Showing 78001 words to 81000 words out of 138998 words
da kai”
“Ba dan haka ba ne Nawwara, saboda na samu kusanci da ke, ina sonki sosai Nawwara”
“Ni kuma bana son ka, bana kaunarka Jibril”
“Na sani”
Ya fada yana hade maganarta ciki da dacin rai. Zaunawa ta yi shi kuma ya mike tsaye na koma office dinsa, sam be gamsu ba shi da tsakaninsa da Nawwara ba, tabbas ya bar ta da ciki kuma ya san ba zata iya zubar da cikin ba.
‘Ta haife shi, idan har babu haihuwa tsakamina da ita mi zai sa ta yi wannan maganar?’
Shine abunda zuciyarsa take ta raya masa, wayarsa ya dauka ya kira Siraj bugu biyu Siraj ya yi picking.
“Siraj ina son kasa a bincika min duk wani abu da ya shafi Nawwara, akwai da a tsakanina da ita Siraj kasa a abincika min”
“Okay”
Daga haka ya kashe wayar ya kira Abbah, sai da ta dade tana ringing sannan ya dauka yana kiran sunansa.
“Hello”
“Jibril”
“Abbah ina wuni”
“Lafiya kalau ya aiki?”
“Al-hamdilillah, Abbah akwai da tsakanina da Nawwara”
“Waya fada maka?”
“Ita ta yi subul da baka”
“Kaje gidansu ko? Bana fada maka karka je ba”
“Ban je ba, Abbah a nan kamfanin take aiki”
“How when?”
Ya kwashe komai ya fada ma Abbah amman be fada masa zance ya cilas mata aiki a tare da shi ba. Abbah ya yi shiru kamar mai tunanin abunda zai ce.
“Abbah we're meant to be”
“Kana son ta ka saketa? Bana son ka zama cikin irin mazan nan da ake fada Jibril ni yanzu ko wani aure ban yarda ka kara yi ba sai ka gane kuskurenka”
“Wallahi Allah Abbah na canja zan zauna da Nawwara zama na tsakani da Allah ba zan taba sakinta ba, Abbah ita kadai ce take so na tsakani da Allah”
“No ba yanzu, kuma na fada maka karka kuskura taka kafarka gidan nan”
“Tau Abbah ba zan yi ba, amman da Mahaifiyata tana da rai da ta roka min kai ka amince, rashinta ne yasa na rasa komai, ba ni da mata ba ni da ɗa sai kai kadai kai kuma ka kasa fahimta ta”
Yana fadar haka ya kashe wayar ya aje saman table, sai ya dora hannayensa saman table din ya dafe kansa ya dinga rusar kuka kamar karamin yaro.
Kuka yake sosai kuka ina zai saka kanshi, kuka neman mafita, be san mahaifiyarsa ba domin be tashi tare da ita ba, amman yana jin zafin rashinta kamar yanzu ta mutu ta barshi, ji yake ina ma tana raye da yanzu ta roka masa Nawwara ta yafe masa, ta shiga cikin lamarinsa ta gyara masa komai, be taba jin zafin rashin mahaifiya ba kamar yau.
Hannunsa yasa ya janyo aljihun table din da take zaune ya dauko hoton wata matashiyar mata mai kama da shi yana ta kallonta yana kuka kamar mace.
Kuka ya yi sosai har sai da ya soma jin kamar jiri yana dibarsa sannan ya tashi ya shiga bathroom ya wanke fuska ya dawo ya dauki ruwan freezer ya sha, sai ya dora gorar saman freezer ya nufi kofar fita.
Ko da ya fito Nawwara na zaune tana duba abubuwan da suke cikin computer, ya samu thirty seconds yana kallonta mugun burgeshi take gani yake a duk duniya babu wata mace da ta kaita daraja da kima da kuma kyau, ji ya yi kamar yaje ya rumgume kamkam a kirji, sai dai yasan ba shi da wannan damar. Karasa ya yi inda take yana kallonta da manyan idanuwansa masu kamar madara kamar zai cinyeta.
“Lokacin cin abinci ya yi, a nan zaki ci ko restaurant zamu je?”
“Ka ce min idan uku ta yi zan iya zuwa gida idan har babu aiki da yawa, kuma na ga yanzu uku sauran kwata”
Ta fada ba tare da ta kalleshi ba dan gaba daya ta tattara hankalinta ya maida kan computer.
“Ee amman a ka'ida karfe biyu da rabi zuwa uku ma'aikata suke zuwa cin abincin rana, taso muje restaurant”
Mike ta yi tsaye yana gaba tana biye har suka sauko kasa gaba daya, tare suke daga kafa kuma su aje tare har suka isa restaurant din dake cikin kamfanin, wani abun da ya bawa Nawwara mamaki suna shiga sai duk wanda ke gurin ya tashi ya fita, aka barsu su kadai daga ita sai shi. Karasa ya yi can guri wani teble wanda shi kadai yake zama akansa ya zauna ita ma ta zauna a kujerar dake fuskantar tasa.
Waiter ne ya zo da sauri yana tambayar abunda za a kawo musu.
“Fried rice and chicken soup”
“And drink?”
“Fanta”
Ya juyo gurin Jibril.
“And you Sir”
A hankali ya juyo ya kalleshi ba dan yasan a abunda yake tambaya ba sai a lokacin ya kula da shi domin gaba daya hankalinsa yana gurin Nawwara.
“And you Sir”
Ya sake maimatawa ganin kamar be ji abunda ya ce ba.
“Just water”
Nawwara ta masa wani kallo
“Ni ladai zan ci abincin kenan?”
“No”
Ya yi saurin amsa mata sannan ya sake kallon mutumen ya ce
“White rice and pepper soup”
“Drink?”
“Lemun juice”
“Okay”
Ya juya da sauri ya koma inda ya fito. Cikin yan seconds sai ga abincin an kawo musu, Nawwara ce ta fara dan ta nuna masa ita fa cin abincin kawai ya kawota ba komai ba, shi kan kasa taba abincin ya yi ya tsura mata ido kamar mai kirga lomomin da take, zuwa can ta dago ta kalleshi, sai ya yi saurin daukar spoon ya soma wasa da abinci dan har ga Allah baya jin cin abincin, kawai saboda ita ta samu ta ci ne yasa shi zuwa ko ba komai hakan zai kara masa kusanci da ita, yadda take cin abinci mugun burgeshi take ya tattara hankalinsa gaba daya ya mika mata, har ta gama cin abinci be yi ko da loma daya ba.
Wani abun da ya ba waiters din mamaki biya bill din abunda be taba yi ba, idan ba ya ci abinci a guri sai dai pa dinsa ya biya ko da kuwa shi da wani suka ci, amman yau shi ya biya da kansa sannan suka fita.
A lifter ma kallota yake ta yi zuciyarsa na mugun fisgarshi kamar zata fasa kirjinsa ta fito.
“Can i hug you?”
Ta juyo da sauri ta kalleshi kamar yadda yake kallonta, idanuwansa sun yi fari kal har wani ruwa ya kwanta a ciki.
“Baka da hankali Jibril, ka rumgume ni muharramarka ce? Ko dai ka dauka kamar Aisha na ke ne? Gaskiya kana bukatar komawa makaranta ka fahimci addini sosai”
“Am sorry”
Ya furta yana dauke idonsa daga kallonta so zai samu sauki zuciya, tare da danke hannunsa ya matse sosai.
Suna shiga Office ya wuce Office dinsa ya zauna saman kujera ya dora hannunsa saman goshinsa ya rufe ido yana sauraren bugun zuciyarsa.
Bayan an mintuna Nawwara ta shigo Office din rike da jakarta.
“Ni zan wuce”
Bude ido ya yi ya kalleta sai ya dauki wayarsa ya kira direbansa, yana yin picking.
“Get ready”
Yana fadar haka ya kashe wayar, da kansa ya dauki akwatinsa ya saka laptop dinsa da tardunsa sannan ya mika mata jikar.
“Aje saman teble”
Sai da ya aje sannan ta dauka suka.
“Ni fa gida zanje fa naga garin hadari ma ya hadu”
“Na sani a ka'idar kamfanin nan as you are my pa dole ni zan saukeki gida ko kuma direban kamfanin nan”
Ya yi tunanin zata musa masa ne, sai dai shi ba ya yi ba ne dan kawai ya kara kusanci da ita, haka dokar kamfanin take.
Tare suka fito duk mai son kallonsu sai idan sun bada baya sannan ake daga ido a kallesu domin sun san abunda Jibril ya fi tsana shine kallo. Ko da suka fito daga cikin kamfanin har an fara yayyafi motar da Jibril zai shiga kuma tana fake daidai bakin kamfanin, direban na ganinsa ya bude masa gidan baya da sauri yana kara masa umbrella, shi kuma sai ya zagaya ta wacan bangaren ya budewa Nawwara dan baya son ta shiga gaba, abunda ya bawa direban mamaki, ba tare da tunani komai ba ta shiga ta zauna, sai ya maida kofar ya rufe sannan ya zagayo ya shiga direban ya rufe masa, sai ta dora akwatin a tsakiyarsu ta maida hankalinta gurin gilashin motar tana kallon yadda ruwan sama ya soma sauka da karfi.
“Guiwa locos”
Ya fada yana kallonta, sai direban ya fisgi motar kamar ba ruwa sama ake ba, har aka shiga cikin unguwarsu bata juyo ta kalli inda Jibril yake ba, shi kuma idonsa na kanta, a hankali ya kai hannu zai taba hamnunta sai a ya yi dai dai da juyowarta tana fadawa direban inda zai aje ta.
Hakan yasa shi saurin janye hannunsa ya danke ya maida kallonsa gurin gidajen da suke unguwar da yadda mutanen suka fake saboda ruwa.
“Ya isa”
Direban na tsayawa ta bude motar zata fita sai ya yi karaf ya ce
“Akwai ruwa sosai ki dan jira a rage”
“A'a”
“Tahir kara mata lema”
“A'a”
Haka ta bude motar ta saka kafafunta cikin cabon da ke gurin tana tafiya ruwa na dukanta, sai da ya daina hangota sannan ya bude motar ya fita ya zagayo gefen da ta fito yasa hannunsa ya kwashi kasar da ta taka wacce ta fitar da sawon kafarta ya danke a hannunsa sannan ya koma cikin motar.
“Gida”
Kai tsaye direban ya nufi Sama road da shi, a hanyar ta tafiya ce ya fiddo wayarsa ya jira Rabi.
“Zan aiko miki da kudi duk abunda ya kamata ki siye, sai ki ka a addiren da zan turo miki yanzu amman sai kin tambaya saboda ban ga ainahin gidan ba”
Daga haka ya kashe wayar, har suka isa kasar na jinke a hannunsa ji yake kamar Nawwara ce ya rike, suna isa ya fita motar direban na tara masa lemar ya daga masa hannu alamar ya bari.
Falonsa ya shiga da hannu daya ya cire kayan jikinsa faffadan kirjinsa ya bayyana muscle din jikinsa duk suka fito real namiji, sai ga karensa ya zo da gudu yana kada masa bindi, shi kuma be kula shi ba ya nufi wata kofar ya bude ya shiga harabar gidan dake can ciki, kwantawa ya yi saman tile din ya shafa kasar a kirjinsa ya ware hannayensa ya lumshe ido ruwan saman na dukansa.
NAWWARA POV.
Sai da na tabbatar ba zasu hango ni sannan na hada da gudu ina ta tunanin subul da bakan da na yi, da yanzu ya gane ya zanyi kenan? Gaskiya ina da yauta sosai ni mi ya kaini wannan maganar ma. Kamin na isa gida komai nawa ya jike saboda ruwan da ake sosai. Inna ma ta yi mamaki ganina cikin ruwa, a bakin kofa na tsaya na cire tufafina sannan na saka wasu su kuma na rabasu gefen kofa har ruwan ya dauke. Wayana ma ruwa ya shiga ciki ya taba shi sai dai na yi sa'a be yi komai ba.
Saman kujera na zauna sai Noor yanzo kusa da ni ya zauna ya jingina kansa da jikina.
“Momy ki ara min wayarki na yi game”
“A'a kai baka da aiki sai game”
“Momy dan Allah”
Ya fada kamar zai yi kuka, ni kuma na hana shi domin wayar babu carji sosai a ciki, sosai na maida hankalina kan Sakina da ke ta rihazar din sira da zasu yi gasa a kai, Inna kuma ta dauko kur'ane tana karatu.
“Inna ki min addu'ah Allah ya sa na yi ta daya”
Cewar Sakina ganin Inna tana addu'a bayan ta gama karatun kur'anen.
“Yaushe ne ma?”
“Gobe kuma?”
“Eh daman kwana biyu aka bamu ai”
“Allah ya bada sa'a”
Na fada tare da tashi na fita waje dan yi alwalar la'asar. Bayan na gama sallah ne Inna take tambaya ya aikin na amsa mata da Al-hamdilillah, sannan na dauki wayata na kira Bilal sai ta saka min user busy, haka na yi ta har biyar na yamma ta yi amman bata shiga ba, hakan yasa na fahimce cewar na saka numberta a blacklist ne, amman mi na masa har haka ne? Ko dai yana fushi da ni ne?
Sallama muka ji da bakuwar murya, duk kokarin da na yi na rike Noor sai ya ci tura domin tuni ya kai bakin kofa shi da Jamila daman rigangan suke gurin amsa sallama ko leke aga wanene.
“Nawwara na nan?”
Na ji kamar muryar da na sani, hakan yasa na yi wuf na fita waje, Rabi ce tsanye da gown ta dora rigar sanyi sama fuskantar dauke da murmushi kamar kullum, sai dai ba ni take kallo ba Noor take kallo cike da burgewa, hakan yasa na maida shi bayana sai ta kalleni tana cigaba da fadada murmushinta, kamin ya matsa jikin kofar gidanmu ta ce
“Bismillah”
Sai ga wasu maza su biyu suna ta shigowa da kayan abinci da kuma manyan akwatuna guda uku suka dora saman barandar dakin Inna. Ni dai kallo na bisu da su har suka gama ganin ta juya zata fita yasa na ce
“Waya ce a akawo?”
“Ke ma ai kin sani”
“Dan Allah ki koma da kayan nan”
“Ni ba zan iya ba, amman zaki maidawa da kanki”
Inna da ke tsaye bayana ta ce
“Malama jeki abinki mun gode kinji”
“Nima na gode Mama, Handsome boy sai anjima ko”
Noor ya daga mata hannu yana murmushi da ya fitar da dimples dinsa.
“Okay Anti mun gode”
Ji na yi kamar na buge masa baki. Bayan ta fice Inna ta kalleni ta ce.
“Ba a maka alheri ka maida ko ya yake Nawwara, idan ma har kina jin ba zaki iya amfani da abunda ya baki ba, zaki iya kyautarwa, kuma idan har kika cigaba da nuna baki son abun hannunsa ba zaki karba hakan yana nufi har yanzu kina sonsa, amman idan har kika karba kika manta da komai kika nuna masa ba komai hakan zai kidimar da shi, domin zai gane cewa yanzu kina mu'ala ne da shi kawai ba ta so ba”
“Amman ai kamar ina son sa ne idan na karba”
“Ba daga nan take ba”
Sakina taje ta bude akwatin tana duba babu komai a ciki sai tufafi da abaya da kuma gowns, sai atamfa da lace wadanda ba a dinka ba,
“Amman gaskiya ba za a maida wannan kayan ba, ai ba mu muka ce ya kawo ba, mun ci banza”
Cewar Sakina tana gwada wasu tufafin a jikinta.
“Wallahi Anty ko ba zaki aureshi ba ki tatsi banza ko zafi ki rage”
Ni dai ban kulata ba balle banzan zancenta, haka na zauna cikin rashin dadin rai har dare saboda Bilal be kira ni kuma na tura masa sako be maido min da amsa ba.
Bayan sallah isha'i dpo ya zo gidanmu, ya yi wasu tambayoyi ni da Inna sannan na fada mana ya shigar da kara kotu kuma karshen watan nan ne za a fara zaman kotu, hakan ya faranta min rai sai na dan sake zuciyata ta washe.
Washe gari ba mu karya da abunda muka saba karyawa ba, saboda Indomie da aka kawo mana ita Sakina ta dafa suka ci ita da Jamila da Noor shi kan har tsalle yake yana direwa kasa yana jindadi sun ci indomie.
Inna kan kunu ta sha as usual nima shi na sha dan bana son ko warin indomie na ji balle kuma na kalleta har ya kai ni ga ci.
Bayan sun wuce makaranta, ni kuma na soma gyara gidan, sai da na gama sannan naje na samo mai ruwa ya zuba mana jalka shida Inna ta bashi dari da hansi, sai na zuba na shiga wanka.
Ina cikin bandaki na ji sallamar Baba Sulaiman da Baba Dahiru, wato kanen mahaifina da kuma yayansa, sai dai ga dukam alamu ba su kadai suke ba, domin Hayaniya ta yi yawa, ko da na fito Inna ta shimfida musu tabarma suna zaune ciki har da abokin Baba wanda ya sama masa aiki a Abuja da kuma Alhaji Bashir Makama wato mahaifin Jibril da wani dattijo tare da su.
Na ji dadin da Allah yasa na shiga wankan da Hijabi da fitowa ta yi min wuya, karasa na yi na durkusa har kasa na gaishesu, sannan na wuce dakinmu zuciyata cike da maganganu kala kala. Ina cikin saka tufafi Inna ta kira hakan yasa na yi hanzarin saka kayan na saka wani Hijabin na fito na zauna kusa da ita.
“Nawwara kin gane ni”
Na dago na kalli Alhaji Bashir da ya yi maganar sannan na daga masa kai.
“Zuwa na yi na baki hakuri akan abunda muka miki, hakika bamu kyauta ba, na sani amman dan Allah dan darajar iyayenki ki yafe mana, Wallahi har ga Allah Jibril ya canja kuma ya yi nadama, be san na zo nan ba ba shi ya turo ni ba, kuma bana son ya san na zo, na yi niyar yin haka tuntuni amman kunya da nauyinki yasa na kasa yi, yanzu ma sai da na biyo ta bangare Babanninki suka karfafa min guiwa sannan na samu na karaso ki dubi girman Allah ke da mahaifiyarki ku yi hakuri da abunda muka muku”
“Ba fa kai ka yi ba”
Cewar Baba Dahiru, sai ya amsa da
“Ai da na ya yi kamar ni na yi kenan”
Ni dai bance komai ba banda hawaye babu abunda na ke, Inna ce kawai take amsa masa, shi ma sai da su Baba Sulaiman suka saka baki, daga karshe ya yi magana agaisuwar rashin Baba, sai kuma ya tambaya yi Noor.
“Sun tafi makaranta”
“Amman Jibril be san yana da ba ko?”
Kai na daga masa, sai ya soma labarta mana yadda Jibril yake son da da kuma irin halin rayuwar da ya shiga bayan rabuwarmu.
Ya dauki kudi mai yawa ya bawa Baba Sulaiman da Baba Dahiru, sannan ya miko mana bandir din yan dubu daya.
Sannan ya yi mana sallama yana cewa yau ya zo kuma yanzu zai koma daman saboda ni ya zo.
Bayan sun tafi Inna ta zaunar da ni tana ta fada min maganganu akan rayuwa da kuma hakuri, ganin irin kuka da na ke.
“Na hakura Inna amman ni fa ba zan taba komawa ba”
“Babu wanda zai cilas miki komawa, amman ko dan ɗan dake tsakaminku ya kamata ace kun yafi juna”
Tashi na yi na fita na koma dakinmu na zauna na yi kuka sai da na koshi sannan na shirya na fito na yi