk office's ɗin glass door ne na ciki yana hango na waje kamar yadda na waje zai iya hango na ciki, kallon mamaki suke ganin yadda ya biyoni yana kirana ni kuma naƙi na tsaya.
Daf da zan shiga Lifted ya miƙa hannunsa ya riƙoni.
“Nawwara ki saurare ni mana....!”
Tassss na yi ƙarfin halin wanke masa fuska da mari mai kyau, har sai da ya lumshe ido, komai da ke hawa na uku sai da ya tsaya kasancewar ma'aikatan dake aikin gurin suka ɗauke hannayensa masu tafiya kuma suka tsaya cak suna kallon ikon Allah.
“Karka sake kuskuren kai Hannunka ka taɓa min jiki, ka ɗauka nima kamar sauran ƴan matanka nake ko? Karuwai masu binka? To ni ba ƴar iska ba ce kar hannunka ya sake taɓa jikina shashasha kawai”
Har lokacin da nake masa wannan furucin be buɗe ido ba, ni kuma ban fasa faɗa masa abunda nake so ba, a gurin baka jin ƙarar komai sai na muryata da kuma sautin takun talkamin Zinatu wacce ta doso inda muke rai a ɓace, tana ƙarasowa kusa da mu ta ware hannu zata rama marin da na yi ma Jibril sai ya yi saurin buɗe ido ya yi karaf ya riƙe mata hannu.
“Don't...”
Ya faɗa cikin muryarsa dake amsa amo biyu. Cike da tsananin mamaki Zinatu ta kalleni da kalleshi ta ce.
“Baka ga abunda ta yi maka ba?”
“She's My wife....”
Ya faɗa rinannun idanuwansa da suka kaɗe suka yi ja suna kaina, ni kuma na yi murmushin takaici na tattara yawun bakina na tofa masa a fuska.
“Tuuff Allah ya tsare Nawwara da zama matar Jibril, matar da ka kira da annoba yau ita kake kira da matarka? Matar da kace ganin baƙin maciji ya fi maka ganinta, matar da ka ce baka ƙauna bata dace da kai ba yau ita kake kira da matarka? Matar da ka wulaƙanta ka fifita karuwa akanta? Matar da ka kira mashiririciya ƴar talakawa ita kake kira da matarka? Matar daka zalumta ka dannewa haƙƙi ita kake kira da matar da baka son abokanka su ganta yau ita kake kira..”
“Enough....!”
Ban ƙarasa ba ya katsa min tsawa idonsa cike da ƙwalla wasu kuma sun ganganro zuwa kumatunsa. A maimakon na yi shiru sai hakan ya bani damar cigaba har ma da nuna shi da yatsa.
“Ba irin da bane Jibril, Nawwara da ka sani a baya ba ita ba ce a yanzu, tirr da kai Jibril, tirr da haihuwar ɗa irinka, na yi nadamar da na taɓa saninka a rayuwata, azzalumi macuci maha'inci, wanda be san komai ba sai zalinci da cin amana”
Hawaye nake ina faɗin wannan maganar kamar yadda shi ma yake hawaye kamar ba gobe, a ada ne na faɗa masa wannan maganar dukana zai yi har sai na faɗi uban da ya aikoni, amman abun mamaki sai ya faɗi saman gwuiyoyinsa ya fashe da kuka yana ƙoƙarin riƙa ƙafafuna abunda ya bawa kowa na gurin mamaki.
“Ki yi haƙƙuri Nawwara dan Allah ki yafe min...”
Da gaske hawaye yake kamar yadda nima nake hawaye na tsanarsa da kuma tuna irin zalumcin da ya yi min. Mutume nan ne ya shigo wanda ya taɓa shigowa a wacan lokaci da nake cikin office ɗinsa, shi ne ya yi ma duka ma'aikatan dake gurin magana suka fice da sauri ciki har da Zinatu da jikinta ya gama yin sanyi da mamaki.
Sai kuma rage daga ni sai Jibril sai kuma wannan mutumen, baya baya nayi sai Jibril ya matso da sauri ya rumgume min ƙafafu yana kuka kamar ba shi ba.
“I'm sorry Nawwara i'm so sorry”
“Haƙuri kake bani da gaske ko Jibril?”
Ya yi saurin ɗago kansa yana gyaɗa min kai a tunaninsa zan haƙura ne.
“Waya faɗa maka zan yafe maka? Miyasa zaka yaudari zuciyarka da abunda ba zai taɓa zuwa maka ba? Nawwara will never ever ever forgive Jibril for what he did to her, indai har wannan ne yasa ka riƙa aikamin wasiƙar aiki to ka daina wahalar da kanka”
Ya yi saurin miƙewa tsaye ya riƙa fuska yana girgiza min kai.
“No no no ba haka ba ne Nawwara i just want be close to you i need..”
“Close to epidemic? Close to black snake...”
Ya yi saurin rufe min baki yana kuka kamar ƙaramin yaro.
“Nawwara please...”
Hannu nasa na janye hannunsa ɗaga baki na ce
“Na tsaneka Jibril na tsani duk wani masoyinka, na tsani farincikinka kukanka shine farincikina na tsaneka Allah ya wandaranka”
Na juya cikin kuka na danna lifted ta buɗe na shiga, ina jin yadda yake ƙoƙarin riƙoni abokinsa ya hanashi. Ko da na fito reception kowa kallona yake nasan baya rasa nasaba da hawayen dake zuba a idona. Gurin dana aje jakata na nufa na ɗauka ina hawaye na fice.
#RB
#TEAM MUSTAPHA
#TEAM JIBRIL
#TEAM BILAL.
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
2⃣7⃣
*MUSTAPHA POV.*
A hankali ya yi parking ya fito daga motar kamar marar lakka ya nufi part ɗin mahaifiyarshi.
Tana hakimce saman kujeara ya shigo jiki ba ƙarfi kamar marar lafiya, gaba ɗaya sai ta tattara hankalinta ta maida gunsa tana kallonsa har ya zauna a kujerar dake gefenta na dama.
“Son na yi ta kiran wayarka kashe, tun da ka fita baka dawo gida ba sai yanzu hankalina duk ya tashi, kuma ka kashe duka wayoyinka”
“Ina Office”
Ya amsa mata cikin muryar dake nuna tsantsar damuwarsa. Tashi tayi takoma kusa da shi ta zauna tana ɗaga bayansa.
“Duk tsawon lokacin nan kana office? Haba son miyasa zaka riƙa wahalar da kanka kana damuwa ga abunda har ga Allah baka da laifi? Bafa kai ka kashe yarinyar nan ba dan mai zaka damu kanka su suka kashe ƴarsu da kan su”
Juyowa ya yi ya kalleta.
“Momi ke kika siye gidansu Nawwara?”
“What why would i?”
“Lokacin da naje gidansu Nawwara ta yi wani furuci da ke nuna an siye gidansu kuma an basu kwanaki kaɗan su tashi ke ce ko Momi?”
“Wato Mustapha har gidansu yarinyar nan kake zuwa fira? Yarinyar da basu da tarbiya ga shegen hassada ya yi musu yawa, dan Allah ka cire yarinyar nan a ranka Wallahi ba ajinka ba ce”
“Da ace ni na sakawa kaina son ta da na cire shi cikin sauƙi ba tare da kanki kin sani ba, na yi iya ƙoƙarina na ganin cewar na gujewa soyayyarta amman sai na kasa, babu yadda za'ayi na sakawa kaina ƙaunarta Momi Allah ne ya saka min”
Ya miƙe tsaye ya zuba hannayensa a ajihu.
“Please Mom ki maida musu da gidansu, kuma karki sake yin wani abu da zai takurawa rayuwarsu, idan har baki tayani neman yafiyarsu ba to be kamata ki ƙara ɓata min suna a gurinsu ba”
Yana kaiwa nan ya nufi ƙofar fita cikin yanayi marar daɗi, Hajiya ma miƙewa ta yi tsaye ta bishi da kallo har ya fice sannan ta ce
“Wato revenge ɗin da zata ɗauka ta haɗa ni da ɗana ko? Uhmm Wallahi Nawwara kin deɓo ruwan dafa kanki, duk kika ce zaki shiga tsakanina da ɗana bake ba kaf ɗanginku sai na hana musu zama lafiya, kuma Wallahi ɗana ba zai taɓa aurenki ba ƴar matsiyata kawai”
faɗa take tana huci tsabar jin zafin ɗanta ya kamu da son Nawwara. Ɗakin ta nufi tana da bala'i har su Zarah da Ikram suka fito ɗaga ɗakinsu jinyo muryarta tana matsifa.
*** *** ***
Around eight am kowa ya hallara a dinning ɗin cin abincin safe ban da Mustapha, hakan be damu Hajiya ba domin ta san halin da ɗanta yake ciki, sai kawai ta cigaba da jera kayan abincin tare da su Ikram da kuma Ma'u mai aikinta. Fitowar Alhaji ne yasa Zara dake ɗaki fitowa domin yin breakfast ɗin, ganin babu kowa a kujerar Mustapha yasa Alhaji ya kalli uwargidansa ya ce
“Yau ma ba zai yi breakfast ɗin ba?”
Ikram ta yi karaf ta ce
“Ai daman sai tara yake karyawa”
Hajiya kuma ta taɓe baki tana cigaba da haɗawa Mijinta tea ta ce
“Ai ina ganin tsakanin jiya da yau in ban da ruwa babu abunda Mustapha ya ci, ko jiya be fita aiki ba sai sha biyu na rana be dawo gida ba sai da isha'i”
Kallon rashin fahimta Alhaji ya yi mata yana ɗaukar tea da ta aje masa ya kurɓa
“Saboda mai?”
“Uhmm saboda yarinyar nan mana”
Wani dogon tsaki Alhaji yaja ya kalli Ikram a fusace ya ce
“Jeki kira min shi wannan ai iskancin banza ne”
Da sauri Ikram ta tashi ta nufi ƙofar fita, bata ɗauki dogon lokaci ba sai gata ta dawo falon tare da Mustapha dake cikin shigar kayan bachi.
“Good morning Dad”
Ya faɗa murya can ƙasa-ƙasa kamar wanda baya son magana.
“Seat”
Alhaji ya faɗa ba tare da ya amsa gaisuwar da ya yi masa ba, ba musu Musyapha yaja kujera ya zauna yana fuskarta Daddynsa, mahaifiyarsa taja kujerarta ta zauna tana kallon ɗanta a natse Alhaji ya fara magana ta yadda ɗan nasa zai fahimta.
“Mustapha ka daina damunka kanka nayi imani har ga Allah baka da laifi akan wannan lamarin, saboda ba kai ka kasheta ba iyayenta ne silar mutuwarta. And a part from her sister ka aje shi a gafe domin ba tsararka ba ce, idan ma aure kake so ka nemo ko ƴar wani gidace ni zan aura maka ita amman ba dai wannan yarinyar ba”
Sauke idonsa ya yi ya kalli tea ɗin da Ikram ta aje masa a gabansa sannan ya sake data kai ya kalli mahaifinsa ya ce
“Dady ita kaɗai ce macce da nake so”
“No Look Son yarinyar nan ba ƴar gidan mutunci ba ce sannan aurenta biyu fa kai kana sauranyinka ka ce zaka aureta, after that yaron dake hannunta yanzu ana zargin shege ne fa bashi da uba, wasu ma na cewa babu wani aure da tayi zaman banza ta yi abuja ta dawo da ciki sai wannan auren da ta yi na biyu, ba ƴar gidan tarbiya ba ce Mustapha ƙara ka auro ƴar mutunci kuma ƴar gidan mutunci”
Mahaifiyarsa ya kalla domin yasan ita kaɗai ce zata iya faɗawa Daddynsa wannan maganar, kallon mahaifinsa ya sake yi
“Amman ina fatar Momi ta faɗa maka ni na lalata ƙanwarta ko?”
Alhaji ya yi saurin girgiza kai.
“No no son ba kai ka ɓata ta ba, daman can yarinyar lalatacciya ce, mahaifinta ma ance sata ya yi da aka mashi aka masa shegen duka har ya mutu....”
Zarah dake aikin tsire baki tayi karaf ta ce.
“Wallahi sam yaran gidan nan basa da mutunci ko kaɗan”
Tsawa Mustapha ya katsa mata.
“Idan ana maganar tsakanin Uba da ɗa ki daina saka bakinki a ciki”
Momi ma ta katsa masa tsawa.
“Ta daina saka bakinta iya ba ƴar'uwarka ba ce? Wai mi yake damunka ne Mustapha?”
“Nima ban sani ba, kawai ni dai abunda na sani zuciyata na son Nawwara”
Ya amsa mata da cikakiyar gaskiyarsa, shi kansa a yanzu ba zai iya ayyana abunda yake damunsa ba, kawai dai yana samun kansa cikin wani kalar yanayi da be taɓa samun kansa a cikinsa ba. Alhaji ya buga tebur ɗin da ƙarfi
“Ba zaka aureta ba Mustapha, ana nuna maka hanya kana ba haka ba, ka bar ganin kai kaɗai na haifa zan iya shafe labarinka a doron ƙasa matuƙar ka zaɓi yarinyar can ƴar nasara mutunci”
Miƙewa ya yi tsaye ya nufi ƙofar fita ba tare da wata kalmar ta ƙara fitowa daga bakinsa ba.
“Could you see this?”
“Na gani, ni gani nake kamar ba banza suka barshi ba, dan ni ban taɓa ganin yarimyar da Mustapha ya zo ya ce min yana so ba duk wanda na gansu tare zai ce abokiyar aikinsa ce ko abokiyarsa, amman be taɓa buɗe baki ya ce min ga wacce yake so ba sai wannan zagalar, duk yabi ya canja saboda wata ƴar iskar yarinya, jiya ma haka ta zugoshi yazo ya rufeni da masifa wai na siye gidansu, ni kuma ban san na siye wani gida ba wata ƙila so take ya ɗauki maƙudan kuɗi ya ɗanka mata”
“Bari ai zamu saka ƙafar wando ɗaya da shi”
“Da shi kuma? Sai dai da su ai su suka susuta naka yaro, shi kaɗai fa Allah ya bamu idan ka saka ƙafar wando ɗaya da shi ai abun akan mu zai koma”
Ƙwafa ya yi ya cigaba da shan tea ɗinsa yana ta huci.
*** *** ***
JIBRIL POV.
Be bar kamfanin ba sai tara na dare, ko da ya isa gida jikinsa da mugun nauyi kamar wanda ya yi wani aiki, bathroom ya shiga ya sakarwa kansa