Showing 114001 words to 117000 words out of 138998 words
da ni komai ba suka tafi Noor nata dariya yana dago min hannu.
Cikin gida na dawo na dora girkin rana, sannan na dauko tufafin Inna da suka yi datti muka soma wankewa ni da Sakina muna fira sama sama, sai dai faduwar gabana na ta karuwa, ina jin kamar na yi kuka kuma ba dan a min wani abun ba.
Da la'asar Jibril ya aiko da dare bansa a daukar masa Noor sai na fadawa direban cewar basu dawo ba, daman idan suka fita wani lokacin har isha'i suna kai wa basu dawo ba, direban na wuce da kamar minti biyar sai ga Bilal ya kirani a waya hankalinsa a tashe.
“Nawwara Noor ya dawo?”
“Aa kun dawo ne?”
“Bayan fitar mu be dawo ba?”
“Aa be dawo ba, lafi... ”
Kamin na tambaya ya kashe wayar, ni kuma jikina ya yi sanyi na soma ambaton Allah a hankali
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
[11/10, 6:59 PM] Farar Mace...: *RAI BIYU...♥🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
5⃣3⃣
Jina yi kamar bana da karfi a jikina na kasa shanyar da na ke, sai na zauna a gurin gabana nata faduwa.
“Nawwara”
Inna ta kirani saboda ta lura da yanayina, sai na kasa amsa mata saboda kukan da ya cika min zuciya nasan ina bude bakina zai fito.
“Lafiya miya faru? Dawa kike waya?”
“Bilal ne, tambayata yake wai Noor ya dawo”
Na fada ina ta kokarin danne kukana.
“Kamar ya? Ba tare suka fita ba”
“Tare suka fita”
“Amman shine zai kira ya tambaya ya dawo bayan kuma ya san tare suka je? Wane irin rainin wayo ne wannan?”
Cewar Sakina tana matse zanen Inna.
“Wata kila wani abun ne ya faru, ina ji jikina ba dadi”
“Tun jiya na lura da ke sai dai nasan matsalar bata wuce tsakaninki da Bilal ba shiyasa ban yi magana ba, sabodana bana son ina yawan shiga fadanku, amman babu abunda zai faru da Noor Inshallah”
Ajiyar zuciya na sauke ya share guntun hawayen da ya zubo min na tashi na koma bakin kofar dakinmu na zauna, Sakina ta cigaba da wanke kayan. Haka muka zauna shiru har aka kira magariba Bilal be sake kirana ba gabana kuma be daina faduwa ba. Bayan na sallah isha'i na dauki waya na zimmar na kira Bilal sai kuma nake ganin rashin dacewar hakan, saboda ya saba fita da Noor su kai har dare basu dawo ba, dan me yanzu zan soma kiransa ai sai ya zargeni yace ko dan munyi fada ne, haka na maida wayar muhallinta na aje, kamar Inna ta san abunda ke raina sai kawai na ji ta ce
“Karki ji kunyar kiranshi Nawwara, ki kirashi mana ko muma hankalinmu zai kwanta”
Ba musu na daga wayar na kira number Bilal amman har ta gama ringing be dauka ba, haka na jera masa kira hudu be daga ba, daga baya kuma sai naji wayar a kashe, hakan ya kara fadar min da gaba, ina kokarin fadawa Inna cewar wayarsa a kashe take sai ga sakon Jibril ya shigo.
_Nawwara Noor ya dawo? Ina son gani dana zan aiko da mota yanzu_
Ni kuma na yi saurin mayar masa da sakon cewa basu dawo ba, sai ya sake aiko min da wani
_Dan Allah karki shiga tsakanina da dana Nawwara na roke ki, kiyi min duk abunda zaki min amman karki hana min Noor_
_Idan sun dawo zan fada maka_
_Gani nan zuwa na dauki dana_
_Aa karka zo_
Bw sake cemin komai ba, nasan be yarda da ni bane yana ganin kamar ina kokarin hana masa Noor ne.
“Inna na ta kira na kira be daga ba daga baya kuma sai aka kashe wayar”
“Allah dai yasa lafiya”
Cewar Inna ni kuma na amsa da Amin, kamin mu hada baki gurin amsawa Jidda da ta shigo a yanzu kamar marar lafiya, ina kallonta na san ba lafiya ba, sai dai ban kawo cewar maganar Noor bane saboda a tunani bata san sun fita ba. Kasa gaisawa ta yi da Inna sai kawai ta sakar min ido hawaye ya soma mata zuba
“Ke lafiyar ki?”
Na tambaya ina dafata.
“Nawwara”
Sai kuma ta yi shiru kamin ta cigaba.
“Dazu da Bilal ya fita da Noor wai ya tsaya da shi a AGG MALL ya siya masa chocolate shine sai yaga wani abokinsa suka tsaya gaisawa, wai Noor ya fito daga ciki ko da suka gama gaisawan ya nemeshi ya rasa”
Nina mike tsaye da sauri Inna kuma ta dinga furta
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Sakina kuma ta dora hannu saman kai tana kiran
“Mun shiga uku”
“Yanzu ina shi Bilal din yake?”
Inna ta tambaya hankalinta a tashe.
“Yana can gidansu, wai besan yadda zai fada muku ba shiyasa be zo ba tun dazu, nima yanzu yake fada min kuma ya ce ya bada report gurin yan sanda da gidan radio”
Ni dai ban iya cewa komai ba ban da hawayen da nake, muna haka naji tsayawar mota a kofar gidanmu wanda hakan ya tabbatar min da cewar Jibril ne kuma daman yana kusa da unguwar a lokacin da ya kira.
“Ga Jibr.. Il nan... Yace tafiya zai yi da Noor”
Na fada muryata na rawa.
“Ki fita ki fada masa gaskiya dole ne ya sani”
Inna ta umarceni, tashi na yi na fita ina hawaye, nasan Jibril ba zai yarda ba amman ya zama dole na fada masa, ko da na fito yana jingine jikin motarsa yana danna wayarsa da alama ni zai kira.
Fitowata tasa ya dago kai ya kalleni yanayin yadda na ke tafiya na doso shi yasa ya kunna fitilar wayarsa ya haska fuskata.
“Karki fara min complain ba gurinki na zo ba Wallahi, kawai zan dauki dana ne kuma nasan idan ban zo da kaina ba ba zaki bari taje ba, and i need to be with my son”
“Jibril.... Noor ...... Noor”
Na kasa magana saboda kukan da ya ci karfina. Ya sakar min ido sosai yana son jin abunda zai fito daga bakina.
“Noor ya bata....”
“What? How?”
Na kasa magana sai kuka na ke.
“Look Nawwara, idan ma kin shirya hakan ne dan ki samu nisanci da ni to wannan ba hanya ba ce, dan zan iya jure komai ban da rashin Noor, dan Allah ki canja tsari”
“Wallahi ba wasa na ke ba Noor ya bata”
Ya tsaya kallona dan tabbatar da zancen da nake gaskiya ne ko akasin haka.
“Kamar ya Noor ya bata bata ya bata ya bata as how?”
Ya tambaya yana mai daga murya tare da hannyensa sama, ni kuma sai kuka na ke ina ta kokarin rufe baki.
“Ki daina wannan banzan kukan naki ki fada min yadda aka yi dana ya bata”
Na razarana sosai saboda yadda ya katsa min tsawa da kuma irin bacin ran dake cikin muryarsa.
“Da suka fita da Bilal shine suka tsaya Agg mall siyen chocolate sai ya nemi Noor ya rasa”
Ya yi dariya marar sauti
“Ki ce Bilal ya sace min yaro ya siyar ko kuma ya boyeshi ya nemi kudin fansa”
“No Bilal ba zai yi haka ba, Wallahi Bilal ba zai taba cutar da Noor ba”
“To wa zai cutar da shi waya batar da shi a yanzu?”
Ya fada a tsawace.
“Wallahi Bilal ba zai cutar da Noor...”
Hannunsa ya daga zai mareni sai kuma ya kaiwa gilashin motarsa bugun yana wani irin huci.
“Akan dana zan iya taba kowa Nawwara kuma kowa da kowan nan har da ke, idan kin san wani abu ne kula da Bilal tau ki gaggauta kanwace shi tun wuri”
Yana fadar hakan ya bude motarsa ya shiga ya bar ni nan tsaye ina aikin kuka, sai ga Sakina ta fito da gudu ta nufi hanyar Babban gida, ni kuma na juya na koma, ko da na shiga Inna na ta buge bugen waya tana kuka kamar yadda Jidda take.
Ko da tara na dare ya yi gidanmu ya cika da jama'a makota da kuma yan uwa, maza suna suka shiga gari inda ake sa ran za a ganshi har Agg mall din anje amman ba a ganshi ba, ko da Baba Sulaiman ya aika Sakina ta kira masa Bilal sai ta dawo ta fada mana cewar wai yana police station an tafi da shi tun dazu, kowa yayi mamakin wanda zai kulle Bilal a wannan lokacin sai da Baba Sulaiman da Inna suka fada cewar Jibril ne, a ranar duk wanda yake cikin gidan nan ya tabbatar da cewar Noor yana da Uba.
Ni da Inna da Mama turai da Baba Sulaiman da Sakina da kuma Jidda muka kwasa muka je station din, daidaikun mutanen unguwa suka bimu saboda gulma. Mun tararda Jibril a can sai mahaifin Bilal da mahaifiyarsa tana ta kuka, sai wani kanensa daya.
“Ina Bilal din yake?”
Inna ta tambayi Mahaifinsa sai ya amsa mata cikin rashin dadin rai.
“Yana can ciki sun ce ba zasu fito da shi ba, tun dazu muke a nan tsaye babu irin rokon da ba mu musu ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Cewar Inna, ni kuma na doshi gurin Jibril sai yayi saurin tashi ya fice daga station din, da gudu na bishi ina kiran sunansa daker ya juyo ya kalleni fuskarsa babu annuri.
“Minene”
“Wallahi ba Bilal ba ne ya sace shi”
“Ke kika sace shi”
“Wallahi ba Bilal ba ne, dan Allah ka kyale kasan yan sandan nan basa da mutunci zasu iya ji masa fa”
“Ke ta Bilal kike ni kuma ta da na nake, babu ruwana da alakarku ya fito min da da na ya zauna lafiya”
Yana fadar hakan ya bude motarsa ya shiga ya barni nan tsaye.
Wasa wasa aka kwashe kwana uku ana abu daya, Jibril ya ki bari a saki Bilal saboda yana zargin shi ya batar masa da da, ita kuma mahaifiyar Bilal da yan uwansa suna dora laifin akaina, a ganinsu ko da da gaske Bilal ya batar da Noor ai be cancanci a ayi masa irin wannan wulakancin ba, har fade take wai danta be taba zuwa cell ba sai dalilina, babu irin magiyar da bana ma Jibril amman kullum maganarsa daya Bilal ya fito masa da da, ni da shi baka iya tantance waye ya fi shiga damuwa, sai dai Jibril ya fini shiga tashin hankalin sosai saboda haukacewa yake kokarin yia kan neman dansa, har mahaifinsa sai da ya zo har sokoto saboda wannan maganar Noor, kullum mafarki na Noor sai dai har yanzu zuciyata bata zargin Bilal. Ranar talata ranar da mahaifin Jibril wato Alhaji Baahir ya yasa a kashe maganar gurin yan sanda muna station mu dukanmu Jibril ya saka Bilal gaba yana masa magiya har da kukansa.
“Dan Allah dan Annabi Bilal ka fada min inda da na yake? Idan kudi kake so ka fada min zan baka ko nawa ne, kuma Wallahi na maka alkawari ba zan bari a ama ka komai ba, amman Noor shi kadai ya rage min ka tausaya min Bilal dan girman Allah”
Bilal ya kasa magana sai hawaye yake, gaba daya kamaninsa sun canja.
“Wallahi Bilal be dauki Noor ba”
Na fada cikin kuka, sai mahaifiyar Bilal ta kwatse ni.
“Ke dan Allah can rufewa mutane baki, baki fada tuntuni ba sai yanzu tsohuwar munafuka, ko da yake Allah ya kara ai kai ka ce ka ji ka gani”
Ban kara mata magana ba, har muka fito station din, muna dawowa gida sai ga Jibril ya iskoni har gida be tsaya a waje ba ya shigo cikin gidanmu da sallama ba tare da ya nemi uzinin shiga ba, ban tabbatar da irin ramar da yayi ba sai a wannan lokacin idanuwansa sun fada sosai. Gaban Inna ya je ya risina yana hawaye kamar karamin yaro
“Inna na rokeki ki saka Nawwara ta fada min wani abu akan batan da na, shi kadai ya rage min a duniyar nan, yau kwana hudu kenan ba a ga Noor ba, duk wanda ya dauke ke Noor rayuwarsa yake so ba kudi na ba, da kudi nane da yanzu an kira an ce na bayar, babu inda ban duba ba, babu irin binciken da ban sa anyi ba amman an kasa ganin Noor”
Inna ta kasa ce masa komai, ni da nake zaune nesa da ita na kalleshi cikin hawaye na ce
“Ban san komai a akan batan Noor ba, idan kuma baka yarda da ni ba, zaka iya sakawa a kulleni kamar yadda ka yi ma Bilal”
“Na rasa mahaifiyata Nawwara a lokacin da ban san miye duniya ba, ban sani ba ko zan iya jure rashin Noor”
Haka kawai ya fada ya mike tsaye ya shafa kansa ya fice. Sai da ya fice sannan Inna ta ce
“Miyasa baki fada masa gaskiya akan abokinsa ba? Mai yiyuwa shi ya sace Noor”
“Idan kuma ba shi bane fa Inna? Sai mu dauki laifin mu dora masa? Mai yuyuwa yan satar mutane ne suka sace shi ko kuma yan garkuwa da mutane sai mu dauki laifin mu dora masa?”
“Amman idan ba a bullowa wannan matsalar da wuri ba zata iya zama babba, kina da dalili da hujja mai karfi ta zargin wannan mutumen kuma shi kadai ya rage a yanzu wanda zamu iya zargi”
Tabbas ni kaina zuciyata a yanzu Siraj take zargi, amman ina cikin kwankwanto saboda kar na yi zargi na jefa rayuwarsa cikin matsala daga karshe kuma ya zama ba shi din ne ba. Ina jin kewar da na sosai kullum mafarkinsa na ke yadda muke rayuwa da shi a cikin gidan yana ta min gizo a ido wani lokacin har ji na ke kamar yana kirana.
JIBRIL POV.
Daga gidansu Nawwara kai tsaye ya nufo gida har ya iso be daina hawaye ba, zuciyarsa kuna bata daina kuna ba, nan da nan ya fara tarin jini sai da ya saka tissue ya goge, babu wanda idanuwansa suke son gani kunnuwansa suke son jin muryarsa a yanzu irin Noor, daman tun kamin faruwar hakan jikinsa yake masa ba dadi ashe na rabuwa da dansa ba, rabuwansu na karshe ya tuno lokacin da yaje daukarsa yace Bilal zai fita da shi, rumgumar da ya yi masa ya dingajin kamar yanzu yake masa ita.
“Ina kake Noor ina kake?”
Ya tambaya yana buga sitarin motarsa yana kuka sosai kamar makaramin yaro.
“Miyasa nake ta rasa abubuwan da suke da muhimmanci a rayuwata ne? Miyasa ne? Allah karka karbi rayuwar da na a yanzu da na fi bukatarsa Allah kada ba basu damar cutar da shi Allah ka kubutar min da dana”
Kamar zai fadi haka ya fito daga motar yana kuka be damu da ma'aikatan gidan su ga kukansa ba shi dai matsalarsa da isheshi. A falo ya zauna yana ta misalta irin yadda Noor yake idan ya zo gidan, sai kuma ya dauko wayarsa ya bude gallery yana kallon hotunan Noor da kuma wanda suka yi tare.
“Wa zai min haka a duniyar nan? Mina tarewa wani? Bilal mi na maka? Oh Allah”
Ya mike tsaye yana share hawayensa, a dare kasa bachi yayi kamar dai ko wane dare yana ta aikin sallah da rokon Allah ya fito masa da dansa, kudi mai yawa ya diba ya bawa Malamin nan mai koya masa karatu akan yasa a yi masa addu'a Allah ya bayyana masa dansa.
Yana zaune yana shan ruwan tea kamar kullum domin tun da abun ya faru baya cin komai sai ruwan tea maganinsa ma ya daina sha. Sai ga Kiran Abbah ya shigo wayarsa cikin yanayin damuwa ya daga.
“Assalamu Alaikum”
“Wa'alaikassalam Jibril ka zo gida yanzu nan ina jiranka”
“Okay”
Yana kashe wayar ya mike tsaye ya shiga bedroom ya canja kayan jikinsa daga jallabiya zuwa kananan kaya, a gaggauce ya fito saboda yasan yau Abbah zai bar sokoto yasan dalilin kiransa ba zai wuce ya fada masa Maganganun hakuri ba.
Ko da ya isa Abdullah fodio road ya tararda Abbah tare da wani bako, bayan sun gaisa sai Abbah ya gabatar masa da shi.
“Ga Dsp Sani Muazu nan na fada masa komai akan case din Noor, abunda yasa na ce kasa a saki Bilal saboda a bullo masa ta wata hanyar, tun da har ya kwashe kwana uku a station da duk irin wahalar da ake bashi be fadi gaskiya ba zai taba fada ta hanyar tsiya ba, so wannan dsp ya san yadda xai bibiyi Bilal har a gano gaskiyar lamarin”
“Thank you Abbah”
Abbah ya dafashi.
“Ka kwantar da hankalinka Jibril Noor dinka yana nan lafiya kalau, kuma za a gano shi da yarda Allah duk wani bayani sai kanyi masa ni yanzu zan wuce”
Sai da Abbah ya koma ciki yayi yan mintuna sannan ya fito Jibril ya raka shi har gurin mota suka yi sallama dan baya jin xai iya binsa har airport, bayan Abbah ya wuce ne Jibril ya dawo ya cigaba da yi ma Dsp bayani akan abunda ya sani a game da Bilal sai Dsp ya nemi hoton Bilal da addirensa da komai nasa.
Suna haka wayar Jibril ta yi ringing yana dubawa ya ga Number Siraj cikin sauri ya dauko a tunaninsa ko zai sanar da shi wani abun ne, domin shi ma ya damu sosai akan batan Noor duk wani shiga da fita da ake tare da shi ake yinsa.
“Hello Siraj”
“Jibril kana ina ne?”
“Ina nan Abdullah Fodio Road lafiya?”
“Nawwara ce ta kirani a waya tana kuka tana min magiya wai na fada mata inda danta yake”
“What? Ita da kanta?”
“Yes ita ce ni abun ya bani mamaki ne”
“Kana ina ne? ”
“Ina gida”
“Bari naje na sameta”
Yana kashe wayar ya mike tsaye yana kallon Dsp
“Taso muje can inda zamu samu hotonshi”
Tare suka fito sai Dsp ya shiga motar Jibril suka nufo gidansu Nawwara. Sai da ya tsaya nesa da gidansu Bilal ya nunawa dsp gidan sannan ya karaso kofar gidansu Nawwara, kiranta ya yi ya sanar mata yana kofar gida yana son magana da ita sai ta ce ya shigo ciki.
Ko da ya shigo ya sameta tsakar gida tana aikin kuka duk ta rame ta yi baki sosai kamar ba ita ba, sai da ya gaisa da Inna sannan ya zauna saman tabarmar da Inna ta shinfida masa yana kallon Nawwara har cikin ransa yake jin kukanta.
“Ki yi hakuri Nawwara dan Allah ki daina kukan nan kina tada min da hankali”
“Jibril Siraj ne ya sace Noor”
Ta fada cikin kuka.
“What?”
Ya kalli Inna sai kuma ya maida dubansa gurin Nawwara a tunaninsa bakinciki ne yake son taba ta.
“Listen Nawwara...”
“Wallahi ba karya na ke ba, shi ya kade Noor kuma yana cikin plan dinsa kashe Noor da ni da kuma kai”
“Okay na