Showing 36001 words to 39000 words out of 138998 words

Chapter 13 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

748

buɗe ido nake sai na ji sun min nayi sosai, bana iya tuna abunda ya faru da ni balle har na gane inda nake har sai da nayi ƙarfin halin buɗe idona dake ciki da danshi domin bana iya gani da su sosai.

“Sannu”

Bana iya tantance mai muryar amman tabbas na taɓa jin wannan muryar ko a ina ne, da sannu idanuwana suka buɗe wasai har na iya tantance a asibiti na ke, yanzu kan na tuna abunda ya faru amman waya kawo ni asibiti? Kamar ance na kalli gefena sai idanuwana suka sauka kan Mustapha idonsa narai-narai kan nawa. Unƙurin tashi na yi amman babu wani kuzarin kirki a jikina.

“San..nu..”

Ya faɗa murya na rawa, kansa ƙasa-ƙasa kamar mai saunata. lallai ma wannan mutumem ya raina min da hankali miya kawo shi a inda na ke ma? Tambayar da na kasa amsawa kaina kenan, cikin ƙarfin hali na ɓalle drip ɗin da aka saka min a hannu, na sauke ƙafafuna ƙasa, hannun da na ɓalle cannula yana ta jini na ɗauki Hijabina da ke saman durowa na saka.

“Nawwara....”

Ya faɗa yana miƙewa tsaye idonsa a razane kan hannuna dake ta zubar da jini. Da hannun na nunasa ina masa wani mugun kallo.

“Kar sunana ya sake ziyartar laɓɓanka, kar kuma ka sake ƙoƙarin furta wata kalmar a gareni, ban taɓa tunanin kai hasararren ɗa bane sai yau, zakka marar tarbiya, Zahili dan gantali haihuwar hasara”

Tun da na fara wannan maganar kansa na ƙasa ya rumtse ido yana ta saurarena, mi kuma tuni na fara takawa zuwa gurin ƙofa to my surprise sai ga Jidda ta shigo rike da kaya niƙi-niƙi a hannunta.

“Har kin farka?”

Da ni take magana amman idonta yana kan Mustapha da kamar akwai wani abu a ƙasa. Ƙarasa ta yi ta aje kayan da ke hannunta ta zo ta dafani, sai na kaɓe mata hannu idanuwa cike da ƙwalla zuciyata kuma har wani fisga take kamar zata fito.

“Me kuke yi a nan”

“Suma kika yi a hanya, sai Mustapha ya ganki ana neman inda za a kaiki shine ya kwaso ki ya kawo asibiti”

Kai tsaye ta bani amsar, Mustapha kan tuni ya yi mutuwar tsaye saboda kalaman da na masa.

“Ya akayi kika sani?”

Na tambaya yayinda da hawaye suka sauko daga idona suka wanke min fuska. Sai da ta kalli Mustapha sannan ta kalleni ta ce

“Mustapha ne ya faɗa min”

Dauƙe kai na yi na cigaba da tafiyata na ƙi kula kiran da take min har na fice daga ɗakin.

‘Taya Mustapha yasan alaƙar da ake tsakanina da Jidda? Miyasa be kira wani daga cikin gidanmu ba kira Jidda?’

Shine abunda na ke ta saƙawa a raina ina tafiya, Jidda na bina da kira.

‘Amman kuma ai bata san illar da Mustapha ya yi mana ba, bata san aibunsa a garemu ba’

Tuna wannan yasa na tsaya har na saka Hijabina na danne Hannuna ina jiran ta ƙaraso.
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


2⃣2⃣

“Haba Nawwara abunda kike ba shi da kyau Wallahi na san kin tsani masu kuɗi amman wannan mutumen fa taimakonki ya yi ban san abunda bawan Allah nan ya yi miki ba duk kin bi kin tsaneshi, haka sam be dace ba, ni kaina na tuhumesa lokacin da ya zo har gida ya faɗa min na ce miyasa be faɗa ba gidanku ya ce yana gudun zargin ne kuma da na zo nan asibitin na tarar mutun biyu da suka kawo ki tare, Wallahi babu wani abu Nawwara dan Allah ki kwantar da hankalinki”

Shine abunda Jidda ta faɗa lokacin data ƙaraso kusa da ni. Mustapha kuma na daga can nesa da mu ya sako min ido kamar zai cinye ni. Kallo ɗaya na yi masa na ɗauke kai ba tare da na ce da ita komai ba na cigaba da tafiyata, zuciyarta na mugun bugawa kamar zata faɗo. Tare muka fito da Habiba a har bakin gate ɗin Specialist hospital dake sokoto, motar Mustapha ce ta sha gabanmu be ce komai ba ya miƙa hannu daga inda yake zaune ya buɗe mazaunin baya. Jidda ce ta iya riƙa ganbun motar ni kan ko kallo bata isa ban na kauce mata na cigaba da tafiyata har na tsada mai adaidaita na shige ina faɗa masa inda zai kaini, yana ƙoƙarin tashi sai ga Jidda ta dakatar da shi ta shigo tana min masifa wai abunda na ke bana kyauwa, ni dai ban kulata ba saboda na san bata san zafi da irin ƙiyayyar da raina ta Mustapha ba, tun da ban taɓa faɗa mata cewar shine mutumen da ya yi sanadiyar muturwar ƴar'uwata ba.

A gurin da aka saba saukeni na ce ya ajeni na saka hannu aljihu na ciro kuɗi a bashi sai a lokacin na tuna da hoton Habiba da na baro a wacan baƙin kamfanin da bana fatar ko a mafarki na sake zuwa, gaskiya na ji babu daɗi sosai domin shine kaɗai hoton Habiba da nake da shi a yanzu wanda take da girmanta, ta ɗaukeshi ne lokacin da zata yi canjin makaranta daga Hafsatu zuwa Nana girl's, abunka da takala ba hotone a gabanmu ba sai idan wani abun ya tashi na dole sannan muke zuwa yin hoto.

“Ina wayata?”

Na tambayi Jidda bayan mai adaidaita ɗin ya bamu canji, hannu tasa cikin jakarta ta ɗauko wayar ta miƙa min.

“Gashi”

Ina karɓa na sa kai gabana muka cigaba da tafiya tare.

“Gaskiya halinki bashi da kyau Nawwara, idan har baki yabawa Mustapha ba to ba zaki zageshi ba”

“Ce miki ya yi na zageshi?”

“Ko baki zageshi ba kin faɗa masa magana marar daɗi domin alamu sun nuna haka, ban san abunda bawan Allah ya yi miki ba, ko dai akwai wani abun ne?”

Na tsaya ina kallonta

“Wai miyasa kika damu ne Jidda?”

“Saboda ya taimakeki, da be kawo ki asibiti ba da Allah kaɗai yasan halin da zaki kasance akan hanya”

“Da barina ya yi akan hanyar mota ta takani ko kuma mutane suka ɗaukeni suka jefar a bola, da ya fi min farinciki sama da ɗauko da ya yi ya kawo asibiti, dan Allah ki tattara duk wani abu da ya danganci maganar nan ki ajeta a gefe”

Na tada kai na cigaba da tafiyata har na isa gida ban waiga na kalli Jidda dake gefena ba. Ita ce ta faɗawa Inna abunda ya faru da kuma irin abunda na yi ma Mustapha har Inna da kanta ta dinga ganin rashin kyautawa da kuma faɗar abunda na yi ba halina ba ne.
Ni dai ban iya cewa Inna komai ba tun da nasan ita ma ban faɗa mata cewar shine mutumen da ya yi ma Habiba aika-aika ba. Tufafin jikina na cire na saka a murhu na ƙone tare da Hijab ɗin duka na haɗa na ƙone saboda mutun biyu Mustapha da kuma Jibril tsakanin su ba zan iya banbance wanda zuciyata ta fi tsana ba. Ina gaban Murhu Inna ta fito daga ɗaki jin ƙauri ta saka salati.

“Lafiya kike ƙone kayan aikin kuma Nawwara mi yake damunki?”

“Inna sun koreni dan haka bana da buƙatar wannan kayan”

“Garin ya wani abun kika yi?”

“Ban yi komai ba, saboda kawai na daɗe ban je ba”

“Ba kince Bilal ya faɗa musu baki da lafiya ba?”

“Wai basu yarda ba shugaban Kamfanin ne bashi da mutunci”

“Allah ya kyauta ya baki wani”

Ta faɗa cikin muryar da ke nuna bata jidaɗin haka ba. Ƙarasowa ta yi kusa da ni ta riƙani ta tayar tsaye.

“Tashi gaban hayaƙi, bari na saka miki ruwa ki yi wanka”

“A'a zan iya Inna”

“Babu ƙarfi jikinki Nawwara baki ga yanxu kika dawo daga asibiti ba”

Da kanta ta haɗa min ruwan na shiga banɗaki na yi wanka, bayan na fito na ɗauki buta na yi alwala na shiga ɗakinmu sai na samu Inna zaune tana yanka min albasa a wake da shinkafa, saboda ta san ina son na saka albasa da tumatur idan zan ci wake.

“Gashi nan idan kin gama sallah sai ki ci, bari na kawo miki ruwa”

Ta miƙe tsaye ta nufi ƙofar fita ni kuma sai na yi saurin dakatar da ita.

“Haba Inna kina ta min abu sai kace ƙaramar yarinya ni ya kamata ace ina hidima dake ba wai ke ki yi da ni ba”

Tsayawa tayi jikin ƙofa tana murmushi tare da wasa da wuƙa da kuma ragowar albasar dake hannunta ta ce.

“Nawwara ji nake kamar da nayi wani sakaci kaɗan rasaki zanyi, ɗazun da baki dawo a lokacin da kika saba dawowa ba hankalina ya tashi sosai, ba san yadda zanyi ba idan har na rasaki bayan na rasa Habiba, kuma kina a matsayin RAI BIYU a yanzu ni da kuma ɗanki, shi ma ya damu da be ganki ba lokacin da ya dawo daga makaranta, yana ta tambayar ina Momy nace mishi kina gurin aiki amman daker ya yarda ya tafi islamiya, ɗanki yasan zafin rabuwa da mutun yasan idan aka tafi ba a dawowa shiyasa saboda ya rabu da Habiba dan haka ba zamu iya jure rashinki ba”

Tana faɗar hakan tasa kai ta fice idonta cike da ƙwalla, ni kuma na jingina na lumshe ido ina sauke ajiyar zuciya, wani irin tausayinta ne ya rufe ni. Jin wayata tayi ƙara yasa na buɗe ido na nufi inda wayar take, tun kamin na ɗauka gabana na faɗi saboda saƙone daga One-On-One Limitless Company, ji nayi bana da buƙatar sanin abunda saƙon ya ƙumsa, dan haka na danna delete na goge shi ba tare da na karanta ba.

Sai da na gama rama sallah azahar sannan na gabatar da sallah la'asar, sai na zauna na ci abincin sai ba sosai ba saboda bana jindaɗin abinci a yanzu, sai dai shigowar Inna yasa na zage dantse na yi ta auna abinci domin nasan zata damu idan ta ga banci da yawa ba. Na yi ƙoƙarin ganin na danne damuwata amman mahaifiya ta fi gaban wasa ita da kanta ta tsinkayi hakan a cikin idona.

“Nawwara kamar akwai abunda yake damunki, idan dai dan maganar aikin nan ne ki kwantar da hankalinki Allah zai sake baki wani kamar yadda ya baki wannan”

Kai kawai na iya ɗaga mata domin na gansu maganar aikince kamar yadda take hasashe, domin idan har ta tiƙe ni ban san mi zan faɗa mata ba. Tashi tayi ta fita jin wata maƙociyarmu ta shigo, ni kuma na rafka uban tagumi ina kallon ƙasa amman hankalina yana can gurin rayuwata ta baya.

FLASH BACK.
_“Yau za'ayi ina fatar zaka samu zuwa kai da madam, tau ya yi sai kun ƙaraso”_

_Haka na ji ya faɗa a waya, sannan na miƙe tsaye yana min wani gumun kallo ya ce._

_“Wallahi duk kika sake abokaina suka zo gidan nan kuma kika fito sai na halakaki, kinji ni ko?”_

_Da sauri na ɗaga masa kai hawaye na zuba a idona, sai ya kaɗa kai fuska babu annuri ya nufi ɗakinsa yana wani irin jinkansa, ni kuma na zube a gurin ina kuka saboda zafin ruwan zafin da ya watsa min a hannu kuma ya hanani kuka saboda tsabar zalumci. Ina a gurin ina aikin kuka har ya shirya ya fito sai ƙamshin turare yake ya tsaya a kaina ya nuna ni da yatsa_

_“Ki shiga cikin ɗaki ki kulli kanki karki yarda ki fito”_

_Na amsa masa da tau jikina na rawa ina ta ƙoƙarin haɗe kukana nasan idan har na yi kuka a gabansa zai iya dukana, kamar yadda ya umarce ni haka na shiga cikin ɗakin na rufe kaina wanda hakan ya bani damar tausayawa kaina da kaina. Can zuwa dare na soma jin hayaniyar abokansa ta hirar da suke na iya gane ashe muƙamine ya samu amman ya gagara faɗa min saboda ƙiyayyar da yake min, haka yake duk lokacin da wani abun ya sameshi sai dai na ji a waje ba dai ya faɗa min ba. Har suka yi abunda zasu yi suka gama ban fito ba, bayan fitarsu da minti ashiri na ji an buga ƙofar ɗakina, yanayin yadda aka banki ƙofar ne ya fahimtar da ni cewar Jibril ne yake buga ƙofar, cikin hanzari naje na buɗe saboda na san baya son jira, sai nayi arba da yatsunsa biyar a kuncina, ma'ana wanke min fuska da mari yana faɗin_

_“Ke kiƙa faɗawa Abbah zanje meeting ba dake ba ko?”_

_Baya-baya na yi ina girgiza masa kai_

_“Na rantse da Allah ban faɗa ba, Wallahu ba ni bace”_

_Na faɗa cikin kuka, sai ya watsa min harara, yace na canja tufafi muje amman duk na masa kuka cikin mutane sai ya ɓanlani, jin wannan yasa hawayena ya yanke tun kamin ma mu fita domin na san haƙinsa ne sarai zai iya ci min mutunci a gaban kowa, sai dai ban daina jin zafin marinba har muka isa gurin da ake tare, gurine dake cike da manyan mutane an ƙawata gurin anyi masa kwalliya gwanin sha'awa. kowa da mazauninsa, an kasa mutane daban-daban wasu na tare da matansu wasu kuma na tare da familysu. Tare muka shigo da shi amman muna shiga harabar gurin sai yayi kamar be sannin ba tare da gargaɗina akan karna yarda na nuna cewar ni matarsa ce. Guri na samu kusa da wasu baƙin na zauna, bayan an gama jawabin da akeyi aka kirashi aka karramashi, sai yaje ya karɓi Award ya yi jawabi godiya, a lokacin Abbah da Hajiya basa nan dan haka babu wacce zai kira bayan su sai ni da nake matarsa, amman abun mamaki sai ya kira sunan budurwarsa Asiya ko kuma ma nace karuwarsa, haka ta miƙe tsaye tana ta karairaya ta haura gurin tana taya shi murna. Ni kuma ina daga nan zaune ina hawaye_

_Wani mutun ne ya miƙo min tissue yana min kalaman da mijina abokin rayuwata be taɓa min ba_

_“Kuka be cancanci kyakkyawar fuskarnan taki ba dan Allah karɓi ki share hawayenki”_

_Kallonsa na yi amman na kasa karɓa saboda idon Jibril na kaina, haka mutumen ya matsa min amman naƙi kula shi har aka tashi taron, a gurin da zamu shiga mota ya tare mutumen ya riƙa bugar masa baki wai ya yi magana da matarsa, babu kalar baƙar maganar da saurayin be faɗa masa ba, sannan aka rabasu ni kuma ya sakoni gaba muka dawo gida, kamar jira yake mu iso ya sakani gaba da duka wai na kula wani namijin har wani huci yake kamar zaki..._

BACK TO STORY

Shigowar Noor ne ya katse min tunani, sai ya yi saurin aje allon dake hannunsa ya nufo yana share min hawayen da ban san sun zubo ba.

“Momy miyasa kike kuka? Shiru shiru shiru kinji Allah ya miki albakar, yi shiru shiru faɗa min waya taɓa ki?”

Shine abunda yake faɗa tare da saka haɓar rigarsa ya goge min fuska, ina kallonsa gabana ya faɗi fuskar Jibril ce shimfiɗe a fuskarsa babu inda ya ragoshi tun daga kan hancinsa har ido da baki da fari komai na ubansa ne, rumgumeshi nayi muka kwanta saman kafitar da nake zaune.

_“Ba cikina ba ne...!”_

Shine abunda ya faɗo min a rai, sai na ƙara ƙanƙame Noor kamar ance za a rabani da shi. Bachine ya kwashemu ni da shi bamu farka ba sai da Sakina ta shigo tana tashina wai anyi magariba.
Bayan Sallah isha'i Bilal ya kirani a waya yace min yana ƙofar gida, nasan daman zaizo tun da yau ban karɓi kuɗin da ya saba bani ba. Sai dai na sha mamaki lokacin da fita muna fira da shi.

“Miyasa kika fita Kamfani ɗazu kina kuka?”

Shine abunda ya fara tambayata, nasan wata ƙila wani ne ya faɗa masa, ni kuma sai na masa ƙarya da cewar saboda sun ƙoreni yasa ni kuka, ya nuna min damuwarsa sosai har ma ya yi alƙawarin zai yi wani abu wajen ganin an maidani aikin, amman na nuna masa bana so. Sai tara da rabi muka rabu ban faɗa masa cewar na suma a titi ba duk na san nan gaba kaɗan zan ji a gurin Jidda domin bata ɓoye masa komai da ya dangance ni.

Ko da na shiga gida wayata na ta ringing ko da na duba sai naga baƙuwar number, kamar kar na dauka sai kuma na ɗauka tare da sallama, sai na ji ba a amsa min ba kuma ba a ce komai ba har na tsawon lokaci, hakan yasa na sake sallamar nan ma shiru har sai da na duba wayar naga mai kiran be kashe ba, na sake karawa nayi sallama a karo na uku ba amsa min ba kuma ba a ce komai ba, hakan yasa na kashe wayar dan da alama mai kiran yana son sauraren muryarta ne kawai duk da ban san ko wanene ba.

WASHE GARI...

Misalin bakwai da rabi saƙon kamfanin ya sake shigowa, nan ma ban karanta ba na goge, na shigaba da haɗa abun karinmu da nakeyi. Sallamar baƙuwar murya yasa na ɗago daga gaban murhun da nake na amsa mata ina mata kallon rashin sanin, sai da ta gaisheni sannan ta matso kusa da ni ta aje min leda biyu dake hannunta ta ce

“Wai gashi inji Ya Mustapha ya ce abawa Nawwara, kuma wai yana mata sannu da jiki”

Har na buɗe baki zance mata ta ɗauki kayan ta koma da su sai ga Inna ta fito daga ɗaki tana amsawa kamar tasan ni ba zan amsa ɗin ba.

“Mashallah ki ce an gode Allah ya saka da alheri, jiki kuma ya yi sauƙi sosai”

Da wannan budurwar ta juya ta koma wacce nake san ran riƙonta ake a gidansu Mustapha domin iyayensa shi kaɗai suka haifa. Tana fita na ɗauki kayan na fice na bar Inna tsaye tana kallon ikon Allah domin nasan idan har na ce yarinyar ta ɗauki kayan ta koma dasu a gabanta ba zata bari ba, amman yanzu bata san mi zanyi ba dole ta saka min ido.

Ina fita na yi karo da shi a ƙofar gidanmu sai ya ɗanyi nisa da gidanmu kaɗan yana sanye da jallabiya, daga inda nake tsaye na jefa masa ledodin na juyo abuna.
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


2⃣3⃣

“Me kika yi kenan?”

Ina shigowa gida ta jefo min wannan tambayar, da fari na tsaya tunanin abunda zan ce mata sai kuma daga baya na yanke shawarar faɗa mata gaskiya.

“Mayar masa da abunsa na yi, bamu da buƙatar taimakoshi”

“Amman Nawwara ban taɓa sanin baki da hankali ba sai yau, mutumen da ya tsinceki gefen titi ya taimaka miki ya kaiki asibiti garin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login