Showing 99001 words to 102000 words out of 138998 words

Chapter 34 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

764

na gode da ka yaba”

Sai dan yi murmushi.

“Aiko ya kamata na bada tukuici ko?”

“Ka adana tukuicinka da daddadan kalamanka har sai na fada maka dalilin wannan kwaliyar tawa”

“Akwai wani daliline bayan wanda na gani?”

“Sosai ma, a wancan gani ka yi, wannan kuma ji zaka yi”

Ajiyar zuciya ya sauke yana murmushi.

“Nawancy kina yaudarar zuciyata da yawa, da fushi na zo nan gurin, amman kin shiga kin yi nikaya kin tarwatsa duk wani damuwa da fada da na zo da su”

“Ai daman haka ya kamata ko wace amarya ta kasance gurin angonta, mai wanke danuwarsa ta shimfida farinciki a zuciyarsa”

“Ina ma da gaske Nawancy amaryar Bilal ce da yafi kowa farinciki a duniyar nan”

“Akwai wanda ya isa ya hana abunda Allah ya zo kasanewarsa tun farkon hallitar Nawwara?”

“Babu”

“Ashe ko Nawwara sai ta fi Bilal kasancewa a cikin farinciki daga ranar da aka daura aurenta da angon da ya fi ko wane ango tsada a duniyar nan”

Ya yi murmushi yana kallona tare da lumshe ido.

“Ina son ki sosai Nawancy”

“Kai so na kawai ka ke ni ko kaunar ka na ke”

Ya sauke ajiyar zuciya.

“Kamin ki kaini duniyar da ba zan iya dawowa ba, fadan min dalilinki na yi wannan kwaliyar”

“Kamin na maka albishir mai tsada ya kamata ace ka fada min abunda ya kawo ka nan”

“Yo tun yaushe kika duniyar kwakwalwa kika mantar da ni wanene ni ma, balle abunda ya kawo ni nan kuma”

“Yanzu dai rumtse idonka sai na fada maka albishir din”

“Ai kunnene yake ji ba idanuwa ba”

“Ina gudun kyawawan idanuwan nan naka su ba ni kunya ne”

Sai ya yi dariya ya lumshe idanuwasa.

“Inna ta ce na fada maka, idan ka shirya ka turo magabatanka suje can Baban gida su gana da nawa magabatan”

Da sauri ya bude idanuwansa ya kallini

“Da gaske Nawancy?”

“Na saba maka irin wannan wasan ne?”

Wani ihu ya yi ya daka tsalle ya dire, ni kuma na yo cikin gida da gudu ina dariya. Da na shigo sai na ce da Inna Bilal ya ce zai turo magabatansa amman be saka rana ba.

“Mashallah Allah ina fatar kina sonshi dan karki yi wa kanki zabi irin na baya, kuma ina son ki bawa Allah zabi a cikin lamurranki nima zan taya ki da addua idan aurenki da Bilal alheri Allah yasa ayi, idan kuma ba alheri ba ne Allah ya kawo maslaha”

“Amin Inna, inshallah Alheri ne”

Daga wannan sai fira ta biyo baya Inna na ta nanata min burinta na ganin na yi aure domin shine kwanciyar hankalinta, a daren Bilal ya yi min kira ya fi a kirga ni kuma na ki dagawa, misalin uku da rabi na dare na tashi na yi nafila na Mikawa Allah zabina akan ya zaba min dukan abunda zai fi zama alheri a rayuwata. Washe gari bayan na gama komai na shirya na nufi asibiti zuciyata cike da tunanin yanayin Jidda gabana kuma nata faduwar da ban san daliliba.

Jirbil kawai na tarar a dakin Noor baya nan, na gaisheshi cikin ladabi kamar yadda na saba masa a yanzu. Be amsa min ba sai ya matso kusa da ni yana ta kallona kamin ya risina kasa wanda hakan yasa ni ja da baya.

“Nawwara dan Allah ki yafe min abunda na yi miki na san na yi kuskure amman ki dubi girman Allah ki yafe min”

“A kwanakin nan da muka dauka be isa yasa ka fahimci cewar na yafe maka ba?”

Ya mike tsaye yana kallona.

“Ki kalli cikin kwayar idanuwana ki ce kin yafe min”

Ya fadi hakan ne saboda ya tabbatar da yafiyar tawa, domin yasan babu abunda zan gani a cikin idanuwansa sai tsanarsa da kiyayyarsa, ras na sauke idanuwa cikina nasa zuciya a natse bakina ya furta cewar.

“Na yafe maka Jibril Allah ma ya shaida na yafe maka”

Lumshe ido ya yi sai ga hawaye sun sauko masa, yaja wani dogon numfashi ya sauke, sannan ya bude idanuwansa ya kalleni

“Yanzu za ki iya aure na kenan?”

“Dan na yafe maka ba shi yake nufin zan iya sake zaman aure da kai ba, ni ina da wanda zuciyata take so”

“Wa kike so Nawwara? Wanene wannan wanda ya fini sa'a da dacewa a rayuwa? Wanene wanda be shirya zaman duniya a yanzu ba?”

Na shiru ina kallonsa.

“Mustapha ne ko?”

Kamin na ce wani abu sai wata nurse ta turo kofar dakin ta shigo hannunta rike da na Noor.

“Sir an gama”

“Thank you”

Ya fada yana share hawayensa, sai da ta fice sannan ya nufi Noor ya dauke shi ya rumgume.

“Come here my happiness”

“Momy yanzu kika zo?”

Na daga masa kai sai na karasa gurin gadon na zauna, Jibril kuma ya zauna a kujerar da ke fuskantata yana rumgume da Noor, idanuwansa na ta xika da hawaye tana kallona.
Muna haka aka turo kofar dakin a aka shigo Zinatu ce tare da Rabi sai kuma wani bakon mutun da ban waye fuskarsa ba. Da dan farka ta karaso kusa da mu ta aje ledodin da ke hannunta sannan ya zauna kusa da ni tana kallon Jibril.

“Ashe kana nan”

“Akwai wani gurin da ya kamata na kasancene bayan nan?”

Ya fada yana mikawa mutumen hannunsa su gaisa. Rabi kuma ya zo tana mikawa Noor hannu

“Zo nan dan Daddynsa”

Dariya kawai ya yi mata amman be yarda ya bar jikin Jibril ba, ya labe sosai kamar wani karamin yaro mai shan mama.

“Sir Akwai maganar da ya kamata mu yi”

“Tana da muhimmanci ne sosai?”

“Eh akan abunda kasa ayi ne, kuma Siraj yana waje yana jiranka ya ce a gaishe da Noor”

Zinatu ta mike tsaye ta karbi Noor shi kuma ya tashi ya fice dare da mutumen da kuma Rabi.

“My Son ya jikinka?”

“Na ji sauki Daddy ya ce nan da kwana biyu za a warware hannu”

“Mashallah Allah ya tsare gaba ya kara lafiya”

“Amin”

Ya amsa bakin nan chakoi, sai ta kalleni.

“Kin kusa komawa aiki kenan ko?”

“Inshallah”

Daga haka ban sake cewa wani abu ba, itama bata sake cewa ba, sai ma dauko ledar da ta zo da ita da tayi ta bude ta fiddo chocolate mai shegen tsada ta mikawa Noor. Bayan kamar mintuna talatin sai Rabi ta sake shigowa tana fadin.

“Zinatu Siraj na kiranki wai ki zo zai wuce”

Zinatu ta sauke Noor saman jikinta ta aje shi kasa tare da yi masa kiss.

“Allah ya kara sauki da na”

“Amin na gode”

“Nawwara na wuce”

“Mun gode Zinatu Allah ya bar zumunci”

“Amin”

Bayan ta fice, Rabi ta maida kofar dakin ta rufe ta nufo ni tana fadin.

“Nawwara ina son muyi magana da ke mai muhimmanci”

“Akan me?”

“Akan ke da Noor da Jibril da kuma Siraj abunda ya shafi rayuwarku ne ku duka”

Gabana ya fadi

“Ban gane ba”

“Asirrance na ke son mu yi maganar, amman kamin nan ko kin san cewar Jibril ya kori Bilal a kamfani tun last week? And there's something behind Noor accident...”

Na mike tsaye da sauri.

“When how i don't understand?”

Kamin ta kara cewa wani abu sai ta ga Jibril ya turo kofar dakin ya shigo, sai ta yi saurin juyawa tana dariya.

“Kin jiki Nawwara da wata magana, masu kudi ai suna can inda suke, ni dai na tafi Allah kara lafiya”

Kamar na ce wani abu sai kuma na amsa da.

“Amin na gode”

Tana ficewa, Jibril ya kalleni ya ce.

“Kin san an kawo Mustapha a asibitinmu kuma ba shi da lafiya sosai, yana icu room 14”

“Na sani”

“Mi kike son a masa?”

Na masa wani kallo kamar ban fahimci abunda yake cewa ba. Sai yasa hannunsa aljihu ya ciro karamin hoton Habiba ya mika min. Na karba hannuna na rawa sam na manta da inda na jefarda hoton ma. Ina karba sai ya juya ya fice ya bar nan tsaye da mamaki, ya aka yi yasan abunda Mustapha ya aikata? Ina ya samu hoton Habiba? Me yake nufi da abunda nake son a yi masa, ga kuma maganganun Rabi da suka tsaya min a rai.

Saurin juyawa na yi na fita harabar asibitin ina tambayar inda icu yake, aka fada min sai na doshi gurin da sauri ina duba number din room din har na kai ga mai 14, ina dosar dakin sai Jibril ya fito tare da wasu Nurses, kallona kawai ya yi ya dauke kai ya fice, ni kuma na saki baki jikina a sanyaye ina kallon dakin, Mustapha nake hangowa da ke kwance kamar gawa, Mutanen da ke cikin dakin suna ta rusar kuka, ban san lokacin da nawa hawayen suka fara zuba ba, na juyo da sauri na biyo bayan Jibril hangosa na yi tsaye yana magana da wani likita na doshi inda yake ina hawayena bakina na rawa kafafuwana kuma kamar zan fadi.

Yana hangoni ya yi saurin sallamar mutumen ya shige dakin, ni kuma ina isa na baki kofar office din na fada.

“Me ka masa Jibril? Me ka masa?”

Ya zauna saman kujera yana kallona

“Duk mutumen da ya kashe rai shima kisa ne ya cancanta da shi, daukar fansar yar uwarki na yi miki”

“Be kashe rai ba, fyade kawai ya yi mata miyasa zaka kasheshi mi ya kama?”

“Ba shi kadai zan kashe ba?”

“Mutum nawa zaka kashe?”

“Adadin mutanen da zasu furta ko kuma su nuna soyayyarsu a gareki, kamar Bilal”

Ya fada yana tabe baki, ni kuma na zaro ido naja baya baya har ina kokarin faduwa, sai kuma na juya a firgice na fice daga office din kamar mahaukaciya.


____________________________

Da gaske Jibril ya kashe Mustapha? Ko dai mafarki ne Nawwara take?
Mai Rabi zata fadawa Nawwara mai muhimmaci har haka ne? Mi ta sani akan Siraj da Noor da kuma Nawwara?
I can't wait for the next chapter 😍

KhadeejaCandy ce ✍️
[11/8, 9:37 PM] +234 703 352 5246: *RAI BIYU...♥🖤*

Wattpad @KhadeejaCandy


4⃣8⃣

Har na kawo bakin gate din asibitin kuka na ke ina ta tunanin abun yi, wane irin mutum ne da zai kashe rai saboda cin ma wata bukata tasa ta kanshin kansa? Ko ni da na tsani Mustapha ba zan iya kasheshi ba ko na saka a kasheshi ba, bayan shi kuma ya ce Bilal ne next, dole ne na sanar da police wannan maganar ba zan iya kyalewa ba, wayata na dauko na kira Bilal bugu daya ya dauka muryarsa da walwala da alama yana cikin farinciki.

“Nawancy”

“Kana ina”

“Ina kofar gidanmu”

“Dan Allah ka sameni guiwa station yanzu”

“Lafiya? Kuka kike yi”

“Ka zo yanzu ka ji”

“Okay tau”

Daga haka na kashe wayar na tari achaba na hau domin shi ya fi kusa da station, ko da na isa har ya isa bakin station din yana ta yi min waya, yana ganina ya doso inda na ke yana tambaya dalilin kiransa da na yi.

“Bilal Jibril ya kashe Mustapha kuma ya ce kai ne na biyu”

“What? Nawancy kin san abunda kike fada kuwa”

“Na sani na gani da idona ya kasheshi”

Na fada ina kuka, sai ya matso kusa da ni yana kwantar da hannayensa.

“No listen Jibril is very smart ba zai kashe Mustapha, maybe dai yana miki wasa ne, ko kuma yana son ya yi amfani da wannan damar ne ya cinma wani buri nasa”

“Wallahi da gaske ne, na ga gawar Jibril da kaina”

Na fada ina cigaba da kuka, sai ga wani dan sanda ya zo kusa da mu yana tambayar dalilin zuwanmu gurin.

“Dpo na ke son gani shi yace na same shi nan akan case din mahaifinmu”

“Amman baki da number shi?”

“Ba ni da amman shi yana da tawa number, dan Allah ka fada masa da gaggauwa”

“Okay”

Ya juya ya koma ciki, na yi wannan karyar ne saboda na samu gamin dpo cikin sauki, domin nasan duka wadannan kananan yan sandan ba zasu iya handling case din Jibril ba. Bayan kamar minti biyar sai ga police din ya dawo ya ce mu shiga ciki, sai dai basu bamu damar hakan ba sai da suka binka komai na mu.

Cikin office dinsa muka sameshi yana sanye uniform dinsa na yansanda yana ta rubuce rubuce a takardun da ke gabansa, da hannu ya nuna mana kujerar zama.

“Bismillah”

Na zauna hawaye na ta bin fuskata, sai ya aje rubutun da yake ya fuskance mu.

“Lafiya dai Nawwara?”

“Ba.. Ba.. Ba akan case din Baba na zo ba, na ce haka ne saboda na samu ganinka”

Na fada ina kuka, sai mika hannunsa ya dauko tissue ya bani na share hawayena da majinar da ta zubo min, sai kuma ya mike tsaye ya nufi freezer sa ya bude ya dauko gorar ruwa da kofi ya bulbula min.
Ba musu na dauka na shanye, ya sake zuba min na shanye sai ya karbe kofin ya maida gefe ya zauna yana kallona.

“Relax ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ki a nan”

Na gyada masa kai sannan na sauke ajiyar zuciya wanda hakan ya bani damar soma masa bayani.

“Wani ne yake barazana ga rayuwar Bilal ya ce sai ya kasheshi”

Ya kalli Bilal a kaikaice.

“Miye tsakaninki da Bilal din?”

“Shine wanda zan aura”

“Wacan wanda yake barazana ga rayuwarki fa?”

“Tsohon mijina ne”

Jinginawa ya yi da kujerar yana kallonmu.

“Fada suka yi da har maganar kisa ta shiga ciki”

“Aa kawai dai baya son shi ne, yanzu ya kashe wani kuma ya ce Bilal ne na biyu”

“Dan taadda ne mijin na ki?”

“Aa likita ne, amman yanzu yayi ma wani allura ya mutu”

Ya kalli Bilal

“Kai namiji ne maybe zaka fi yin bayani mai gamsarwa, ko fada ya taba hada ka da mutumen? Ko kuma wani abu ya shiga tsakaminku”

“Gaskiya babu abunda ya taba shigo tsakaninmu”

“Haka kawai yayi maka barazanar kisa?”

“Aa shi besan an yi ba, ni ya fadawa kawai ina son a shiga tsakaninmu da shine domin duk abunda ya samu Bilal shine”

“Okay amman dole ne zamu yi magana da shi, yanzu zan sa a dauki statement dinku, kin san inda zamu samu wacan din?”

“Ee ina da number wayarsa”

“Tau ki bamu sai mu kira”

Daga haka ya dauki telephone dinsa ya kira wani police yana shigowa ya sare masa shi kuma ya nuna mu.

“Kaje ku dauki statement dinsu, kuma ka karbi number a hannunta ka kira mutumen ka ce ana nemansa”

“Yes Sir”

Tare muka fito da police din suka kawo mu reception suka dauko takardar aka saka sunana da na Bilal sannan na soma yi musus bayanin komai, bayan mun gama na basu number Jibril suka kira shi, ko thirty minutes ba a kara ba sai gashi ya iso gurin fuskara babu annuri. Sai aka sake maida mu gurin dpo tare da statement din da aka dauka. Muna shiga Jibril ya mika masa hannu suka gaisa ya zauna saman kujera ba tare da ya jira an masa izinin zaman ba, Bilal ya zauna a kujerar da ke fuskantar ta Jibril, ni kuma na zauna a kujerar da ke bayan Bilal.

“Dpo kun ce kuna bukatar ganina”

“Yes Nawwara ta kawo kararka akan cewar kana barazana ga rayuwar mijin da zata aura Bilal”

Sai ya juyo ya kalli Bilal kamar daman can be san da shi a gurin ba sai yanzu, sai kuma ya maida dubansa gurin dpo.

“Mi nayi?”

“Ta ce ka ce sai ka kashe Bilal, kuma ka kashe wani kamin shi ka ce shine next”

“Yanzu dpo tsakanin da Allah na maka kama da mai kisa?”

“Ai abun ba daga kama ba ne”

“Idan ina son kashe Bilal ba sai na fadawa Nawwara ba, kuma taya namiji mai iyali kamar ni xai bata lokacinsa gurin wannan wasan kamar wani karamin yaro? Ni ban kawo kararshi ba shi zai kawo karata? Mutumen da kake gani yana barazana ga rayuwata da ta iyalina, my friend has told me Bilal din nan yana da hannu a kokari kashe min yaro, amman ban masa komai ba saboda ban tabbatar da gaskiyar ba na fi son na kama shi red handle, wannan yasa na koreshi daga kamfanina, a kamfanina yake aiki amman babu irin cin fuskar da baya min da matar nan saboda ya san ina sonta”

Ya juyo ya kalli Bilal.

“Saboda na koreka daga aiki shiyasa kake kokarin bata min sunan asibiti ko? Kake kokarin saka Nawwara against me ko? Idan mun gama da wannan case din zan shigar da nawa case din akanka, dan zaka iyayi min komai wajen ganin ka bata min suna ko aikina”

“Kana ganin xaka iya taka kowa saboda kana da kudi ko Jibril? Zuciyarka tana yaudararka akan ka aikata dukan abunda kake so saboda kana da kudi ko? Har yanzu zuciyarka karya take fada maka, ka kasa fahimtar cewar ba komai kudi suke siya ba, kana yaudarar kanka da yawa Jibril”

Cewar Bilal cikin fushi. Sai Jibril yasa dariya ya kalli dpo ya ce

“Kaga abunda na ke fada maka ko? Babu komai a zuciyarsa sai tsanata da neman hanyar da zai lalata min suna”

Ni kuma na mike tsaye ina fadin.

“Ba bata maka suna zai yi ba, gaskiya ya fada, kuma ni ka fadawa cewar sai ka kashe Bilal kuma yanzu haka ka kashe Mustapha”

Dpo ya daga mana hannu.

“Ba fada muka kiraku ku mana a nan ba”

“Kamin nan dan Allah dpo ina son ka bani yaranka suje su duba wanda ta ke cewa na kashe”

Mun dade a office din Bilal da Jibril suna ta musayar yawu, sannan saka rubuta yarjejeniyar cewar duk abunda ya samu Bilal Jibril ya saka hannu akan cewar ya yarda aka kira Siraj ya yi sheida Bilal kuma aka kira mahaifinsa. Daga bisani muka dunguma gaba daya muka nufi asibitin. Abun mamaki muna shiga dakin da Mustapha yake sai muka same shi zaune yana cin abinci kamar ba shi na ga a mace ba dazu. Yana ganina ya rika kokarin saukowa saman gadon sai mahaifiyarsa ta katsa min tsara.

“Ke kan kin shiga uku Nawwara, ba zaki bar dan mu ya huta ba, wannan wace irin rayuwa ce saboda ke dan mu yake kwance nan yanzu kuma sai ki biyoshi har nan asibiti akan wane dalili”

Juyawa kawai yan sanda suka yi suka koma ni kuma na sulale kasa a gurin ba dan na suma ba sai dan kafafuwana da suka min sanyi, ga hawayen da suka soma nin zuba babu kakkautawa.

“Haba Mom miyasa kike min haka ne? Wallahi da ki yi ma Nawwara fada kara ki yi min”

Tasowa ta yi ta karaso inda na ke.

“Ban san kaddara ba Nawwara, duk na rasa dana saboda ke ki fara kirga irin asarar da zata sameki kema”

“Tir da mace dattijowa irin ki ta tsaya tana fadin bata yarda da kaddaraba, ke an fada miki Nawwara son Mustapha take ne?”

Cewar Bilal yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login