Showing 81001 words to 84000 words out of 138998 words
ma Inna sallama. Gidansu Jidda na nufa da Mamanta muka fara gaisawa sannan na shiga dakinta sai ta juya min baya tana dannar wayar da ke hannunta. Ban damu ba na zauna gefen katifarta na soma mata magana.
“Jiya na yi mafarkinki Jidda, na yi mafarkin Mustapha zai cutar da ke”
Tayi banza da ni kamar bata ji ni ba, ganin hakan yasa na tashi zan fita sai ta kira sunana.
“Nawwara”
Hawaye na gani a idonta.
“Yi hakuri”
Dawowa na yi na zauna sai na dafata na fashe da kuka sosai, kwantar da ni tayi kafadarta sai da na yi kuka na gaji sannan na labarta mata abunda ya faru tsakani da Jibril da kuma iyayesa da suka zo gidanmu.
“Ki kara hakuri Nawwara ba gashi kin fara ganin sakamako ba, ni dai abunda na ke so ki yafewa Mustapha”
“Zan yafe masa”
“Amman..... Zaki iya”
Sai kuma ta yi shiru.
“Tashi kije karki makara”
Ta fada, ni kuma na tashi sai ta rakoni har kofar gida sannan na fice ita kuma ta koma. A hanya na hadu da Mustapha ina tunanin ita ta fada masa gani nan na fito, sai ya sha gabana da motarsa sannan ya bude ya fito, sai kuma ya kasa ce min komai sai kallona yake.
“Na yafe maka Mustapha ka dauka kamar komai be faru ba, amman zan gargadeka karka sake shiga hanyata, dan Allah dan Annabi ka fita hanyata”
Ina fadar hakan na kama gabana na cigaba da tafiyata na barshi nan tsaye yana ta kallona.
Har na yi kamar na bi ta gurin gidansu Bilal duk da na san by this time yana gurin aiki, sai kuma na bi hanyar da na saba bi.
Na isa gurin aikin da misalin sha biyu saura kwata, yau ma atamfar roba ce a jikina da gyale. Kai tsaye na wuce gurin aikina zuciyata cike da son ganin Bilal, sai dai ban san takamaiman inda yake aiki ba.
Ina isa kofar ta bude min, office dina na fara gyarawa sannan na shiga na shi Office din baya cikin hakan na nufin be shigo ba kenan, sai na na gyara komai sannan na fito, ko da na dawo nawa Office din wato office din farko wayata na ringing alamar kira ko da na duba sai na ga Number Zinatu da fari na yi mamakin da sunanta ya yi appearing a wayata sai dai tuna Rabi data karbi wayata tace za a saka min numbers mutane kuma nima a basu tawa yasa danna picking na kara a kunne.
“Nawwara dan Allah ki sauko hawa na biyu yanzu”
“Me zanyi?”
“Dan Allah dai ki sauko Bilal yake nemanki”
“Okay”
Cikin hanzari na fita na shiga lifter, a hawa na biyu na sauka komai na gurin glass ne ma'ana wani ma'aikacin yana iya hango dan uwansa, haka na rika duba sunayen da ke gurin har na kai ga wanda aka rubuta Bilal Usman na tura na shiga, sai na samu dakin cike da mutane duka tsaye wani katon cake na gaban Bilal da wuka a jiki,
Ina shigowa sai hankalinsa ya dawo kaina kamar marar gaskiya, sam baya farinciki kamar ba shi suke yi ma wakar happy birthday ba, kasa jurewa na yi sai idanuwa suka cika da kwalla, shi kuma ya gagara karbar cake din da Zinatu take kokarin kai masa a baki.
“Happy birthday my dear”
Shi kuma hankalinsa gaba daya a tashe yake ni kawai yake kallo.
__________________________________________
Masu son ganin Jibril da Mustapha da Bilal da Nawwara ku kwatantasu a idonku, ni dai iya abunda na sani Bilal ya fi su kyau 😜
#COMMENT
#VOTE
#SHARE
#FOLLOW.
kalmomi dubu hudu na yi🙄 dan haka har na jibi ne wannan 👻
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
*Shafin yau na ku ne Maman Hannep Novels Group, Rai Biyu Fan's Group Khadeeja Candy Novels Group*❤🖤
4⃣1⃣
Tana daf da kai masa cake din a baki sai ya yi saurin rike hannunta.
“No thanks”
“Haba Bilal sai ka ce wani abu yau ne birthday ka fa”
Sake kai masa a baki da karfi har tana shafa masa ragowar da yake hannunta a fuska tana dariya ita da mutane da suke cikin office din. Sannan ta juyo ta kalleni
“Karo mana Nawwara let's have fun”
“No ina da aiki a ciki, Happy birthday Bilal”
Na fada idanuwa cike da kwalla, sannan na juya na fito hawaye na bin fuskata.
Ban yi nisa a tafiyarba na ji muryarsa yana kirana ni kuma na kara sauri kamin ya karo inda nake har na shige lifted, ina sauka hawa na biyar na shige Office ina kuka, ko mintuna ban yi da zama ba sai gashi yazo gurin kofar, ina kallonsa ta computer na ki budewa sai kuka na ke har ga Allah na ji zafin wannan abun, da ya gaji da tsayuwa ya kirani, ban daga ba har ta yi ringing ta gaji ta katse, haka ya jera min kira har guda goma sha uku ban dauka ba, be bar gurinba sai da Jibril ya karaso sannan ya yi hanzarin barin gurin, ni kuma na yi saurin tashi na share hawayena, sai dai hakan be hana shi fahimtar kuka na yi ba.
“Good morning”
Na fada ina a tsaye idanuwa a kasa muryata na bayyana kukana, a maimakon ya amsa min sai kawai ya karaso gaban table dina yana kallon fuskata.
“Me kike yi ma kuka?”
“Ba komai”
Na fada idanuwa na kara cika da kwalla.
“Fada min mana waya taba ki?”
“Babu”
“Aikin ne baki so?”
Na kasa amsawa sai hawaye nake.
“Mi Bilal ya zo yi nan? Miyasa kika ki bude masa?”
“Ba komai”
Ya daki table dina.
“Dole ne ki fada min abunda yasa Gimbiyata zubar wannan hawayen mai daraja da tsada”
Ya fada kamar ba shi ya yi maganar fuskarsa babu alamun wasa sai ma kara hade rai da ya yi
“He's just come to apologise”
“Apologise for what?”
“Yau ya yi birthday, shine ya yi celebration tare da Zinatu”
Kallona ya tsaya yi sosai kamar mai karantar abu a fuskata, sai kuma ya kyalkyale da dariya har sai da office din ya dauka gaba yana amsa amonsa.
“Wow wow so that's means Zinatu ya ke so ba ke ba? Daman can ba saurayinki ba ne ko? Ko kuma...”
Ganin yadda na ke hawaye yasa shi saurin rufe baki yana gintse dariyar da ke cinsa.
“Okay calm down Naj-Babe i will talk to both of them”
Yana fadar hakan ya nufi office dinsa sai cigaba ya ke da dariyar, kamar cikinsa zai fashe. Ni kuma na zauna a gurin hawaye na ta min zuba zuciyata kuma na mugun zafi.
JIBRIL POV.
Be shigo office din da dadin rai ba, amman wannan labarin na ya faranta masa rai.
“Excellent”
Ya furta yana kokarin zama, abun ya fi tsaya masa a rai Zinatu da gaske tana son shi ko kuma ta yi ne kawai as a friend ita kuma Nawwara kishi ya rufeta.
“Wow”
Ya furta yana dora kafarsa daya saman daya yana lilo da kujerar.
“Allah ya kara raba kanku”
Bayan kamar thirty minutes Nawwara ta shigo Office din idonta a kasa.
“Kana bukatar wani abun ne?”
Kallonta yake, ya ji dadin abunda ya faru amman wannan halin da take ciki baya son shi ga hawayen da ta kasa dainawa har yanzu, yasan tana jin kwatankwacin irin zafin da yake ji a duk lokacin da ta kula wani ba shi ba. Mika hannu ya yi zai riko hannunta sai ta yanje ta yi cikinsa da masifa.
“Miyasa kake son taba hannuna ne? Miyasa kuka dauki rumgumar mace da taba hannunta a matsayin wayewa? Baka san zunubin da ke akwai a taba hannun mace da ba muharramarka ba? Baka da rayuwa mai kyau Jibril”
Uffan be ce mata ba har ta juya ta fita, sai dai maganganunta suna masa zafi, baya jindadin yadda duk maganar da ta zo mata a baki take fada masa, ciwon da ke damunsa ne ya taso masa har yana neman numfashinsa sai da ya dinga sauke ajiyar zuciya yana dafe zuciyar sannan ya samu sassauci har ya nufi freezer ya sha ruwa, sai kuma ya bude durowarsa ya dauko cocaine ya zo ya zauna gaban teburinsa ya soma shaka. Sai ga Nawwara ta shigo da wasu takardu a hannunta tsayawa ya yi kallonta kamar yadda ita ma take kallonsa.
“Kana da meeting da pearls global company misalin sha biyu da rabi, wannan kuma daga Dr Ishak Hacker ne zaka saka hannune a maida masa”
Ta fada tana dora masa takardun saman table dinsa, kamar be damu da ganin da tayi masa yana shan cocaine ba ya dauki pen ya saka hannu, ita kuma ta juya ta fice ba tare da ce masa komai ba. Wayarsa ya dauka ya kira Siraj.
“Ka bincika?”
“Eh amman ance bata da wani da kuma binciken ya nuna bata ma taba yin ciki ba”
Ya busar da iskar bakinsa dan ba abunda yake son ji kenan ba.
“Ka tabbata?”
“Yes, walimar da kasa a shirya yau za'ayi”
“Thank you Siraj ayi abunda ya dace”
Ya katse kiran yana ta tunani, sam zuciyarsa bata yarda babu da tsakaninsa da Nawwara ba, ji yake kamar dai Siraj be yi binciken daidai ba, ko kuma Nawwara tasa a boye masa ne. Rabi ya kira dan jin yadda aka yi daman tun da ta kai kayan ta kirashi be dauka ba sai ta aiko masa da sako amman be bude ba.
“Good morning Sir”
“Ina jinki!”
“Na kira wayarka baka daga ba kuma na aiko maka da sako, anyi komai yadda ya dace Sir sai dai ita kadai na yi ma siyayyar”
Ta fada da zimmar ta ji abunda zai ce tace ba tayi ma yaronta ba dan ita a zatonta Jibril ya san da shi.
“Eh daman ita kadai zaki yi ma”
Yana fadar hakan ya kashe wayar yana jin kansa kamar marar lafiya. Sha biyu saura kwata Nawwara ta sake dawowa office din.
“Akwai wani abun da ya kamata muje da shi gurin meeting din ne?”
“Ee takardun kamfanin nan, suna cikin can”
Ya nuna mata wani katon box dake lake da ginin gurin, karasawa ta yi tana kokarin budewa amman ta kasa.
“Sai kin sa password”
“Miye password din?”
“N¹¹A²³W²¹W³¹A³³R¹³A”
Sunanta ne zere sai mixing da aka yi da numbers, tana saka. Password din sai ya bude, farkon box din cocaine ce mai yawa, na biyu kuma zinari ne irin wanda aka ciro cikin kasa ba a sarrafashi ba, sai dollars dake binsu daga karshe ne takardun suke.
“Duka zan dauko?”
“Ki duba files din wanda aka rubutawa 001 zaki dauko”
Daki-daki ta bisu har ta wanda yake magana akai ta dauko, sannan ya maida marfin box din ta rufe ta taso ta nufo table dinsa.
“Miyasa kake son shan cocaine ne?”
Yaja ragowar dake hancinsa sannan ya dauke idonsa daga barin kallonta.
“Saboda na rage damuwa da bacin rai”
“Waya fada maka tana cire damuwa?”
Ya mike tsaye ya nufi gurin window ya tsaya tare da sanya hannayensa aljihu.
“A lokacin da na haukace akan tunaninki na rabu da kowa, na watsar da dukan abokaina sai Allah ya hadani da Siraj, shi ne kadai mutumen da ya taimaki rayuwata na fara dawowa mutum da wannan cocaine din, a duk lokacin na shakata ina samun sassauci akan tunaninki, musamman a lokacin da take buguna ba kamar yanzu da bata min aiki ba”
“Amman miyasa kake sha?”
“Saboda ta zame min jiki”
“Idan har kana son ka kore damuwa ka rika daukar kur'ane kana karatu, ina tunanin ka san illar wannan cocaine din”
Ya juyo ya kalleta.
“Ba ni da wani zabi ne saboda tunaninki na fara shanta”
NAWWARA POV.
Ban sake ce masa komai ba na juyo ya baro office din, zuciya cike da rashin jindadin halin rayuwar da jibril yake yi. Yanzu akaf a familynsa a rasa wanda zai tsaya ya fada masa gaskiya akan rayuwa? Babu mai iya bata lokacinsa ya zauna da Jibril ko dana dan lokaci ne? Abun bakiciki ne namiji kamarsa ace be san abunda ya dace ba, shikenan saboda be da mahaifiya a raye mahaifinsa ba zai iya zauna da shi ya fahimci rayuwar dansa ba?
Ni kadai ce zan iya canja rayuwar Jibril a yanzu, saboda ni kawai yake saurare ni ce kadai zan matsa tsawa be maida min ba, dole na taimaki rayuwarsa ko dan dana ba ni da wani zabi a yanzu da ya wuce wannan ko na ki ko na so uban Noor ne kuma dole wata rana Noor zai yi rayuwa da Ubansa, idan bashi a tafarki mai kyau taya Noor zai kalleshi?
Tunani kenan sai kuma wata zuciyar ta jefo min tambaya.
‘Yanzu mutumen da ya wulakanta ya nuna baki da muhimmanci a rayuwarsa mutumen da ya kiraki da annoba? Yasa aka kiraki karuwa? Ya ce dan da kike takama da shi ba nasa ba ne? Ya wulakanta mahaifanki ya tozarta ki a idon duniya ya ce ganin bakin maciji ya fi masa ganinki, shi zaki taimaka? Irin wannan mutumen zaki tausayawa? Wanda ya kasa baki taimako daga lokacin da kike bukatarsa ya fifita karuwa akanki?’
“No no ba zan iya ba”
Na furta a fili idanuwana cike da tsanarsa.
“Yaje ya yi ta yin rayuwar da yake ganin zata fidda shi ni babu ruwana a ciki”
Ina rufe bakina yana fitowa daga office, ni kuma na mike tsaye na dauki takardun.
“Naj ina ɗa na?”
Wani wawan kallo na watsa masa.
“Da kuma? Ko cocaine din ta fara bugunka?”
“Ina cikin hayyacina na san abunda na ke ina dana ko yata?”
“Mtssss kana hauka Jibril baka ma san abunda kake fada ba”
Ina yin gaba na ji an fisgoni na fado kirjinsa sai ya rumgume kamkam ya lumshe ido, ina jin yadda zuciyarsa ke mugun bugawa numfashinsa kuma na fita da sauri. Iya karfin da Allah ya bani da kuma dabara ya saka wajen ganin na kwace kaina amman na kasa ko kwakkwaran motsi, saboda karfinsa ya ninka nawa sau saba'in.
“Ka sake ni ko na maka ihu”
“Ko kin yi ihu babu wanda zai zo”
Ya fada idonsa a lumshe yana kara kwamtar da kaina a kirjinsa.
“Kina jin yadda zuciyata take bugawa ko Naj saboda ke”
“Idan baka sake ni ba zan sake zuwa aikin nan ba, daman saboda ka rika min haka ka tirsasani yin aiki a tare da kai ko?”
Ya dora kansa saman kaina.
“Ina ma zamu dawwama a haka”
“Ba zan sake zuwa aikin nan ba”
Ya yi saurin saki na.
“Ina son ki sosai Naj ina miki irin son da wani da namiji be taba miki ba”
“Ni kuma bana son..”
Na kasa karasa saboda hannunsa da yasa ya rufe min baki, sai kuma ya duka kasan guiwoyinsa ya hade hannayensa.
“Dan Allah dan Annabi Naj ki yafe min abunda na yi miki, dan Allah ki manta da komai”
“Na manta da komai saboda ka san ka zalince ni ko? Mugu bakin azzalumi”
“Ki kirani da ko wane irin suna zan karba miki, ki ayyanani a duk kalar mutumen da kike gani zan dauka, ki ci mutunci a gaban kowa zan jure matukar hakan zaisa ki yafe min”
“Ba zai taba sa na yafe maka ba”
“Fada min abunda zan yi ki yafe min Naj, ni kadai na san irin abunda na ke ji a zuciyana, na kan tsani kaina idan a duk lokacin da na tuna abunda na aikata miki, tunaninki ya haddasa min ciwo da damuwa, rashin kulawar nan taki ina jin kamar yana kokarin rabani da rayuwata ne, i will die soon Naj mai yuyuwa a wannan lokacin zaki tausaya min ki zo gaban gawata ki yafe min”
Hawaye yake irin hawayen nan dake nuna tsantsar abunda ke zuciyarsa, ga nadama da damuwa nan ƙarara a fuskarsa.
“Lokaci meeting yana wuce”
Na fada tare da daukar takardun na nufi kofar fita. A ranar meeting hudu muka yi uku a cikin kamfanin daya kuma a wani kamfanin da muka je tare, sai dai sam babu walwala da sakewa a fuskar Jibril da ma yadda yake maganarsa da mu'alama da mutane, dukan abunda zan yi hankalinsa yana kaina, da muka dawo na yi sallah shi kuma ya dora alwala ya fita zuwa sallah a masallacin da ke kamfanin ni kaina ban taba sanin akwai masallaci a kamfanin ba sai yau, bayan na dawo ya cilasta min zuwa cin abincin rana kamar jiya, da muka shigo office ya dauko wasu takardu ya aje min wai na yi typing dinsu a computer shi kuma ya nemi wata kujera ya aje gaban teburina yana kallona har na yi aikin na gama.
Tare da shi muka shiga mota, ya kawoni a inda ya aje jiya sannan ya mika min wata sabuwar laptop, wai da ita zan dinga zuwa office kuma na je gida ta aiki ce sai kuma na bukaci na kwashe duk abunda ke cikin wacan computer ta office na saka a laptop din, ni dai ban ce masa na gode ba balle sai anjima na fito na yi tafiyata.
Ko da na isa gida yamma ta yi lis saboda yau na dade sosai a gurin aikin, na darar da gidanmu cike da mutane suna ta mana murna wai Sakina ta ci gasa an bata gida kuma wanda yasa gasar ya dauki nauyin karatunta sannan ya yi mata kyautar dubu dari biyu da hansin, ita kanta kamar zata hade kanta dan murya.
Jibril kawai zuciyata ke raya min ya saka gasar nan, sai kuma daga baya na soma tunanin Mustapha domin shine a unguwar ya fi kowa sanin inda Sakina take karatu, har dare mutane nata shigo mana, Inna ta siye minti ta yi sadaka, bayan sallah isha'i Bilal ya kirani a waya na ki na daga sai ya aiko min da sako wai yana kofar gida, nan ma ban mayar masa da amsa ba jim kadan sai ga yaro ya shigo wai ana sallama da Nawwara, sai na yi karaf na ce
“Je ka ce ba zata zo ba”
Inna ta saki baki.
“Ba zaki zo ba? Ba kyau wulakanta dan adam fa, Wallahi ki kama kanki, ni bana son yawan zuwan da ake ama miki sallama, wallahi ko aikin nan da kike zuwa hankalina be kwance yake ba, bani da kwanciyar hankali idan ba aure kika yi ba”
“Inna Bilal ne fa”
“To dan me ba zaki je ba?”
“Wai birthday yayi yau shi da Zinatu suka yanka cake din kuma a gurin aikinmu wai har da kirana dan na gani”
“Kishi kike kenan, ashe ana kishin abunda ba a so?”
“Ni ina son shi”
“Kina son shi kike nuna baki son shi? Kina son shi miya hana ki aure shi? Yanzu