Showing 54001 words to 57000 words out of 138998 words
a aljihu ya nufi window.
“Ban san ko sau nawa zan faɗa masa ya yarda ba, Wallahi na faɗa na ƙara duk wata mace da ba Aisha ba bana son ta, amman mahaifina ya tsaya kai da fata akan sai na auro wata, ya neman min auren ƴar Alhaji Dahiru ne saboda yana yaba tarbiyar gidan kuma yana son zumuncinsu ya ƙara ƙulluwa, after that you're not his biological daughter, jin wannan yasa Mahaifina ya ɗaga min ƙafa, amman Alhaji Dahiru ya dage akan shi yana son ayi, har da cewar wai baya son auren ya ɗauki lokaci.
Aurena da ke baiwar Allah ba alheri ba ne, domin ni dai har ga Allah bana son ki, lemme ask you some questions, shin zaki iya auren namijin da ya taɓa kusantar wata mace kamin ke? Zaki auren Namijin da ya taɓa sanin wata mace kamin ke? Zaki iya zama da namijin da zuciyarsa da gangar jikinsa duk na wata macen ne? Could you?”
Na girgiza masa kai.
“No i couldn't, ba zan iya auren namijin da ba be san ƙimar zaɓin iyayenshi ba”
Ya matso kusa da ni cikin ɓacin rai, ya riƙa fuskata ya soma magana cikin murya mai amsa amo biyu.
“how dare you, ke iyayenki sun san ƙimarki ne zasu barki hannun wani saboda ƙwadayin abun duniya, bayan baku haɗa komai da shi ba daga gadi! Wallahi duk kika aure kin saka rayuwarki cikin matsala sai kin ƙwammace kiɗa da karatu, duk wanda ya ce zai raba ni da Aisha ba zai sha da daɗi ba”
Ya ciro wayarsa da ɗayan hannunsa ya nuna min hotonta da ke gaban wayarsa, yana matsar min fuska iya ƙarfinsa, a nan na fara kokuwar kuɓucewa amman na kasa.
“Wannan matar ta fiye min ke sau dubu ɗari, dan haka karki yaudari zuciyarki kar kwaɗayin abun duniya yasa ki salwantar da rayuwarki ni da ke kamar RAI BIYU ne wuta da ruwa ba zamu taɓa haɗuwa ba, you bitch...!”
Yana kaiwa nan ya wulgar da ni saman manyan cushion, ya yi ficewarsa cikin zafin rai. Ni kuma na tashi zaune da sauri ina taɓa bakina da nake tunanin yama fara jini saboda zogin da yake min.
Na kusan minti goma a falon sannan na fito ina ta ƙoƙarin ɓoye abunda ke fuskata. Ban tararda Salima a falon ba, sai Hajiya Zainab da yaranta ƴan mata da ke ta min kallon uku saura kwata.
“Direba zai maida ke gida, Salima ta koma tuni saboda an kira Daddy ku ba lafiya”
Gabana ya faɗi sosai, miya samu Daddy ina ta tambayar kaina har na fito harabar gidan na nufi inda direba yake, na shiga bayan motar sai ga wata budurwa ta zo da jakunkuna ta saka min a motar sannan direba ya kama hanyar gida da ni, tun kamin mu isa gida na fara hawaye saboda tunanin abunda ya sami Daddy da kuma baƙin cikin abunda Jibril ya yi min.
**RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
3⃣0⃣
Ganin Motar Anty Mairo da Zubaida wato manyan ƴaƴansa guda biyu a harabar gidan ya ƙara tayar min hankali, cike da fargabar abunda ya samu Daddy na fita motar na nufi cikin gidan.
A falon Momy babu kowa sai ƴar aikinta Suwaiba, ban tsaya komai ba na nufi part ɗin Daddy. Mamaki ne ya maye gurbin tashin hankalina, sai ya zo akasin tunanina da kuma furuncin step mother ɗin Jibril cewar Daddy ba shi da lafiya.
A sanyaye na shigo falon idona kan Daddy dake making call yana murmushi, ban ankaro da ban yi sallama ba sai da Anty Zubaida ta hankarar da ni ta hanyar amsa min da.
“Wa'alaikissalam”
Saurin share hawayen fuskata na yi na yi sallamar duk da kasancewar na kai tsakiyar falon. Sai duk suka haɗa baki gurin amsa min ciki har da Momy. Cike da mamaki na zauna kusa da Anty Zubaida ina cigaba da kallon Daddy.
“Nawwara har kin dawo?”
Cewar Momy.
“Eh ko da na fito Salima ta dawo gida ko da na fito Hajiya tace min Salima ta wuce wai Daddy ba lafiya”
“Ee na kirata na ce ta dawo gida jikin Daddynta ya tashi amman da sauƙi daman jinin ne ya hau amman ya sauka”
Ajiyar zuciya na sauke na kalli Daddy da ya aje waya a kunnensa ina masa ya jikin.
“Alhamdulillah, ya kika baro can ina fatar kina son shi?”
Har na buɗe baki na yi magana sai Momy ta yi karaf ta karɓe.
“Kana maganar tana son shi Alhaji wace mace ce zata kalli Jibril ta ce bata son shi, ai Hajiya ta kirani ta faɗa min sun fahimcin junansu sosai kuma shima ya yaba da ita sosai”
Ƙasa na yi da kaina saboda bana son ƙaryatata ko kuma na kunyata ta a gaban ƴaƴanta akan wannan zancen da ba haka yake ba.
“Maa Sha Allah, haka muke so Allah ya tabbatar da alheri a ciki, mahaufinsa ma ya faɗa min yana son a ɗaura masu aure kamin ta koma makaranta albashi idan ta kammala sai ayi bikinsu”
Jin wannan maganar ta Daddy yasa idanuwa cika da ƙwalla. Anty Zubaida da Anty Mairo suka shiga tsokanata har ma da Salima, ban san lokacin da na fashe da kuka ba na tashi da gudu na bar falon.
Ɗakinmu ma dawo na zauna bakin gado ina ta kuka, wata zuciyar na raya min na kira Baba na faɗa masa wata na cewa a'a, tabbas a lokacin ina son Jibril amman rashin aurensa shi zai fi min alheri tun da har ya nuna min akwai wacce yake so.
Ina ta tunanin mafita sai ga Momy ta shigo ɗakin tare da Salima tana faɗin.
“Kun saka min ƴa kuka bari na rarrashi abata”
Tana zaunawa kusa da ni sai ta kore Salima daga ɗakin da sunan zata rarrasheni, Salima na fita sai ta canja fuska ta kalleni
“Iyakar halacci Nawwara mun miki ke da iyayenki, ashe ko ba mu cancanci komai ba sai kyakkawan sakamako, kin dai san Alhaji ba zai miki zaɓin da zai cutar da ke ba, kuma wannan auren da kike gani idan har kika aureshi ke da danginku duk kun warke, ƙin yi wannan auren zai ɓata abotar Daddynku da shi na tsawon shekaru ashirin, idan kuma kika yarda kika aureshi tam kamar kin zuba babban jari ne a dukiyar gidan nan da kuma ta gidanku, domin mahaiɗinsa na cikin masu kuɗin da ake ƙirgawa da su a africa ba ma Nigeria kaɗai ba”
Na ɗaga kai na kalleta cikin muryar kuka na ce
“Amman Momy baya so na yana da wacce yake so, kuma ya faɗa min matuƙar na yarda na aureshi sai na yi nadama”
“Ai nasan baya son ki, daman taya za'ayi Namiji kamar Jibril ya so mace irin ki? Yaron da yake ganin ƴaƴan turawa da larabawa, kuma ɗan da magana kawai zai yi ma kuɗi su faɗo ƙasa sai kalli ƴar talaka irinki ya ce yana sonta? Ke ni fa Salima na so a bashi amman Alhaji yaƙi wai wani ya riga ya bada ita ba zai ce ya fasa ba saboda wannan, amman idan kika yi haƙuri da sannu zai fara sonki har ya kyautata miki, ke ko be so ki dole zai kyautata miki domin su masu kuɗi matuƙar suna auren mace dole ne su kyautata mata domin dukiya bata musu zafi.
Nawwara karki yarda ki faɗa ko ki nunawa Alhaji cewar baki son zaɓin da ya yi miki domin hakan zai iyasa zuciyarsa ta buga ya mutu gaba ɗaya, dan Allah ki yi min alƙawari zaki auri Jibril albashi idan daga baya kika ga zaki fito sai ki ce ya sakeki, kuma kin ga waje ma zaku zauna kina karatunki shi yana sha'aninsa”
Ta ƙarasa tana riƙe hannuna cike da magiya. Kai kawai na iya ɗaga mata alamar na amince ba dan raina ya so ba, har ga Allah ni kaɗaina ina ganin kamar idan ban auri zaɓin Daddy ba ban masa halacci ba.
Bayan fitarta Salima ta shigo tana zolayana, yadda ta ga ina kuka ya tsorata ta har ta soma tambayar ko wani abun ne ni kuma na amsa mata da ba komai.
A haka na jure na kauda kaina daga duk wani abu da zai nuna bana son auren saboda kar ran Daddy ya ɓace, su kuma sai hidimar ɗaurin auren suke har ana daf da ɗaura aure Baba be daina min magana akan idan bana sonsa na faɗa ba, amman na ƙi na faɗa, ni dai kawai na ɗaukarwa kaina alƙawarin zan jure ko ma minene saboda na zama ƴar halak a gurin Daddy da Momy.
Ana cikin haka ne Ya Jamil ya samu transfer gurin aiki zuwa Jos, ni kaina na jidaɗin haka nasan idan ya yi nisa da ni zan fi samun sakewa.
Sai da ana sauran kwana biyu ɗauren auren Jibril be taɓa kirana ko a waya ba, kuma be je ya gaishe da Baba ba, sai dai Mahaifinsa ya tafi tare da muƙƙarabbansa suka gaishe da Baba, komai a ɗaurin auren a nan Abuja aka yi saboda haka sai ranar da aka ɗaura min aure sannan mahaifina ya ga fuskar mijin ƴarsa kasancewar ya samu halarta tare da wasu ƴan'uwansa.
Na ji ni daban a cikin wani yanayi marar misaltuwa a wannan ranar, bana farinciki kuma bana baƙinciki ni dai kuka kawai na ke kukan da ban san dalilinsa ba, ganin haka yasa Momy ta kaini ɗaki ta ja min kunne akan na daina kukan kar mutane su zargi wani abu, haka na wanke fuskata na keɓe kaina a ɗaki har sai da ka ce na fito ga Baba can zamu gaisa.
Babu wata gaisuwa da na yi da dashi sai ta kuka kuka na yi sosai har sai da shi ma na saka shi kuka, ya yi min nasiha sosai akan rayuwa da kuma zamantakewar aure, ya faɗa min yanzu na tashi daga ikonsa na koma ikon wani, hakan yasa na ji ni cikin wani babban ɗaki mai nauyi.
Washe gari ma da zai koma sai da ya kirani shi da ƴan uwansa suka zagaye ni suna min huɗuba mai ratsa jiki.
Kwana biyu da ɗaura min aure aka kwantar da ni a babbar asibitin Abuja saboda rashin lafiyar da ya taso min, a wannan ranar ce Jibril ya hau jirgi ya bar ƙasar nan, har na yi jinyar na gama be taɓa kirana ba sai dai mahaifinsa da wasu Sisters na sa sun zo duba ni da kuma step mother ɗinsa, Mahaifinsa ne ya fi nuna min kulawa da damuwa, su kan kamar daman sun zo ne by force.
Bayan an sallameni da kwana biyu Salima ta fara shirin zuwa makaranta, ni kuma Daddy ya hana ni da sunan wai ba zan koma ba sai na ƙara jin sauƙi, ni kuma ban musa musu ba na amince, ina ji ina gani Salima ta koma makaranta ni ina nan.
Yana lura da yanayi na sosai, har ta kai wata rana ya kirani a ɗakinsa ya tambayeni ko dai bana son auren ne, sai an kasa amsa masa, ya yi min nasiha akan haƙuri da halin Jibril wai daman yasan za a samu haka saboda baya son auren kwata-kwata babu zancen aure a gabansa, wannan yarinyar ce kawai yake kulawa ita kuma ba ƴar mutunci ba ce zaman kanta take wannan dalilin ya saka mahaifinsa ya ƙi yarda ya aureta, a ranar yake labarta min cewar Jibril ne ya hana na koma makaranta wai ya ce be bada izinin na koma makaranta ba.
Ranar na yi kuka sosai har sai dai na raina kaina, mutumen da ba zai iya kirana ya tambayi tafiyata ba shi ne zai ce bada umarnin kar a barni na koma karanta kuma a ƙyaleshi saboda kawai yana taƙama da kuɗi.
A haka na kwashe wata shida a ban koma makaranta ba, idan kuma nunawa Momy ina son anje gida gurinsu Inna sai ta ce min ba haka ba, wai ba zata bari na tafi bada izinin mijina ba. Tun daga ranar da aka ɗaura min aure da Jibril duk wata sai Alhaji Bashir Makama ya aikowa da Momy kuɗi ya ce a bani amman bata taɓa bani ko naira ba, bata ma taɓa faɗa min ko nawa ba ne tana dai faɗan min ya aiko saboda kawai na yi masa godiya.
Tun da Jibril yasa ƙafarsa ya bar ƙasar nan be sake waigo Nigeria ba, kuma be taɓa ɗaukar waya ya kirani ba, wani daga familynsa be taɓa zuwa da sunan ganina ko duba lafiyata ba.
Da wannan baƙinciki na ke kwana na ke tashi ban taɓa nunawa kowa ba, sai dai hakan be hana Daddy damuwa ba, wata rana bayan na gama haɗa abun karyawa mun sai ya aiko yana kirana, ko da na shiga sai na samu Momy tare da shi, guri na samu na zauna na natsu ina ta sauraren abunda yake faɗa min.
“Na gaji da wannan halin na Jibril, ba zai yiyu ya ce ba zaki koma makaranta ba, kuma baki tare ɗakinki ba, tun da ya tafi be ma kira ya tambayi lafiyarki ba, dan haka na faɗawa mahaifinsa idan ba zasu iya tanƙwara ɗan su akan abunda suke so ba, ni ba zan cutar da ƴata ba, na faɗawa mahaifinsa idan har yana ganin rabuwa da ke shine maslaha tam mu muna maraba, kuma ina fatar wannan hukuncin ya yi miki”
Kamin na ce wani abu sai Momy ta yi karaf ta ce.
“Haba Alhaji yaran zamani ai sai an yi haƙuri, karka yi maganar raba auren su ko shekaran jiya na tambayeta ta faɗa min ita tana son mijinta, kawai ka yi ta musu addu'ah”
Kallo ɗaya na yi mata na ɗauke, wata ƙila tana min haka ne saboda ni ba ƴar ta ba ce, Daddy kan tuni ya gama gamsuwa da bayaninta, jiki a sanyaye na taso na fito daga part ɗin Daddy.
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
3⃣1⃣
A nawa tunani Momy tayi min haka ne tun farko saboda kar na auri ɗanta, yanzu kuma bata son a kashe auren ne saboda dukiyar gidansu Jibril tasan duk wulaƙancin da zai min ni ba ƴarta ba ce saboda haka wannan ba zai taɓa damunta ba, babu wanda zai fi jin zafi jin zafin ɗa kamar uwar da ta haifeshi, ni kaina da Mahaifana ne ce zan iya fahimtar da su kuma su fahimta, amman wannan duk abunda zan yi sai dai su kalleshi a a matsayin butulci.
Duk da maganar da Daddy ya ce yi ya sai da aka kwashe wata ɗaya har da kwanaki rana ɗaya Momy ta kirani wai na je na shirya yau Jibril zai zo ganina, gabana ya faɗi sosai har na ji ina ma ba zai zo ba har abada domin na san zuwan nasa ba alheri ba ne.
Wanka na sake na saka wasu tufafin kwaliya kan ban yi ba, mai ma dan ya zamin ne jikine yasa na shafa, daman ta saka mai aikinmu ta shirya masa abinci da lemu haɗin gida. Haka na zauna tun sha biyu na rana har magariba be zo ba kuma be kira ba, misalin goma sha na dare Momy ta shigo ɗakina wai na taso gashi can ya zo, Ba musu na tashi na cire kayan bachi dake jikina na ɗauki atamfa na saka da mayafi na saka takalmi na fito jikina a sanyaye na nufi part ɗin baƙi.
Tun a bakin ƙofar falon ƙamshin turarensa ya daki hancina hakan yasa gabana faɗuwa, da sallama na shiga falon amman be amsa min ba sai dai idonsa na kaina har na zauna a kujera na soma miƙo masa gaisuwa a kufile, nan ma be amsa ba, sai wani shan ƙamshin yake ya tsare fuskata da kallo kamar mai neman munina.
“Saboda ke Daddyna yasa na dawo garin nan, saboda ke ya cilasta min dawo wa da aiki a nigeria gaba daya, ke dan Allah ba ki jin kunyar yadda ake ta turaki gurin namiji kamar ni?”
Ɗagowa na yi na kalleshi kallon mamaki da takaici ina ma zai san abunda ke zuciyata da ya taimakamin ya rabu da ni, akwai tsantsan tsoro da fargaba a tare da ni a wacan lokacin shine abunda yake ta cutar da ni sai kuma zurfin ciki da ya zame min hali.
“Zuwanka da rashin zuwanka duka ɗaya ne a gurina, ni dai ina neman izininka zan koma makaranta”
Be ci komai daga abunda Momy tasa aka kawo masa ba, sai ya tashi tsaye ya nufo inda nake ya zauna kusa da ni har jikinsa na shafar nawa ya matso da fuskarsa kusa da tawa ta yadda ni kaɗai zan iya jin abunda zai fito bakinsa sannan ya kalleni ya na ƙara haɗe fuska ya ce.
“Ba aure kika zaɓa ba? Tam zaman aure zaki yi babu ke babu karatu har a bada, ai baki san waye Jibril ba kina da butaƙar sanin wanene tuƙunan”
Yana kaiwa nan ya tashi tsaye na saka hannunsa aljihu ya ciro kuɗi ya watsa min.
“Ga tsiyarki nan”
Ni kuma na miƙe tsaye ina kallonsa na ce
“Tsiyarka dai, tsiyar da ta saka baka ganin kowa da mutunci, na ji ni ƴar talaka ce kuma ni talaka ce amman haka ba zai baka damar ka yi min duk kalar wulaƙancin da ka ga dama ba, kuɗi kawai kake da shi Jibril ni kuma na ɗara ka da tarbiya da biyayya”
Murmushin gefen fuska ya yi ya taɓe baki.
“Fine, zamu gani”
Daga haka ya fice, ni kuma na koma cikin gida ko inda kuɗin suke ban kalla ba, zuciyata cike da ƙuna.
Tun daga wannan lokacin be kuma sake zuwaba sai da aka sake yin wata ɗaya sannan ya kira Momy a waya yana tambayar lafiyata shi ma kuma na san cilasta masa aka yi, bayan ya tambayi Momy aka kawo min wayar sai ya kashe ba tare da ya ce da ni komai ba, a ranar n samu Momy na yi mata bayani akan bana son Jibril kuma bana son zaman aure da shi sai ta muna min na yi haƙuri komai zai wuce da zarar na tare a gidansa, ganin bata goya min bayan rabuwa da shi ba yasa na samu Daddyda kaina na kuka masa halin Jibril da abunda na ke hangowa a zamantakewar auren da zamu yi, amman sai ya bani haƙuri saboda a tunaninsa saboda na daɗe a gidana ne yasa nake wannan tunanin shi ma sai