Showing 93001 words to 96000 words out of 138998 words

Chapter 32 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

763



“Ya kamata ku tafi yanzu, amman kai yaron nan i warning you karka sake shiga sabgar Nawwara ko ban fada maka ba”

Daga Nawwara har Mustapha da Jidda kallonsa suke.

“Waye wannan daman ka san shi ne?”

Jidda ta tambaya tana kallon Mustapha, sai Jibril ya yi cikinta kamar zai dake ta.

“Babu ruwanki a ciki”

Matsawa baya Jidda ta yi ganin yadda temper dinsa take, sai Mustapha ya taso daga inda yake zaune kusa da Noor yana murmushi ya karaso daf da Jibril ya soma gyara masa kwalar rigarsa.

“Ka kwantar da hankalinka Man, macece fa ba namiji ba kasan namijin da ya amsa sunansa namiji baya taba dukan mace, ko da yake kai ragon namiji ne, shiyasa kake duka kuma kake cin zarafin yarinyar nan marainiyar Allah, anya babu kai a cikin kashe mata mahaifi kuwa? Saboda na ga ka tsawwalla rayuwarsu ne da yawa ka siye gidansu... oops sorry na manta she's your ex...- ”

Ya karashe maganar yana murmushi. Jibril ya daga hannu cike da hasala zai naushi bakinsa sai Mustapha ya rike hannunsa cikin zafin nama ya kai masa na shi naushin a baki har sai da Jibril ya yi baya baya ya rike bakin.

“1-1”

Mustapha ya fada yana murmushin keta. Sai Nawwara ta katsa musu tsawa.

“Miye haka? Ya zaku rika yin abu kamar kananan yara?”

Murmushi Jibril ya yi ya kallon Noor da duk tsoro ya gama mamayeshi ya ce

“Wasa ne fa kawai karki daga hankalinki, amman ki fada masa karya sake zuwa kusa da yaro na”

“Ba dan ka na zo nan ba dan Nawwara ne, duk kuma abunda ya shafi Nawwara dole ne ya shafe ni”

Jibril be kara ce masa komai ba, domin yasan wani furuci na fitowa a bakinsa ba mai dadi ba ne, kuma baya son ya yi abunda be kamata ba a gaban dansa, sai kawai ya karasa kusa da Noor ya zauna yana shafashi tare da fiddo wayarsa ya kunna masa game.

“Mu zamu koma, daman na zo ne kawai ganin Noor Allah ya tsare gaba”

“Amin”

Cewar Nawwara, sai Jidda ta daga mata hannu.

“Zamu yi waya”

“Ok thanks”

Suna fita Mustapha ya fara tambayar Jidda labarin Jibril, sai dai bata fada masa komai ba saboda tana tunanin sirrinsu ne ita da Nawwara, but itama tana mamakin yadda aka yi Nawwara ta hakuru har haka ta bari ya zo ganin Noor.

“Amman shi Nawwara take so ko?”

Mustapha ya tambaya yana driving, sai Jidda ta kalleshi.

“Bata son shi, ni dai iya sanina Nawwara Bilal take so”

Kamar zai sake cewa wani abu sai kuma ya yi shiru, sai dai ransa yau yana cike da farinciki saboda abunda ya yi ma Jibril. A bakin kofar gidansu Jidda ya sauketa sannan ya juyo ya dawo gida.

Tun a yanayin shigowarsa ya tabbatarwa da Momynsa yana cikin farinciki, Daddy sa ma ya lura da hakan kasancewar dukansu suna zaune falo ne har su Ikram da Zarah suna kallo harin da aka kai Iraq a channel din Al Jazeera.

“Dad Mom barka da dare”

Sai da suka amsa masa sannan ya zauna saman cushion yana kallon tv kamar yadda suma suke kallo, sai dai ko kadan hakalinsa baya gurin yana can gurin Jibril tunanin halin da Jibril zai kasance kawai yake yana murmushin da be san ya fito masa ba.

“Son lafiya kake wannan far'ar?”

Ya kalleta kamar be san ya yi ba.

“Ba komai, but Mom Dad ya kamata ce kunje ganin yaron Nawwara ya samu accident”

“What...?”

Dadynsa ya fada.

“Mu zaka fadawa muje mu duba yaron Nawwara? Hajiya baki fada masa ya fita harkar yarinyar nan ba? Daman yana nan akan bakansa?”

Momy ta yi saurin dagawa Dadyn hannu.

“Komai da sannu ake binsa kasan halin Mustapha”

“Babu ruwana da wani halinsa, ka var ganin kai kadai na haifa zan iya shafe labarinka a doron kasa matukar ka ce zaka auri yarinyar, ka dauki kanka a matsayin matacce matukar ka tsaya kai da fata akan yarinyar nan”

Mustapha da zuciyarsa ke boiling gumi ya zubo masa ya bude bakinsa da ke rawa ya ce

“Daddy ina son yarinyar nan...”

“Baka san so ba Mustapha, taya zaka so mace da ta auri namiji biyu kuma ta haihu? Kuma in banda haukarka macen da kayi ma kanwarta fyade zaka ce kana sonta kuma da aure? Kana tunanin zata aureka ne? Kana batawa kanka lokacin ne kawai, kuma na fada maka karna sake jin maganar yarinyar nan a cikin gidan nan, ka nemo yar kowa zan aura maka amman ban da ita”

Yana gama fadar hakan ya mike tsaye ya kabe babbar rigarsa cikin bachin rai ya fice, sai Momy ta matso kusa da Mustapha tana kokarin yi masa bayani

“Look son.. ”

“No Mom ke kika ce min Dady ya yarda da maganar yarinyar nan, ashe ba da gaske ba ne? Miyasa ba zaku so abunda na ke so ba? Miyasa kuka gagara ganewa?”

Magana yake kamar ba shiba har numfashinshi na hawa wani kan wani, kamin ta kara cewa wani abu ya tashi rai a bace ya bar mata falon.



NAWWARA POV.

Ba jidadin zuwan Mustapha ba domin ban fiye son yana shige min ba, bana son wata alaka tana shiga tsakanin ni da shi, dan ban yarda mutum ya cuceni kuma ya dawo ya ce zai rabe ni ba Jibrrma dan babu yadda zan yi ne.
Bayan fitar Mustapha da mintuna talatin na kalli Jibril fuska a daure na ce.

“Ina son na kwanta dare na yi fa? Kuma ka san Inna tana waje kai take jiran ka fita”

“Ba zan je ko ina ba, a nan zan kwana tare da da na”

Ban yi mamakin furucinsa saboda cocaine yake sha mahaukacin mutum komai zai iya ai, musamman idan ya samu guri in ban da rainin hankali daga kawai na bashi damar ganin Noor sai kuma ya soma yi min katsalandan a lamurrana.
Tashi ya yi ya fita hakan yasa na bishi baya saboda na samu damar fada masa maganganun da ke bakina, ina fita na samshi bakin kofa a ashe ni yake jira.

“Daga Bilal har wannan dan iskan yaron bana son su sake zuwa gurin da na”

“Baka da damar da zaka shardanta min wanda zai so gurin da na da wanda ba zai zo ba, kai yanzu ko kunya baka ji ka kira Noor da danka? Har kana ikirarin kar wani ya zo dubashi?”

“Yes da na ne, alakar da ke tsakaninku daban babu ruwana a ciki”

“Ni na haifi yarona a hannuna ya girma baka da wannan hujjar Jibril, kuma ko zaka wulakanta kowa ban da Bilal saboda ya taka muhimmiyar rawa a rayuwarta ni da dana, shi Noor ya sani a matsayin Uncle dinsa ba kai ba, da kuma ba naka ba ne nawa ne”

“Ko tau zamu gani”

Na watsa masa harara, ina kokarin juyawa na koma cikin dakin sai ya fisgoni da karfi ya dawo da ni

“Ban yarda ki kwana da shi ba, Inna zata kwana da shi i don't trust you”

Dariya na farayi saboda abun ya bani dariya sosai.

“I'm laughing it's funny very funny”

“Ba wasa nake miki ba Inna zata kwana da shi ba ke ba, idan ba haka ba, ni zan kwana da shi”

“Ban ga dalilin kwana tare da dan da ka kira da shege ba? Kai baka ma jin kunyar yanzu ka kira shi da danka?”

Hannu ya daga kamar zai dakeni sai kuma ya juya baya ya dafe kansa da hannu daya.

“Na dake ni mana, ai ka saba cin zarafina ko? Ka saba yi min wulakanci a gaban kowa, na yi min cin mutumcin da ya fi ko wanne ai ba ka hada hoto da na wani ba? Ka fadawa iyayena cewar ni karuwa ce..”

“Enough...!”

Ya fada a tsawa ce har sai da hankalin wanda duk wajen dakin ya dawo kanmu, wadanda suke cikin daki kuma suka fito waje, sai dai hakan be sashi fasa fadan abunda zai fada ba.

“Ya isa haka Nawwara ya isa haka, wace irin zuciya ce dake haka? Ke kan wace irin mace ce me ke damunki miya ke cikin kanka? Miyasa kika zabi nanata maganganun nan a ko yaushe ne? Kin san abunda yake raina? Kinsan bakinciki da yake raina? Ban isa na wuce wannan kaddarar ba shiyasa na aikata but abunda kike yi babu tausayi a ciki Nawwara, am lemme tell you abunda kike ba burgewa kike ba kokarin kashe rai kike, kokarin rusa wata rayuwar kike kuma babu abunda zai sa na canja daga manufata”

Yana gama fadar hakan yaja hannun Noor ta da fito waje suka koma cikin dakin, Inna hango Inna take na rufa masa baya rai na a bace. Noor na ganina ya yi saurin sakin Jibril ya dawo guna cike da tsoro, dan Noor ya tsani ganin ana fada.

“Da na ni ya sani ba kai ba, karka sake shiga rayuwarsa”

“Dole na shiga rayuwaraa saboda ni ne asalin ubansa”

“Yes ubansa ne kai na gaji da boyewa”

Na juyar da Noor ina nuna masa Jibril.

“Ka ga wacan? Ba Uncle din ka ba ne shine asalin ubanka Baba Faruk ba babanka ba ne rika ka kawai ya yi, wacan azzalumin ne mahaifinka, shine wanda ya ce kai ba dansa ba ne, da aka haifeka be yanka maka rago ba, kuma be san zafinka ba...”

Ban karasa na naji an dago ni an sauke min kyakyawan mari har biyu a fuska, wanda ya haddasa min daukewar wutar cikin kaina tare da ganin wadansu kanana taurari..



___________________________________

Ku yi hakuri da wannan guntun page din 🙏

Mutane da suke cewa kar Nawwara ta yafewa Jibril sai ta musguna masa kuma su ke cewa Nawwara ta cika tsauri da yawa wai zuciya kamar ta kafiran farko 😂

Ni dai nawa ido 👁👁
[11/8, 9:37 PM] +234 703 352 5246: *RAI BIYU...♥🖤*

Wattpad @KhadeejaCandy


4⃣6⃣

Zafin marin ya haddasa min ganin duhu a idanuwana, sai na kyabta idon sau biyar sannan na ga Inna dake tsaye tana hararata, Noor kuma ya fashe da kuka ya rike min kafafu da dayan hannunsa. Hawayene suka soma zuba a idanuwana ina dafe da kuncina, sai na juyo na kalli Jibril da shi ma idanuwansa ke cike da kwalla, juyawa ya yi ya bar dakin ba tare da ya ce komai ba, sai da yaja kofar dakin sannan Inna ta soma fadamin maganganu marar dadi.

“Ina miki kallon mai hankali ashe baki da hankali, abunda kika aikata a yanzu ya fi abunda Jibril ya yi ma Noor shekarun da suka wuce, miye abun burgewa a cikin fadar irin wannan maganar a gaban idon dansa? Wane irin kallo kike son dan sa ya masa? Kina tunanin burgeshi zaki yi? Ki haddasawa danki tsanar ubansa da kanki? Idan ke baki son shi karki shiga tsakanin uba da da, Wallahi da Noor zai girma a cikin talaucin da ya fi wannan kuma daga baya ya hadu da mahaifinsa dole ne sai ya masa biyayya saboda haka Allah ya ce.

Wace irin zuciya ce da ke Nawwara, ke baki ma Allah laifi ya yafe miki ne? Wa kika fi? Idan ma ba zaki yafe masa ba ai ba sai kin shiga tsakaninsa da dansa, Wannan ba halinki ba ne Nawwara kuma ba halina ba ne ba kuma halin Babanki ba ne, ban san inda kika dauko wannan bakar zuciyar ba”

Tun da ta soma maganar na lumshe ido hawaye na cigaba da min zuba, sai na ji ta fisge Noor daga rikon da ya yi min ina bude ido ta nuna min hanyar fita.

“Fita ki bar dakin nan”

Na bude baki zan yi magana ta daga min hannu.

“Bana son jin wata magana daga bakinki ki fice kawai kije gida”

Juyawa na yi kafafuna da nauyi zuciyata kuma da rauni na fito daga dakin ina share hawayena. Kowa kallona yake ni kuma na ki na kalli kowa na fito ina wata tafiya kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki na nufi bakin gate din asibitin.
Miyasa kowa ya kasa fahimtata? Miyasa ni kadai na ke jin abunda na ke ji babu mai ji min zafi? Ni kadai na san irin wulakancin da na fuskanta a gidan Jibril amman yau Inna har ta tana marina saboda shi? Zama da mutane da kalubale shi yake canjawa mutum rayuwa Inna ta kasa fahimtar hakan.

Har na isa gida kuka nake, mai Napep din har tambaya ya yi wai ko an yi min mutuwa ne nidai ban amsa shi ba, da hawayen fuskata na shiga gida Sakina da Jamila suna zaune waje suna shan iskar hadari da ke kadawa, yanayin shogowata yasa Sakina ta taso ta sauri ta tari ne sai ta haska fuskata.

“Lafiya Anti Nawwara? Ko Noor ya mutu ne?”

Na girgiza mata kai alamar a'a, ina kallon yanayinta da ya yi min kama da na Habiba, banbancinsu da Habiba ce rumgumeni zata yi ta fashe da kuka ko da kuwa bata san abunda na ke wa kuka ba.

“Anti Nawwara miya faru?”

Ta tambaya tana jijjigani zuciyarta cike da fargabar abunda ya saka ni kuka.

“Na rasa komai Sakina, na rasa karatuna wanda shine gimshiken rayuwata saboda Jibril, na rasa mahaifina mai fahimtar kukana, na rasa yar'uwar da ke goyon bayana, yanzu kuma zan rasa Noor Inna kuma tana goyon bayan Jibril, ni kan miya ragemin a duniyar nan? Kowa baya fahimtata, babu mai jin yarena, ni kadai na ke kukana, damuwata ni kadai ta dama, ni kadai na ke jin zafina, duniya ta juya min baya ta kona min komai na farinciki, duk abunda na taba zafi yake min, mai amfanin kuma ta mayarda shi toka da na taba sai dai ya bi iska, na kasa gane bayana balle na fuskancin gaba, babu ranar tsayuwar hawayena”

Ta rika hannuna tana kuka kamar yadda Habiba take min.

“Allah yana tare da ke Anti Nawwara shi zai miki maganin komai”

Na gyada kaina alamar gamsu har na saukarda nauyayyen ajiyar zuciya. Sannan na share hawayena na nufi dakinmu.

“Habiba”

Ina shiga na ambaci sunanta kamar tana jina, sai kuma na kwanta saman katifa ina hawaye, wayar da ke hannuna ta yi kara alamar sako, ina dubawa na ga number Jibril.

_I'm so Sorry Nawwara i'm sorry_

Haka ya rubuta a sakon, wai na yi wurgi da wayar na kara fashewa da kuka. A ranar kwana na yi ina kaiwa Allah kukana saboda bachi ya yi kaura daga idona. Na mikawa Allah lamurana, sannan na bar masa zabi akan dukan abunda zai fi zama alheri a rayuwata, a ranar na roka idan ma mutuwa ce ta fi alheri a gareni Allah ya matso min da ita, idan kuma ba iyakar wahalata kenan ba, Allah ya bani zuciyar da zan iya dauka, saboda shi ya tsara min komai.

Washe gari Inna bata dawo ba sai tara da rabi, ban ga annuri a fuskarta ba wanda hakan ke nuna har yanxu bata huce ba kenan, ban kuma ji ta ce na shirya na je ba, daman ni na ke kwana da shi sannan ita kuma da rana taje ni sai na dawo na yi wanka na shirya sannan na koma.
A daki na sameta na durkusa kasa na rike kafafunta ina kukan da ni kadai nasan zafin fitar hawayena

“Inna ki dubi girma Allah ki yafe min, Wallahi duk kika yi fushi da ni Allah ma fushi zai yi da ni, ke kadai kika rage min a duniyar nan, ba ni da wani gata sai na Ubangiji da yayi min ta hanyarki, zan iya jure komai amman ban da fushinki da rashinki babu dan da zaiyi albarka matukar uwarshi tana fushi da shi, mai yawan neman yafiyar mahaifiyarsa da mahaliccinsa kuma dan gata ne har a gurin Allah, kuma ba zai taba tabewa ba, yarda Allah tana tare da yardar iyaye, idan suka yarda da kai to Allah ma ya yarda da kai, ki taimaki rayuwa kada na zama daya daga cikin masu tabewa, kar soyyayyar wami yasa ki yi fushi da yarki”

Zaunawa ta yi bakin gadon tana kallona fuskarta dauke da damuwa.

“Ba zan taba fushi da ke ba, domin na san illar fushin uwa ga yayanta, na mareki ne kuma na daure miki fuska ne saboda ki gane abunda kika aikata babba ne, na san zuciyarki zata zargeni da cewar ina son Jibril fiye da ke, ba saboda kudin Jibril yasa na yi miki haka ba, da kudinsa na ke kwadayi da na cilasta miki komawa gidansa ko kuma kulla wata alaka da shi, ba wannan na ke dubi ba Nawwara, rayuwar dan ki ta nan gaba nake hangowa da kuma taki rayuwar, wata rana zaki gane gaskiya nake fada miki wata kila a lokacin bana raye, amman za ki gasgatani, ba zan taba cilasta miki gurin auren Jibril daman tun farko bamu cilasta miki ba, amman na san ko da mahaifinki yana raye kwatankwacin abunda na aikata shi zai aikata a gareki, ba zan taba fushi da ke ba”

Na kwantar da kaina saman cinyoyinta wata kalar rahama ta uwa tana shiga cikina.

“Na gode Inna, na miki alkawari ba zan sake yin abunda zai sa ki fushi ba, ko da kuwa abun nan baya min dadi”

“Allah ya sauwake miki wannan rayuwa ya baki wanda zuciyarki take muradi wanda zai share miki kukanki kuma wanda za ki more hakurin da kika yi ta hanyarsa”

“Amin”

Sakina ta shigo tana tambayar jikin Noor, sai Inna ta amsa mata da

“Ya ji sauki, yanzu wanka zan yi na koma”

“Bari na shirya na je”

Na fada ina kokarin tashi tsaye, sai Inna ta rike min hannu.

“Aa ba sai kin je ba, ki hutar da kanki daga yau zuwa gobe”

“Saboda mai?”

“Saboda ki samu sukuni a zuciyarki, kuma ki shirya amsa tambayoyin da Noor zai miki, domin yana ta min na ce masa ban sani ba ke kadai kika sani, dan haka yana nan yana jiranki, kuma Jibril yasa an canja mana wata asibitin tun jiya da dare an kaimu wata”

“Tau Inna”

Na amsa ba dan raina ya so ba, tabbas Jibril na daf da rabani da dan na ni kadai na sha zafin daukar cikinsa na raineshi kuma na haifi abuna saboda kawai shi yana da dukiya.




JIBRIL POV.

Shiru ya yi ya rasa abunda zai cewa Abbah, zuwa can ya sauke ajiyar zuciya ya ce

“Abbah sam na manta da ranar ma sai yanzu”

“This is rubbish kasan hasarar kwangila irin wannan tana janyo a fara raina mana kamfani?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login