Showing 42001 words to 45000 words out of 138998 words

Chapter 15 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

750

babu labarinsa, ga kuma Jibril da ya sakoni a gaba yanzu.
Wai shi Jibril me yake nufi ne ya yi nadama ko kuma so yake na koma aiki ƙarƙashinsa ta yadda zai sake gallazamin ya ɗauka kamar da ne?

“Kut”

A fili na yi ƙwafa, kana na ɗaga kaina dake ƙasa na kalli Inna wacce ta fito daga ɗaki tana maganar aikina.

“Ni fa wannan lamarin har tsoro yake bani Nawwara, ban taɓa ganin wanda aka matsawa ya koma aiki kamar ki ba, anya babu wani abu?”

Na yi dariyar da ni ƙaɗai nasan abunda yake nan.

“Babu komai Wallahi kawai dai kin san abu idan aka ce maka da turawa ne, shiyasa”

“Amman ke miyasa kika tsaya kai da fata akan ba zaki koma ba, nifa ina jin da kamar akwai wani abu”

“Babu komai kawai ina musu jan ajine saboda susan ba ko wanne mai neman aiki ba ne wulaƙantacce, zan koma aiki Inna ai dole ma ne na koma aikin ko dan na bawa marar ɗa kunya! Kuma ni kaina ina da buƙatar aikin saboda zai taimaka mana mi tallafawa kan mu da kan mu”

Na faɗa ina sauke ajiyar zuciya Inna kuma tana amsa sallamar Malam Haruna mai gidan da muke haya...!
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


2⃣5⃣

Bayan Inna ta amsa sallamar ta je ta ɗauko hijbinta ta saka sannan ta ƙarasa ƙofar gida suka gaisa da shi. Sama-sama na ke jiyo firar da suke har Inna na faɗin Innalillahi, kamar na unƙura na tashi sai kuma wata zuciyar ta ce na zauna tunda maganar manya ce ake ko ma minene idan ta zo ai zanji, sai dai jikina na ta raya min ba abun daɗi ba ne.

  Sun ɗan ɗauki lokaci suna maganar daga bisani na ji muryar Inna tana roƙon a tausaya mana shi kuma yana faɗin babu yadda zaiyi. Bayan sun gama maganar Inna ta dawo cikin gida jikinta a sanyaye fuskarta kuma na nuna alamun damuwa.

“Lafiya Inna miya faru?”

Zama ta yi kusa da ni tana nuna min kuɗin dake hannunta.

“Wai an sai da gidan ya kawo mana ragowar kuɗin hayarmu na wata takwas kuma wai sati ɗaya wanda ya siye gidan ya bamu”

Kamar daga sama aka jefo maganar haka na jita cikin kunena, zuciyata ta hau bugawa da hauri na zaro ido hannuna a ƙirji na ce

“Sati ɗaya kuma? Waya siye gidan ne?”

“Oho”

Ta faɗa idonta cike da ƙwalla, furucin da na yi na ɗazun ne ya fito da Sakina, Jamila da kuma Noor da gudu suka nufo inda muke zauna suna ta rabon idon da son jin abunda muke tattaunawa.

“Inna miya faru?”

“Tashi zamu yi Sakina an saida gidan”

Inna ta amsata cikin wani irin kalar murya marar daɗi.

“Tau ina zamu koma, waya siye gidan hala?”

Jamila ta tambayi Inna.

“Allah masani”

Dukansu ɓata fuska suka yi da alama suma maganar tashin be musu daɗi ba domin sun saba da unguwar anan haifesu ga ƙawaye da ƴan'uwa kusa da su taya zasu jidaɗin tashin? Idan muka tashi ina zamu koma ? Babban gida ko ina?

“Haya yanzu tsada take ina ma zamuje a bamu ɗaki ban sani ba, babban gida ma idan muka ce zamu zauna babu guri tun da duk sun kame ɗakunan waya ma zai bamu haya da dubu ashirin datara da suka rage mana na ragowar kwanakinmu kai Innalillahi wannan rayuwa daga wannan sai wannan”

Cewar Inna hawaye na zuba a idonta, ni kuma na kalleta na ce

“Ko dai karin kuɗin hayar yake so?”

“Na tambayeshi yace aa shi ai ya riga ya siyar da gidan”

Na yi shiru inata nazari wannan wane irin saida gidana ne ba a shigo ciki anga yadda gudan yake ba kawai sai muji labarin an siye shi kuma wai sati ɗaya mu tashi? Lallai wannan daga gani shiri ne, kuma ba zai wuce Mustapha ba shine kawai na ke zargi.

“Inna ki kwantar da hankalinki zan koma aiki idan aka biyani kuɗin aikin sai mu haɗa da wannan mu kama wani gidan haya, zan roƙeshi ya yi mana haƙuri har ƙarshen wata zamu tashi mu bar masa gidansa”

Na faɗa ina kallon Inna sai Sakina ta ce

“Ko kuma a faɗawa Ya Bilal”

Na katsa mata tsawa.

“Ke wane irin Bilal kuma Wallahi duk wacce taje cikinku ta faɗa masa sai na ɓata mata rai, haka kawai sai mu ɗauki lalurar duniya mu aza masa, shi ma ai yana da tashi lalurar”

Haka muka wuni gidan shiru-shiru kamar wanɗanda aka yi ma mutuwa duk jikinmu ya yi sanyi, tsoron kwana da muke ji a gidan sai ma ya cire mana saboda hankalinmu ya karkata kan wannan matsalar.
Bayan sallah magariba Inna tace naje Babba gida na faɗa musu halin da ake ciki, ba musu na tashi na ɗauki Hijabin da na cire wanda na yi sallah da shi na saka na kama hannun Jamila muka nufi ƙofar fita.
Abun mamaki muna fitowa muka dami Mustapha a tsaye kamar daman can mu yake jira, kallon kallo muka riƙayi da shi, idonsa narau-narau fuskarsa abun tausayi kamar mai shirin yin kuka, ni ko babu komai a idona sai wuta mai tsananin ci a lokacin da ta ga maƙiyinta.

“Guri....guri...gurin.. inna na..zo Daddy ne ya aiko...ni-”

Haka maganar ta riƙa taƙe mishi kamar marar gaskiya, ni kuma abun sai ya bani mamaki kuma ya sakani murmushin takaici.

“Like seriously? Wai Mustapha ko baka san gidansu Habiba ba ne? Baka san ni yayarta ba ce?”

Sai ya amsa min da sauri.

“Na sani! Zan iya rantsewa da Allah ni ban taɓa kula kina cikin unguwar nan ba sai da kika mareni, daga lokacin da kika mareni sai na sa aka min bincike kanki a maimakon na tsargu sai na samu kaina da tausayin halin rayuwar da kuke ciki kuma na yi nadamar abunda na yi ma Habiba kasancewarta ƙanwarki, a lokacin da ta sameni ta bani haƙuri akan karna cutar da ke ina ta shirya abunda zan miki na rama abunda kika min amman sai zuciyata ta hanani saboda tausayinki da take, kin fini kwarjini da ƙima Nawwara kuma ke jaruma ce na gano haka ne daga lokacin da kika ɗaga hannunki kika mareni bayan kuma ba dake nake faɗan ba siya kika yi, wannan ya karantar da ni wani abu a rayuwata lalle ni a idon wasu ba kowa bane tun har mace kamarki zata iya ɗaga hannu ta mareni a bainar jama'a, bayan ko ƴaƴan masu kuɗi basu taɓa unƙurin nuna min ko da yatsa ba balle kuma harara.
Na rasa natsuwata daga lokacin da labarin mutuwar ƴar'uwarki ya same ni, mutuwar Habiba ta canja ni Nawwara, ta tunatar da ni abubuwa da dama da na manta i understand the distance between right and wrong, ta kuma ta sanar da ni abubuwan da ban sani ba a rayuwar duniya, if i begin to tell you how terrible i feel for what I did to your family Nawwara you will find a place in your heart to forgive me, da ace kun sanar da ni tana da ciki da na karɓi cikin kuma na ɗauki nauyin komai na ta, but it too late labarin mutuwarta kawai ya sameni ba a faɗa min dalilin mutuwarta ba amman ni na san cikine saboda ance ta yi zubar jini, Nawwara i'm looking forward to corrected all my mistakes, i made a mistake because I am only human dan Allah Nawwara ki yafe min”

Ta yanayin muryarsa nake fahimtar hawayene suke zuba a idonsa, domin duhu ya sauko bana iya ganin fuskarsa da kyau, sai dai na fahimci hawaye yake kamar yadda nima nake tunawa da ƴar'uwata.

“It's too early to ask my forgiveness Mustapha, i know you are here to play a game with me too”

“No don't get me wrong, i know it too early i'm sorry i shouldn't talk about this, ga wannan ko zaku buƙaci yin wani abu da shi”

Jamila na ganin damin kuɗin da ya miƙo min ta juya da gudu ta koma cikin gida. Ni kuma na yi murmushi ina share hawayena.

“Baka ba kanka dariya ba? Tsayawa kana magana da ni be isa yasa ka ji kunyar kanka ba? What kind of stupid are you Mustapha? What make you think zamu karɓi wani taimako daga gareka? Wannan ne yasa ka turo aka kwashe mana komai kuma ka siye gidan da muke ciki just to humiliate us? Or to force us accept your apology? What kind of person are you?”

Na faɗa cikin kuka, har ya buɗe baki ya yi magana sai kuma ya yi shiru kamar mai nazari, isowar Inna ce tasa ni saurin share hawayena.

“Lafiya Nawwara?”

“Lafiya ƙalau daman Zakkace aka fitar shine Daddy ya ce a kawo muku”

Shine ya amsata yana miƙa mata kuɗin, ni kuma na yi karaf na ce.

“Karki karɓi kuɗin nan Inna, kuɗin maƙiyinki ne, shine mutumen da ya yi ma Habiba fyaɗe ya yi sanadiyar rabaki da farincikinki kuma shi ya turo mana ƴan fashin nan ya siye gidan da muke ciki saboda kawai mu karɓi taimakonsa...”

Mutuwar tsaye Inna tayi na ɗan wasu mintuna sannan taja hannun Jamila da Sakina ta mayar da su cikin gida ni kuma ta ce da ni.

“Nawwara shiga gida”

Ba musu na juya na shige cikin gida sai ta maida ƙofar ta rufe, duk muka yi ɗaki har ita, na yi tsammanin zan ga hawaye ko makamancin haka a idon Inna amman ban ga komai ba muryarta ce kawai take iya karantar da ni damuwarta.

“Daman na yi zaton shine ya aiko da ƴan fashin nan, kuma na san babu wanda zai saye wannan gidan sai shi, amman ban taɓa tsamanin shine ya lalata min rayuwara ƴa ba...”

Ta faɗa tana sauke ajiyar zuciyata, daga ni har ita bamu kwana cikin daɗi ba a wannan daren gashi zuciyata na ta saƙa min zuwa gurin aikin ko kuma na haƙura.



*** *** ***

JIBRIL POV.

Jingine yake jikin kujerar dinning hannunsa saman kofin tea yana ta zagaye bakin kofin ya gagara sha, babu abunda yake tunani sai rayuwarsu ta baya da Nawwara.

Yana jin lokacin da take waya da Inna Inna na faɗa mata zata so har Abuja ganinta ita kuma tana ta ɗauki da murna, amman sai ya haya ya nuna mata sam baya son sanin family ta.

“Kina jindaɗi kin auri mai kuɗi ko? So that ki kawo min su a gida ko? Ni ke na aura ba iyayenki ba dan haka bana buƙatar ganin kowa a gidana”

Matsowa ta yi kusa da shi kamar zatayi kuka.

“Jibril ya kamata ka san iyayena suma kuma su sanka, ko lokacin da za ayi aurenmu ƙin zuwa ka yi ka gaishesu, bayan kuma an yi auren sau ɗaya suka taɓa ganinka ba zasu tantance ka ba...”

Tsawa ya katsa mata ya shaƙe wuyanta.

“Na faɗa miki bana buƙatar ganin kowa anan, ba iyayenki ba har abokanki bana da buƙatar ganinn kowa karki kuskura kawo min kowa a nan, annoba kawai...”

Tuna wannan yasa shi sauke wani dogon numfashi har yana buɗe baki.

“Taya zan tunkaresu yanzu? Ya Allah help me”

Ya faɗa yana kallon Siraj da ya shigo yanzu riƙe da file a hannunsa.

“An gama komai mum nika masa kuɗin gidansa ya sayar mana ya bamu takardu mun bashi kuɗi kuma mun faɗa masa sati ɗaya muka ba ƴan hayan”

“What...?”

Ya ture kofin tea ɗin ya miƙe tsaye.

“Sati ɗaya ya yi nisa Siraj a basu kwana biyu ko uku, miyasa baka da tausayi ne baka san halin da nake ciki ba i can't live without her”

Siraj ya matso kusa da shi ya dafa kafaɗarsa.

“Cool down my friend, Nawwararka ta dawo aiki yau da safen nan”

Jibril ya juya baya yana lumshe ido tare da jan sauran cocaine ɗin dake hancinsa.

“Joke apart Siraj”

“i'm not joking, yanzu aka kirani wacce ake aikawa saƙon ta dawo aiki ta dawo amman bata da uniform na ce a bata sabo”

“Oh my God”

Ya furta ya nufi bedroom ɗinsa da sauri yana cire vest ɗin dake jikinsa. Siraj kuma ya bishi da kallo yana taɓe baki.



*** *** ***

MUSTAPHA POV.

Yafi ƙarfin waya ɗaya a tsaye ƙofar gidan bayan Inna ta rufe gidan, sannan ya kama hanyar gidansu yana tafiya da ƙafa kamar yadda ya zo zuciyarsa cike da mamaki, daman sai yanzu Nawwara take faɗawa Inna kenan Habiba Nawwara kawai ta faɗawa bata faɗawa Inna ba.
Ko da ya isa gida jikinsa a mace ko part ɗin mahaifiyarsa be leƙa ba ya yi shigarwasa part ɗinsa, sallah isha'i a cikin ɗakin ya yi ta. Tunani Nawwara ne ya tsaya masa a rai har garin Allah ya waye be bachi be ko zo kusa da idonsa ba balle ya ɗauke shi, be taɓa samun kansa cikin irin wannan halin ba sai a yanzu.

Kamar sallah isha'i itama sallah asuba a cikin ɗakinsa ya yi ta, yana ta roƙon Allah ya yi masa sauƙin abunda yake ji a zuciyarsa. Misalin sha ɗaya da rabi mahaifiyarsa ta shigo ɗakin sai ya yi saurin juyawa kamar mai bachi. A aladar shi tara na safe yake fitowa su yi breakfast goma ya shirya ya wuce gurin aiki amman yau ga shi har shaɗaya na safe bata ji ɗuriyar ɗanta ba dole ne ta duba tun da taga motarsa ta tabbatar da yana gida.

“Son...”

Ta kira sunansa a hankali tana zama saman gadon kusa da shi. Juyowa ya yi ya kalleta ba tare da ya amsa ba. Jan da idonsa suka yi suka kumbura ya tashi hankalinta sosai, da sauri ta kai hannu ta taɓa kansa.

“Baka da lafiya ne your temperature is so high, miyasa same ka, bari na kira likita”

Tana miƙewa tsaye sai ya riƙa hannunta.

“Please tell me Mom ya zakiji idan kika rasa ni?”

“What...?”

Ta dawo ta zauna tana masa wani razanannen kallo, shi kuma ya tashi zaune yana kiran amsarta.

“Zan haukace Son, ƙara dai ni na mutu kai ka rayu, kai kaɗai gareni fa bani da kowa sai kai i can't afford to lose you, don't talk about this please, you have no idea how mother could feel if she lose her own child, her happiness, kai kaɗai gareni Son ka daina kawo zancen mutuwa a yanzu”

Razani, tsoro da fargabar da ya ganin a fuskar mahaifiyarsa ta karantar da shi halin da mahaifiyar Habiba take ciki.

“Ba zasu taɓa yafe min ba losing a father, mother, child is unforgettable pain ba zasu taba yafe min ba”

Ya furta idonsa na kallon window ɗakinsa. Sai mahaifiyarsa ta kama hannayensa.

“Su wa?”

“Ƴan'uwan Habiba”

“Wace Habiba?”

“The woman i raped”

“When... How”

“Yarinyar da tazo gurinki neman kuɗi kika hanata, ni na yi mata fyaɗe na bata kuɗi and now she's dead”

Hankalinta ya ƙara tashi.

“Fyaɗen da kayi mata ne silar mutuwarta? Taya?”

“Ciki tayi iyayenta suka je zubar da cikin garin zubar da cikin ta rasu”

Ta yi saurin riƙa fuskarsa dan bata son tashin hankalin ɗanta ko kaɗan.

“That's the point Son ba kaine silar mutuwarta ba karka matsawa kanka, su sukaje zubar da cikin ƴarsu suka kasheta”

“Amman ni ne silar cikin”

Shiru ta yi tana ta tunani babu yadda ba tayi ba akan ya daina neman mata amman yaƙi ita kanta abun yana damunta amman gudun ɓachin ransa yasa take ɗaga masa ƙafa ga kuma ubansa da ya tsaya masa kai da fata akan yadda duk yadda yake so a gari ga taka wanda duk ya yi masa ba dai-dai ba.
Ajiyar zuciya ta sauke ta ɗora hannayenta saman kafaɗarsa ta ce

“Son kai ne Sila amman idan ka roƙi Allah zai yafe maka, kuma hukunci za a masa sai dai ayi maka mukuncin wanda ya yi zina su kuma iyayenta ayi musu na kisan kai, zan toƙa maka Allah ya yafe maka kuma kaima ka roƙa Allah ya yafe maka”

“Amman Mom su iyayenta ba zasu yafe ba, musamman yayarta Nawwara”

“Idan Allah ya yafe maka ko da su basu yafe maka ba babu komai, kawai ka natsu na daina wannan halayyar”

“Na daina Wallahi Mom, amman idan Nawwara bata yafe min ba i will never ever being in peace and happiness, because i love her...”

Kamar wacce akayi ma shocking haka ta ɗauke hannayenta daga kafaɗar Mustapha tana kallonsa baki sake.


#RAI BIYU #RB

#TEAM MUSTAPHA
#TEAM BILAL
#TEAM JIBRIL

Bari mu ga TEAM ɗin wa suka fi yawa....? 😁

CANDY ce 👌
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


2⃣6⃣

Bayan su Sakina da Jamila sun wuce makaranta ni kuma na shiga gyaran gida, ina tsaka da wanke-wanke wayata ta ringing kamar ba zan ɗaga ba saboda bana son tashin idan ina aiki har sai na kammala, sai kuma na cire kuiya na miƙe tsaye na nufi saman window inda wayar take na ɗauka, Bilal ne ke kira da gangan na tsaya masa yanga har sai da ta kusa tsinkewa sannan na ɗaga cikin muryata mai nuna tsatsan babu ruwana.

“Assalamu Alaikum”

“Nawancy i'm glad muryarki na fara ji yau da safen nan”

“Baka je aiki ba?”

“Yanzu zan wuce ɗan leƙo waje na ganki”

“Bilal duk na yi datti aiki nake yi”


“Ai nafi son ganinki da dattin kin fi kyau, leƙo mana ke kaɗai nake jira”

Babu yadda na iya dole na amsa masa da tau na ɗauki Hijabi na saka na leƙa waje da fuskata a she yana nan daf da ƙofar gidan jikingine yana jiran fitowata.
Murmushi na sakar masa ina kallon yadda suit ɗin jikinsa ya karɓesa ya fito da kyausa chocolate skin ɗinsa sai shining take kamar wani sabon ango. Shi ma murmushin yake min yana nuna min wani bafulatani dake tsaye da jarkokin ruwa a wheelbarrow.

“Ragowar ruwan da aka zuba mana a cikin gidane Mama ta ce a kawo muku”

“Na gode sosai Allah ya saka da alheri”

“Amin”

Ya faɗa ni kuma na juya da nufin komawa cikin gidan domin nunawa mai amalanken inda zai zuba ruwan, sai kawai na ji Bilal ya kirani.

“Nawancy”

Ina juyowa sai kawai ya kanne min ido ɗaya sannan ya kama gabansa yana tafiya kamar ba shi ba.
Nikan dariya ma abun ya bani wani lokacin Bilal yana min abu kamar wani ƙaramin yaro, hakan kuma ba ƙaramin ƙara min son kasancewa da shi nake ba. Komai na cikin gidanmu sai da aka ciki har muka bada sauran jarka biyu maƙota kasancewar ruwan ya yi mana yawa, hakan ne ya tabbatar min da cewar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login