Showing 72001 words to 75000 words out of 138998 words
alwala ya yi sallah ya ƙara nemi yafiyar Ubangijinsa, sai dai hango Mahaifiyarsa da yayi jikin ƙofa tana kallonsa tana hawaye yasa shi yin zaune tana share nasa hawayen.
Ƙarasowa ta yi kusa da shi ta zauna kana ta riƙa hannunsa tana kallon fuskar ɗanta cike da tausayinsa.
“Son kuka kake yi?”
Ya yi shiru be ce komai ba.
“Zan je na nema maka yafiyarta, in har hakan zai faranta maka rai, damuwarka damuwata ce a duniyar nan bana da wani farinciki sai naka, amman ina son ka sani ba kai ne ka kashe yarinyar nan ba”
“Ba ni na kasheta ba Mom na sani, amman ina jin rashin kyautawa a abunda na aikata, sannan Allah ya jarabeni da abunda ban taɓa tsamani ba, son yayarta, kuma kun kasa fahimtar hakan balle ku goya min baya”
“Na yi magana da mahaifinka zamu nema maka yafiyar Nawwara, da kuma aurenta matuƙar hakan zai kwantar maka da hankali”
Ya yi saurin kallonta kamar be yarda ba.
“Mom da gaske?”
“Kai kaɗai na ke da a duniyar idan ban faranta maka ba wa zan farantawa? Bana son na rasa ka”
Ya kwantar da kansa jikinta yana murmushi tare da sauke ajiyar zuciya.
“Thank you so much Mom i love you”
“Love you more”
Ta faɗa tana hawaye, har ga Allah ba dan tana son nawwara zata nema masa ita ba sai dan kawai ɗanta ya samu salama hankalinsa ya kwanta, amman ita har gobe gani take ɗanta be dace da nata kamar Nawwara ba.
Sun daɗe a haka sannan ta sake shi ta fita shi kuma ya shiga banɗaku dake falon ya wanke fuskarsa ya canja Jalabiyar da ke jikinsa ya zuwa wata jalabiyar black sannan ya fito a compound ya nufi gurin da motarsa take ya shiga horn ɗaya mai gadin ya buɗe masa gate ya ɗauki hanyar gidansu Jidda.
Tun kamin ya ƙarasa ya kirata ya faɗa mata ta fito gashi ƙofar gida, sam ba zaka ganshi a yanzu ka ce mutumen ɗazu ne ba, farinciki ya mamaye masa zuciya ji yake kamar da Momy taje ta bawa Nawwara haƙuri haƙura zata yi ta kulashi.
Yana zaune cikin motar har Jidda ta fito sanye da Hijab tana tafiya kamar marar laƙƙa, jinginawa ta yi jikin motar yana miƙa masa gaisuwa shi kuma sai ya kashe motar ya fito yana murmushi.
Gabanta ya faɗi zuciyarta ta fara bata wani tunani na daban kar dai ya cutar da ƙawarta, mutumen da tasan yana cikin damuwa yanzu kuma har da murmushi a fuskarsa.
“Naje na yi magana da Nawwara amman har yanzu bata fahinta ba, har na faɗa mata maganar da be kamata ba, amman na san nan gaba zata gane kuma zata yafe maka ni dai abunda na ke fata karka cutar da ita dan Allah”
Ya sake yin murmushi yana kallonta fuskarsa da annuri.
“Zan iya cutar da kaina ban cutar da Nawwara ba, da kin san yadda na ke sonta da baki min wannan zargin ba, amman na san duk mutumen da yasan wanene dole zai zargeni, faruncikin da kika gani a fuskata na zo ne na faɗa min cewar Mom ta yarda har ma ta ce zata taimaka min wajen neman yafiyar Nawwara”
“Wow amman na yi farinciki, Allah ya shiga cikin lamarin kuma ya sa ta kula ka”
“Amin nima fatana nan”
Ya faɗa yana kallon hawayen da suka zubo mata, wanda hakan yasa shi wani tunanin na daban.
“Hawaye kike?”
“Ni?”
Ta yi saurin kai hannu ta share hawayen, da alama bata san sun zubo mata ba.
“Kawai ina farinciki ne”
Ya mata murmushi as respond ba dan ya gamsu hawayen nata na farinciki bane, ita kanta bata san hawayen mi take ba, iya abunda ta sani zuciyarta na yaudararta ne da son cuta mata abunda ta san ba zai taɓa yayuwa ba.
‘i'm very stupid taya zan so mutunen da ke son ƙawata?’
A fili kuma sai ta kalli Mustapha ta ce
“Zan shiga ciki”
Nan ma kai ya ɗaga mata yana murmushi da iya fatar baki kawai ya tsaya masa. Har ta juya sai ya kirata.
“Jidda...”
Ta juyo tana kallonsa
“Thank you”
“Anything for Nawwara”
Sai da ta shiga gida sannan ya juya ya shiga motarsa zuciyarsa na raya masa wani abu da baya son kawowa akansa, he's happy at first amman yanzu sai ya nemi farincikin ya rasa tunanin hawayen da Jidda take ya tsaya masa a rai.
Ko da ya isa gida part ɗin Mom ya fara shiga sai dai be sameta ba saboda bata gidan, Ikram ce kawai a falon tana game, yana shigowa hankalinta ya dawo kansa.
“Mom taje zata yi magana da Nawwara abunda ka daɗe kana jira amman kuma sai naga kamar baka farinciki”
Ya kalleta irin kallon nan na sai yanzu ya lura da maganar da take.
“Ofcourse am happy i was just thinking of something else”
“Like?”
Sai yayi murmushin da ya bayyana haƙoransa ya miƙe ya shiga kitchen yana faɗin
“Manta kawai ba wani abu bane mai muhimmaci”
Freezer ya buɗe ya ɗauko gorar ruwa ya kai a bakinsa ya sha sai kuma ya nufi gurin window yana ta tunani.
“Impossible”
Ya sake cika bakinsa da ruwa, sai kuma ya yi murmushi yana sauke ajiyar zuciya.
“I love you so much”
Ya daɗe a kitchen ɗin sai da yaji motsin shigowar Mom sannan ya juyo ya fito riƙe da gorar ruwan ya nufo falo.
“Mom ya kuka yi?”
Ya tambaya tun kamin ta cire mayafin da ke kanta, sai dai bata bashi amsa ba sai da ta zauna saman kujera fuskarta da murmushi.
“Sun ce ba zasu yafe ba”
“You must be joking Mom”
“Ka ci gidanku, ni zan maka wasa”
Ya zauna kusa da ita yana kallon murmushin da ke fuskarta.
“Na yi magana da su kuma sun ce sun yafe maka, baka ga yadda mahaifiyarta ta tarbeni ba kamar daman can babu komai”
“Da gaske? Amman Nawwara fa?”
Ta ɗanyi shiru sannan ta ce
“Ita ma ta yafe maka har ma tace a gaisheka”
“Mom da gaske”
“Sai kaje ka tambaya idan baka yarda ba”
Wani irin tsalle ya yi ya dare kamar mahaukaci.
“Mom i love you so much”
Mom ma tana farinciki ganin farincikin ɗanta, cikin zumuɗi ya fice daga falon ya nufi part ɗinsa. A ranar kasa bachi ya yi saboda farinciki, sai ya kwana yana istigifari da hamdala ga Ubangijinsa, a zatonsa da gaske Nawwara ta yafe masa har ma ta miƙo gaisuwar gunsa.
Around eight o'clock in the morning Mustapha ya fito part ɗinsa zuwa part ɗin Mom, sai dai hango motar abokinsa da ya yi yasa shi tsayawa baƙin ƙofar yana jiran ya ƙaraso.
NAWWARA POV.
Cikin rashin daɗin rai na shiga gida, Inna ma ta lura da haka sai dai bata cemin komai a zatonta tsakanina da Bilal ne wani abu ya faru. Misalin takwas da rabi na dare muka ji sallama a ƙofar gida, Inna ce ta amsa ni kuna idona na kan Noor take ta faman game baya gajiya. Sarai muryar Hajiya mahaifiyar Mustapha a ɗaki kunnena a sallamarsa ta biyu, gabana ya faɗi ba dan tsoro ba sai dan tunanin abunda yake tafe da ita. Inna ce ta unƙura ta fita sai kuma ta dawo ta ɗauki tabarma ta sake fita, sama sama nake jiyo firar da suke da dukan alamu yafiya take nemawa ɗanta abun mamaki har da su wa'azi da nuna ƙaddara, zuwa can kuma dai na ji Inna ta kirani daga inda na ke na amsa mata sannan ya miƙe na fita.
Hajiyar ce zaune saman tabarma yayinda Inna take zaune saman kujerar mata ta tsakar gida.
“Nawwara ce”
Hajiyar ta faɗa tare da kunna fitilar wayarta ta haska fuskata.
“Ina wuni?”
“Lafiya ƙalau, ayi ta haƙuri kinji haka abubuwan duniya suke zuwa”
“Allah ya bamu haƙuri”
Daga haka ban ƙara cewa komai ba na miƙe tsaye na dawo ɗaki. Bata ɗauki tsawon lokaci ba tayi ma Inna sallama ta fice. Inna kamar jira take tana shigowa cikin ɗaki ta hau ni da masifa.
“Wannan halin ba na ki ba ne Nawwara ba irin wannan tarbiyar muka baki ba, yafiya da afuwa ga wanda ya yi maka ba daidai shu aka fi ga musulmi, duk yadda zaki so Habiba ko ki nuna baƙincikinki akan mutuwarta be kai ni uwarta, tun da har na yafe kema ya cancancanta ki yafe, Ƙaddarace ni da ke duk ba mu wuce faɗawa a cikinta ba, yanzu da ace ɗan uwanki ne ya faɗa a wannan halin ko kuma ɗan ki Noor yaje yana neman yafiyar wata ba ta yafe masa ba zaki jidaɗi? Komai zaka yi ka riƙa kwatantawa da kanka”
Tun da take maganar na ke hawaye, Inna ta min fahimta baibai, ta kasa gane irin zafin da ɓakincikin rashin yar'uwata da nake, ko da Habiba tana raye dole na ƙyamaci Mustapha saboda ya yaga mata rigar mutunci, tana ɗora min laifi akan Jibril saboda tana ganin kamar na zufafa da yawa, ni kou na san irin zafin da na ke ji idan na tuna wulaƙancin da ya yi min ya yi min ƙazafin zina a gaban iyayensa da iyayana yasa mutane unguwa suka kira ɗa na da shege ni kuma aka kira da karuwa, irin waɗannan mutanen ne take ganin na zufafa ƙiyayyata a garesu?
“Ki yi haƙuri Inna, zan yi iya abunda zan iya na danne zuciya daga abunda take ji, dan Allah ki yi haƙuri kuma ki roƙa min Allah ya sassauta min abunda nake ji”
Na faɗa ina ta kuka kamar zan haɗiye zuciya na mutu, sai Inna ta zauna kusa da ni ta dafani tana lallashina.
Sama sama na samu bachi a daren ranar saboda kuka da na kwana ina yi ga kuma tunani ƴar uwata da ya dawo min sabo. Washe gari da wuri na farko bayan na gama raka'atayal fajir sai na jira aka tayar da sallah na masallaccin da ke kusa da mu bayan na gama na karanta azkar na safe, da ayatul kursiyu na fara
A 'oothu billaahi minash-Shaytaanir-rajeem. Allaahu laa 'ilaaha 'illaa Huwal-Hayyul-Qayyoom, laa ta'khuthuhu sinatun wa laa nawm, lahu maa fis-samaawaati wa maa fil-'ardh, man thai-lathee yashfa'u 'indahu 'illaa bi'ithnih, ya'lamu maa bayna 'aydeehim wa maa khalfahum, wa laa yuheetoona bishay'im-min 'ilmihi 'illaa bimaa shaa'a, wasi'a kursiyyuhus samaawaati wal'ardh, wa laa ya'ooduhu hifdhuhumaa, wa Huwal- 'Aliyyul- 'Adheem.
sannan ɗora da ƙula'uzai
Allahu ahad, Allahu assamad, Lam yalid walam yoolad, Walam yakun lahu kufuwan ahad.
Qul a'aoothu birabbi alfalaq, Min sharri ma khalaq, Wamin sharri ghasiqin ithawaqab, Wamin sharri annaffathatifee al'uqad, Wamin sharri hasidin itha hasad.
Qul a'aoothu birabbi annas, Maliki annas, Min sharri alwaswasi alkhannas, Allathee yuwaswisu fee sudoori annas, Mina aljinnati wannas.
Sai kuma na karanta hasbiya ƙara bakwai
Hasbiyallaahu laa 'ilaaha 'illaa
Huwa 'alayhi tawakkaltu wa Huwa Rabbul-'Arshil-'Adheem
Sai kuma na karanta
Bismillaahil-lathee laa yadhurru ma'as-mihi shay'un fil-'ardhi wa laa fis-samaa'i wa Huwas-Samee 'ul- 'Aleem.
Ƙafa uku.
A'oothu bikalimaatil-laahit-taammaati min sharri maa khalaqa
Sau uku
Waɗannan addu'o'i ne na neman tsari matuƙar ka karantasu babu abunda zai same ka daga iska har tsafi har ma da wasu ƙwari masu cutarwa, bayan na gama na ɗora da azkar ɗin godiya ga Allah waɗanda ake son musulmi ya karanta safe da yamma. Sannan na rufe da shugabar istigifari wato
Allaahumma 'Anta Rabbee laa 'ilaaha 'illaa 'Anta, khalaqtanee wa 'anaa 'abduka, wa 'anaa 'alaa 'ahdika wa wa'dika mas-tata'tu, 'a'oothu bika min sharri maa sana'tu, 'aboo'u laka bini'matika 'alayya, wa 'aboo'u bithanbee faghfir lee fa'innahu laa yaghfiruth-thunooba 'illaa 'Anta.
Yana na gama na yi salatin annabi ɗari istigari ba ɗari, sannan na yi hasbiyalahu sau ɗari huɗu da hansi, wacce ake karantawa a duk lokacin da mutane yake cikin matsala na halin rayuwa ko neman mafita, kamar neman aure warwarewa al'amura duk ka lamuncin karantawa zaka samu mafita cikin gaggawa.
Ko da na fito har Sakina ta dama kamu, Inna kuma ta aiki Jamila da Noor su siyo ƙosai da suga, bayan sun dawo muka sha kunun har Inna sannan na kama kan Noor na yi mas addu'a irin wacce Annabi yake yi ma jikokinsa Hasan da Husaini
U'eethukumaa bikalimaatil-laahit-taammati min kulli shaytaanin wa haammatin, wa min kulli 'aynin laammatin.
Bayan na gama da Noor na karantawa Jamila sannan na suka kama hanyar makaranta tare da Sakina. Ni kuma na tashi na shirya cikin wata atamfar roba na saka Hijab ɗina mai kama da atamfata, sannan na zo yi ma Inna sallama da karɓar kuɗin Napep.
“Inna zan tafi aikin”
“Allah ya tsare Nawwara Allah ya miki albarka, ban miki faɗa jiya dan wani abun ba sai dan ki gyara”
Ta faɗa tana miƙo min ɗari biyu.
“Ko babu komai kika min faɗa ba zanga laifinki ke uwace kina da damar ki yi duk yadda kike so da ni, kuma abunda kika min faɗa akai kina da gaskiya, ni kaina na san ina da buƙatar ganin na canja ta yadda zan cigaba da rayuwa na manta komai, ni dai fatana ki kasance mai min addua da kuma haƙuri da hali na miki alƙwarin zan canja”
“Addu'a ai wajibi ce ga dukan uwa ta yi ma ƴaƴanta, Allah ya miki albarka ya baki miji na gari wanda zaki ji daɗin zama mai son ki tsakani da Allah”
“Amin Inna”
Na faɗa ƙasan zuciyata na ta kira min Bilal, tun jiya be kirani ba kuma be dawo ba ni kuma ban kira ba.
Sai da na fito daga gidan sannan na soma kiran Bilal amman wayarsa a kashe, hakan yasa ni jin babu daɗi zuciyata na raya min kamar fushi yake da ni, daman na san dole sai ya zargi wani abu ganina tare da Mustapha.
Na yi sa'ar samun napep da wuri amman sai da ya sauke mutun biyu sannan ya ƙarasa da ni inda zai kai ni, koda na isa tara saura kwata tunda na doshi kamfanin zuciyata ta soma rayamin wasu abubuwan sai sai tunawa da maganganun Inna yasa na kawar da komai na nutsa kai cikin kamfanin, na yi mamakin yadda kowa yake kallona kamar wace suka ga baƙuwar fuska, wataƙila an faɗa musu wani abun ne akai na ko kuma dan na yi latti suke kallona oho, ban damu da cire Hijabina ba a ganina yanzu ai an canja min aiki dan haka bana buƙatar cire Hijabi duk kuwa da kasancewar ban taɓa ganin kowa da Hijabi ba a kamfanin.
Har na doshi lifter tunani na ke irin kallon da Jibril zai min da kuma irin wanda zan yi masa idan har na yi aiki a gurin. Ina dosar office ɗinsa gabana ya shiga faɗuwa, ba faɗuwar tsoro ba ko fargaba ba faɗuwa irin ta maƙiyi zai yi arba da maƙiyinsa.
Kamar wacan zuwan nawa na farko haka na yi saka buɗe min, yau ma sai da aka tantance ni a cikin ɗan ƙaramin gilashin nan mai bayyana komai na jikin mutun sannan aka bani damar shiga Office ɗin, ban ji ya ce na aje wayata da ƴar ƙaramar jikar da ke hannuna ba, ni kuma ban aje ba na shiga da abu ta, shi ɗin ne dai mutumen da na taɓa tararwa wacan karon. Tun kamin na yi magana ya rigani.
“Please go in”
Ya doshi ƙofar da ya nuna min gabana na ƙara faɗuwa, ajiyar zuciya na sauke sannan na kai hannu ya tura ƙofar, ba tare da na waigo ba na maida ƙofar na rufe ina kallon bayansa, kasancewar ya bani bayana ne domin shi yana tsaye ne jikin window ya maido hannayensa baya yana kallon waje.
Har yanzu akwai tattoo ɗin taurari a bayansa, mamaki ya kamani sosai ganin sunana rubuce cikin style ɗin wasu harufa tattoo a hannunsa, nasan be san da shigowata ba ko da yake yaji an buɗe ƙofa, ni kuma na gagara kiran sunansa sai kawai na ce
“Excuse me”
Da sauri ya juyo ya kalleni, irin kallon nan na mamaki sannan ya yi hanzarin warware hannun rigarsa ya nufi ƙasaitacciyar kujerarsa ya zauna.
“Kin zo latti, ba a faɗa miki 8am zaki riƙa zuwa ba?”
Na yi shiru ban amsa masa ba. Sai ya soma kallona daga sama zuwa ƙasa.
“Ba a saka mana Hijabi a nan next time ki san irin tufafin da zaki saka”
“Ba za'a saka muku Hijab ba saboda ku ba musulmai ba ne?”
Ya yi murmushin gefen fuska sai ya taso daga inda yake ya doso ni yana faɗin.
“Aiki muke a nan ba addini ba”
“Da wannan aƙidar ka cuci kanka, kai kana ganin kamar babu ruwan addini ko Allah a cikin abunda ya shafi aikinka ko rayuwarka ko? Kana da mummunar aƙida Jibril”
“Ko?”
Ya tambaya yana ta matsowa kusa da ni ni kuma ina matsawa baya, har sai da na kai jikin ginin ɗaki, sosai ya matse ni yana kallon fuskata idanuwa cikin nasa idon, har na buɗe baki na yi magana sai ya duƙa ya kama zanen atamfata ya murja.
“Me kake ƙoƙarin yi ne?”
Ya miƙe tsaye bakinsa kusa da nawa kamar zai haɗe bakinmu.
“Dirty mind, ni ba ɗan iska ba ne”
Ya faɗa kaɗan kaɗan kamar mai raɗa, sannan juya ya doshi kujerarsa. Hakan ya bani damar lumshe ido na sauke ajiyar zuciya, jin abunda yake faɗa yasa ni buɗe idon ina kallon yadda ya haƙimce saman kujerarsa mai juyawa yana min magana cikin isa.
“Dan me za ki saka min tamfar roba?”
“Ba kai na sakawa ba, kaina na sakawa”
“Miyasa kika yi rejecting kuɗin da aka baki ki siye wasu tufafi?”
“Bana da buƙata, tufafin jikina sun isheni”
“Saka ƙananan tufafi marar daraja na zubarwa kamfanin da ƙima, ya kamata ki san wannan”
Ya faɗa fuskarsa babu alamun dariya, sannan ya danna telephone ɗin da ke kusa da shi ya yi magana da halshen nasara.
“You can go now”
Sannan ya kalleni.
“Tea please”
Tsaye na yi a gurin kamar an dasani, shi kuma ya bawa banza ajiyata yana ta aiki da system ɗin da ke gabansa. Waige-waige ɓa farayi har na hango teburin dake ɗauke da kayan tea na doshi gurin zuciyata na ta raya min maganar ɗazu, wai shi ba ɗan iska ba ne, wato ni ce ƴar iskar ko? Har na haɗa tea ya kawo masa maganar bata daina min yawo a kunne ba.
“Ƙarfe uku zaki tashi aiki, idan kuma har muna da meeting ko aiki da yawa zaki iya kaiwa har dare, kuma a shigo min office haka nan kawai, saboda karki tararda ni cikin wani yanayi, har sai idan ni na kiraki, idan wata magana ce akwai telephone a gurin dannawa kawai zaki yi ki kirani”
Ban ce masa komai ba na juya na fita, zuciyata na mugun ƙuna, anya zan iya jurewa na yi aiki a ƙarƙashin Jibril?
Sai da na ƙarewa office ɗin kallon sannan na zauna a saman