Showing 102001 words to 105000 words out of 138998 words
kokarin defending dina, wata muguwar harara Hajiyar Mustapha ta watsa masa. Sai mahaifin Bilal ya katsa masa tsawa.
“Bilal wuce muje”
Sai da ya kalleni kamar ba zai iya bari a gurin ba, sai kuma ya juya ya fice tare da mahaifinsa, ni kuma na unkura na tashi ina nuna na fito daga gurin na nufi sashen da Noor yake.
Ko da na tura kofar na shiga Noor yana bachi hankalinsa kwance, kusa da shi na zauna hawaye na zuba a idanuwana, na kai hannu na shafa shi. Ina haka sai Jibril ya turo kofar dakin ya shigo yana sanye da labcoat, bayan ya maida kofar ya rufe ya zuba hannayensa cikin aljihu ya doso inda nake.
“Na sallami yan sandan”
Ban dago na kalleshi ba balle kuma har na amsa masa.
“I'm sorry Nawwara”
“Na tsane ka Jibril”
“Na sani”
Ya amsa min a takaice.
“Ka sake dawowa saboda ka ruguza sauran farincikin da ya rage min ko?”
“Wallahi ba dan haka na dawo rayuwarki ba, Nawwara ba ki cancanci auren kowa ba sai ni ko dan Noor, yanzu kin fi son ki barwa wata uwar ta yi miki rainon da? Dan kin san ba zan taba bari kije min da shi gidan duk wanda kika aura ba ko?”
“Kowa kallon mahaukaciya yake min, ka kunyata ni a gaban mahaifin Bilal”
“Bani da wani zabin ne Nawwara, Wallahi ina son ki sosai, saboda ke nake ta canja rayuwata Nawwara, dis week wani Malami zai fara zuwa yana karantar da ni saboda kawai na samu xama cikakkane namiji da kike so, amman hankalin ya koma kan Bilal, kin kasa fahimtata Nawwara”
Na daga kai na kalleshi.
“Bana son ka Jibril miyasa ka kasa fahimta? Hakika Noor be yi dacen uba”
“Babu wanda zuciyarki take so sai ni Nawwara, Nawwara idan kika aure wani ba ni ba, rayuwata da ta Noor tana cikin hadari”
“Bari idan na auri Bilal din, ku fadi ku mutu”
Ina fadar hakan na mike tsaye na share hawayena na fice daga dakin zuciyata na mugun kuna.
Ko da na iso gida numfashina har sama yake kamar zan hadiye zuciya na mutu saboda bacin rai, tun daga yanayin sallama ta ya kwantarda Inna irin damuwar da na taho da ita ga wani uban ja da idanuwa suka yi sun kumbura sosai saboda kukan da nayi. Muryata a dakishe na zauna saman tabarmar da Inna take zaune na fara rusa kuka, sai hankalin Inna ya tashi.
“Lafiya miya same ki?”
“Jibril ne”
“Yi hakuri tsagaita kukan sai ki min bayani, amman kamin nan kina da bakuwa”
“Wacece?”
Na tambaya cikin kuka.
“Muma ba mu santa ba, amman tun dazu take jiranki”
Na share hawayena na mike tsaye na nufi dakin Inna domin ganin wacece, abun mamaki sai na samu Aisha zaune tana kallon kofa da alama ta ji shigowata kuma ta ji lokacin da na doso dakin.
_____________________________
Assalamu alaikum fans i will be offline for awhile saboda fever na damuna sosai, jiya ma daker na yi typing yau ma karfin hali kawai na yi Wallahi dan kar na barku kuna ta jira, zan je ganin doctor gobe so yanzu kan sai na samu sauki sosai sannan zan sake yin typing. Thanks All
Best regards ♥️🖤
[11/8, 9:37 PM] +234 703 352 5246: *RAI BIYU...♥🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
4⃣9⃣
JIBRIL POV.
Bayan fitar Nawwara ya zauna kusa da gudan jininsa yana ta kallonsa, shi kansa yana jin rashin kyauta a abunda ya yi ma Nawwara sai dai ya yi hakan dan ya bata ta a gurin iyayen Bilal, kuma ya banbance wanda ta fi so tsakamin Bilal da Mustapha.
Hannunsa yasa aljihu ya dauko wayarsa ya kira wata nurse ta kawo masa wani file tare da sai ya cire wata kadarda ya rubuta ma Noor takardar sallama, sannan ya dauki dansa ya saba a kafada hakan yasa Noor farkawa sai ya soma jijjigashi kamar jariri.
“Shiiiiii cigaba da bachinka Daddynka ne”
Hakan yasa Noor tafewa a kafadar Jibril ya fito tare da shi harabar asibitin ya sakashi gaban mota sannan na zagayo ya shiga driver seat ya tashi motar sai kuma ya daga wayarsa ya kira wata number
“Ki shiga dakin da aka sallami Noor ki kwashe komai zan aiko da dareba ya dauka”
Yana fadar haka ya kashe wayar, ya tashi motar ya hau titi dake cikin asibitin kamin ya sadu da babban titi marafa dan baba da ke cikin birnin sokoto.
Duk bayan seconds ya kan kalli gefen da dansa yake sai idanuwansa su cika da kwalla, hamdalla yake yi ma Allah akan yau yana da gudan jinin wannan dalilin kadai ya isa yasa ya cigaba da tirsasa kansa gurin Nawwara, domin ita ce kadai macen da ta kawo masa wannan farinciki a rayuwa, bayan ya yanke tsammanin zuwansa.
‘I promise you Noor i will to my very own best na ga na zama uba na gari a gareka, i will make you and Nawwara proud of me’
A kasan zuciyaraa yake wannan tunanin yana sauke ajiyar zuciya.
“Ba zan iya hakura da kw ba Nawwara, kema kina bukatar farinciki a rayuwarki, ni na bata komai dan haka ni ya kamata ace na gyara komai”
Wannan karon a fili ya yi furucin yana danna horn a bakin gate din gidansa, a hankali ya yi parking sannan ya dauko wayarsa ya yi ma Nawwara text akan cewar an sallami Noor saboda kar taje asibitin bata tarar da kowa ba, sannan ya fita motar ya zagaya ya bude ya dauko Noor da ke kokarin bude idanuwansa.
“Zan iya tafiya”
Ya fada saboda ya samu a sauke shi ya samu kallon gidan da kyau, kamar Jibril ya sani sai ya sauke shi ya rika hannunsa suna tafiya a hankali, rabon ido kawai Noor yake kamar zasu fado sabo kallon yadda kukasan wani tsohon bakauye, yana saka kafarsa cikin falon sai sayin tile din ya ratsashi ga sanyin ac da ya mamaye ko ina a cikin falon, suna shigowa Jibril ya sake shi ya nufi bedroom yana amsa waya, sai Noor ya daga kansa sama yana kallon pop falon da fankar kamin da dawo gurin kujerun falon da suka katsance farare sol kamar fentin falon da kuma center carpet din da ke falon, karasawa ya yi gurin kujeru sai ya zauna kasa ya kai hannu yana shafa manyan cushion din idanuwansa kuma suna kan katuwar plasma TV mai daukar ido gashi an kawata gurin da wallpaper fari mai daukar hankali, ga wasu manyan flowers da aka aje a gurin suma farar kamar labulayen falon.
“Noor Son tashi tashi zauna saman kujera ya zaka dauka kasa”
Jibril ya fada ganin dansa a kasa kamar wani almajiri.
“Momy ta ce idan mun shiga gidan mutane mu daina hawa musu kan kujera, kuma wasu mutane fada suke idan aka hau musu kujera”
Noor ya fada yana kallon Jibril da ya risino da kansa ya dauke ya dora saman kujerar ya rumgume ya lumshe ido, jikinsa ya yi sanyi sosai taya za a ce yana da irin wannan kudin amman ya kasa bawa dansa kulawa ta musamman da har wani abun na duniya zai burgeni ya kasa hawa? Shi ai iyayensa sun bashi kulawa taya ya kasa bawa dansa?
‘Lokaci be kure ba yanzu ma zaka iya he's still a boy’
Wata zuciyar ta amsa masa wanda hakan yasa shi jin sauki, har ya bude ido ya kalli hoton Nawwara da Noor ke nuna masa.
“Laaaa ji Momy can”
“Kai ma za a maka naka ina son ka sosai Noor”
Noor ya dago ya kalleshi ganin ya yi masa abunda ba a saba masa ba, wato kiss shi dai yana ma Momysa amman ita bata masa jara ma Mama Habiba wani lokacin tana masa kiss idan ya yi abun kirki.
“Me kake so ka ci?”
“Bana jin yunwa a yanzu sai anjima, amman akan wacan abun zan ci”
Ya fada yana nuna dinning area da aka kawata da farin dinning table da aka kawata da farin cabinets mai kyau da kuma freezer da ke hade da cabinets din har baka iya banbancewa. Jibril ya shafa kansa yana murmushi.
“Idan ma a saman dakin nan kake son cin abinci Noor zan dora ka ka ci, ka saki jikinka nan gidanku ne”
“Da gaske?”
Ya gyada masa kai.
“Har da Momy nan zata zo mu zauna? Kuma da Inna?”
Ya sake gyada masa kai yana murmushi, sai Noor ya sauka saman kujerar yana kallon falon bakinsa har kunne hakuran nan a watse bakauye ya shigo gari.
“Can ina ne?”
Ya nuna Kitchen.
“Jeka ka gani”
Sai ya mika hannunaa ya riko hannun Daddynsa
“Aa zo muje tare dai”
“Idan na rigaka isa ba zan bari na shiga ciki ba idan kuma kai ka rigani isa ba zaka bari na shiga ciki ba, ka yarda?”
Ya daga kai yana dariya, sai suka fara yar tseren gudu shi da Jibril da yana lakkame da hannunsa mai ciwo, da gangan Jibril ya bari Noor ya riga shi isa sai duk suka rika dariya Noor har da tsalle, abunda ya dauki hankalin babansa sosai yana kallonsa kamar ya hadeyeshi saboda Kauna.
Suna fitowa daga kitchen din suka sake rigangan shiga bedroom haka suka bi suka zagaje gidan Jibril ya nuna masa ko ina har Swimming pool, a Garden sai da Jibril ya hau icen guava ya katso masa sannan aka sauna lafiya.
“Acan za a saka maka lilo”
Jibril ya fada yana nuna wani bangare na Garden din, sai Noor ya zaro ido.
“Da gaske”
“Eh har dakinka za a maka daban, a saka maka komai da komai har da tv ka da games”
Dadi ne yasa Noor ya rumgumeshi yana dariya, sai kuma ya dago kai ya kalleshi
“Sai gobe zamu je mu lallabata sai ta dawo nan mu zauna, mu a nan zamu kauna har gobe ko?”
Ya daga masa kai, sai Jibril yasa hannunsa ya daukosa suka nufo falo, saman kujera ya zaunar da shi ya yi masa hotuna kala kala har da video sannan ya kunna masa tv ya saka masa kids channel sai yazo ya dauke ya rumgume suna kallon tv tare.
NAWWARA POV.
Tsayawa na yi kallonta saboda na tantancewa idanuwa ita din ce ko kuwa wata ce mai kama da ita, idan har ita dince to gaskiya ta canja sosai fuskarta ta yi kala biyu fari da kuma wani farin na daban, ga wata uwar rama da ta yi fuskarta ta matse sosai.
“Na san zaki yi mamakin ganina Nawwara, kin yi kokari da baki manta fuskata ba duk tsawon wannan lokacin”
“Taya zan manta fuskar da ta kwace min yan ce a gidan aurena? Fuskar da mijina ya fifita sama da tawa”
“Ashe har yanzu a akwai soyayyar Jibril a cikin zuciyarki tun da har za ki iya kiransa da sunan mijinki”
“Miya kawo ki gidanmu? Taya kika zo me kike nema a gareni?”
“Wacce daga cikin ukun tambayar ki nan zan fara amsawa?”
“Duka zaki amsa min kuma ki tashi ki bar mana gida”
“Zan tafi Nawwara gidanku ya yi min yawa da zama, amman ina son ki bani lokacin ki ki saurari abunda zan fada miki ko kuma na ce zan rokeki”
Kamar ba zan zauna ba, sai kuma na zauna saman gadon Inna ina kallonta da jiran abunda zai fito bakinta.
“Na san za ki yi mamaki ganina a wannan lokacin kuma a cikin gidanku, abun da ya fi ko wanne mamaki ma taya aka yi yarinyar da ke Abuja ta zo har sokoto kuma ta gane gidanku ko”
“Ba abun mamaki ba ne Jibril zai iya fada miki”
Na fada mata kai tsaye, sai ta yi murmushin da ke nuna cewar maganar ta soketa.
“Mai zai sa Jibril ya fada min inda kike bayan ya gargade da cewar na fita daga rayuwarsa? Rabon da na saka Jibril a ido shekara biyu da rabi kuma saboda ke Nawwara”
“Ni kuma?”
Na tambaya da mamaki sai ta gyada min kai.
“Ke fa, sai bayan ya rabu da ke ya gane yaudarar kansa yake da cewar baya son ki, ni kaina a wacan lokacin na san yana sonki ko da kuwa baya son ki tau ya san kimarki domin baya taba bari wani ya fadi wata magana marar dadi gareki a gaban idanunki ko bayan idonkin ciki kuwa har da ni”
“Ban tambayeki labarin abunda ya wuce ko abunda zai zo gaba ba, dalilin zuwanki kawai nake son ji”
Ajiyar zuciya ta sauke ta kalleni idanuwanta raurau ta ce.
“Yafiyarki na zo nema Nawwara”
“Ai ni baki min komai ba”
“Na yi komai Nawwara, na tozarta aure na yi amfani da dama ta na ci mutunci auren wata taya Allah ya zai bar ni na gina tawa rayuwar auren a cikin kwanciyar hankali? Bayan ban so yar'uwata abunda na so wa kaina ba?
Kaddarorin rayuwa sun yi ta faruwa da ni Nawwara wanda na ke sa ran saboda na ci mutuncin aurenki ne, a iya sanin da kika min ina budurwa har yau ina nan haka ban yi aure ba, a lokacin da muke soyayya da Jibril muna tsaka da maganar aure sai kawai babansa ya cilasta masa aurenki, a wacan lokacin Jibril sai yake ganin kamar idan ya rabu da ni be aureni ya ci amanata, da wannan damar na yi amfani na dauke masa hankali, ni da kaina na rika jan ra'ayinsa har muka fada kogin aikata alfasha wato zina, a tunani wayewa ce na yaudari kaina sosai da sakewa namiji jiki tun kamin ya aureni, ba ni da tufafin sakawa sai na tsiraici gyale ma irin wanda zai bayyana siffar jikina na ke sakawa saboda na dauki hankalinsa, haka duniya ta yi ta yaudarata har muka tsufa a kogin alfasha ban ankaro ba, bayan Jibril ya rabu da ke sai na bijirowa da Jibril maganar aurenmu abun mamaki sai ya ki amincewa, kin san dalili? Saboda ya riga ya san ni a ya mace tun kamin ya aureni, sai ya zamo baya ganin kimata kuma rashin yarda ta shiga tsakaninmu har ta kai shi da kansa yake cewa ko ya aureni ba zai samu natsuwa ba domin zuciyarsa tana raya masa bayan shi zan iya taraiya da wasu mazan, ina ji ina gani Jibril ya auri wasu matan ya bar a lokacin na ko sunana baya son a kira, ni kuma na gagara samun wani mijin aure na kirki saboda kowa kallon yar iska yake min, saboda na riga na gama zubar da mutunci na tun a yanayin suturata, duk wanda yanzo ba da aure zai neme ni ba sai dai da lalata ko kuma soyayya, wadanda suka zo neman aurena da gaske kuma sai a bi a zuge, a haka zama garin Abuja ya gagareni na koma gurin Yayata Kaduna, na natsu sosai a lokacin na zama ta kwarai fiye da yadda kike tsammani, amman mutuncin da na gagara tsarewa tun a wacan lokacin sai ya kasa bani damar na yi rayuwa yadda na ke so, a haka na fara shafa man nan na mai saka haske wai ko farina zai karu na kara burge maza amman a banza sai ma lalata fatata da na yi, ke ce kadai kika tsaya min a rai ina gani kamar hakkin ki ne yake bibiyata dan Allah dan girman Allah dan darajar Annabinsa ki dubi girman Allah ki yafe min Nawwara”
Kuka take sosai tana kokarin kama kafafuna, wanda hakan ke tabbatar min da cewar lallai Aysha ta yi nadama, sai dai me abunda bata sani ba, ba hakkina ne kawai yake binta ba, tabbas hakkin aure ba zai barta ba saboda ta tozarta da aure a lokacin da ta samu dama, amman an baro kyau tun ranar haihuwa, domin kuwa ta yi abun da yan mata yanzu suka dauka wayewa wato bayarda kai ga Namiji tun kamin ka aureshi da kuma shigar banza wacce Annabi Allah da kansa yake cewa masu wannan shigar tufafin ba zasu shiga aljannaba kuma ba za su ji kamshinta ba, taya namijin da ya sakin tun a gidanku zai yarda ya aureki? Ko da kuwa ya aureki ba zai taba ganin darajar ki ba kuma babu aminci na zaman aure a tsakaninku har a bada ga kuma azabar Allah tana jiranki matukar baki tuba ba, daman shi namiji duk abunda ya aikata ado ne, ko ina a qur'ane idan Allah zai ambata da da namiji yake farawa sannan mace amman da aka kai babin Zina sai Allah ya fara da macen kamin namiji saboda mace tafi shiga tarko kuma idan bata bada dama ba babu yadda za ayi ta namiji ya aikata.
Ajiyar zuciya na sauke zan yi magana sai ga text ya shigo a wayata na Jibril, wai an sallami Noor kuma ya tafi gida da shi sai gobe za su zo nan. Aje wayar na yi na kalleta zan yi magana sai ga Inna ta shigo cikin dakin tana tambayar lafiya jin shisshikar kukan Aysha.
____________________________________
Al-hamdulillah godiya ta tabbata ga Ubangijin da ke ba mu lafiya da rashinta, na samu sauki sosai na gode sosai da kukawarku da addu'o'inku Jazakallahu Khairan 😘
Let my advice be here, For those ladies da suke daukar mallaka kai ga saurayi ko da an muku engaged a matsayin wayewa ko soyayya Wallahi babu soyayya babu wayewa a cikin zina, kuma ko da mutun ya aureki baki da wata kima da mutunci a idanuwanshi, wani ma ba zai aureki ba kin ga kin ga kin zubar da mutunci a banza, kar kalaman banxa su yaudari zuciyarki kar karatun wasu littafan yasa ki rika daukar saka suturar banza a matsayin wayewa Wallahi ba duka writers ba ne include me suke rubuta dai dai ko rashinsa ba me some of our readers suna daukar dukan abunda aka rubuta ko abunda duniya take yayi a matsayin wayewa wanda sam ba haka ne kama mutunci da kimarki shi zai nunawa duniya ko wacece ke kuma mijinki da yayanki zasu yi alfahari da wannan, kar ki ga wata ta yi haka at the end ta auri a mijin kwarai a novels ne ko movies irin wannan abun yake faruwa, in reality 75% basa auren mutanen kirki matukar kika maida kanki karuwa babu namijin kwarai da zai so ki a matsayin matarsa, su ma mazajen na banza ai matan kwarai suke nema su aura, be wise, women with attitude na kwarai a lady with class class din kuma na kare mutunci ba na zubarwa, ko da ke ta kwarai a irin shigar da kike wani zai dauka ke