Showing 66001 words to 69000 words out of 138998 words
lafiya?”
“Shekaranjiya, maleria ce ke damuna”
“Allah ya baki lafiya, Wallahi ban sani ba sannu”
Kai ta gyaɗa min sai ta miƙo hannunta ta kama nawa hannu ta jimƙe a sosai ta lumshe ido sai hawaye, a take hankalina ya tashi ji nayi kamar itama tafiya zata yi ta barni ban san lokacin da na fara nawa kukan ba, sai Maman Nura tasa mana dariya wai daman mu ƴan raki ne idan muna ciwo. Ban bar gidan ba sai da na yi sallah magariba a nan, ko da na dawo gida kaina na ta ciwo saboda kuka da na yi a gidansu Jidda.
Da kaina na labartawa Inna rashin lafiyar Jidda, ita ma kanta bata jidaɗi ɓa domin ta san yadda na ke da Jidda kuma ta san irin halin da Jidda take shiga idan bani da lafiya.
“Zata ji sauƙi ai kin san maleria yanzu yadda take ma mutane balle Jidda da rakin tsiya, Allah ya sauwaƙe sai gobe zanje na dubata”
“Amin amman gaaskiya tana jin jiki domin ta rame sosai jikinta kuma da zafi kamar ba a mata allura ba”
“Allah ya bata lafiya, ai malaria yanzu sai an sha allura sosai ake tashi”
Na tashi cikin rashin kuzari na nufi ɗakinmu. Washe gari da wuri na tashi kamar kullum bayan su Sakina sun tafi makaranta ni kuma na shirya cikin wata doguwar rigar yadi na yi ma Inna sallama tare da faɗa mata zanje gurin aikin sannan na saka Hijabi na fice. Gidansu Jidda na nufa dan duba lafiyar jikinta, una tafe ina ta mamakin tun jiya ba mi yi waya da Bilal ba be kirani ba ni kuma ina tsoron kiransa saboda ban saba ba kuma ban san hali da yake ciki ba, sai dai gaskiya a kwana biyu nan da ya saba min da kiran yasa ni jin babu daɗi.
Na yi mamakin ganinta ƙofar gidan tare da Mustapha suna magana duk da ban san mai suke magana akaiba na samu kaina da tsoro sosai saboda sanin wanene Mustapha.
Daga ita har shi ido suka ƙura min ganin irin kallon tuhumar da na ke musu, ba ma kamar shi da natsu guri ɗaya kamar na rikice da ganina.
“Kin san waye Mustapha a unguwar nan Jidda karki yarda ya yaudareki”
Na faɗa ina kallon Jidda da idonta ke cike da ƙwalla, shi kuma sai ya yi saurin girgiza kai yana faɗin
“Wallahi ba abunda kike tunani ba ne Nawwara”
Ni kuma na watsa masa wani shegen kallo.
“Mi na ke tunani miye bana tunani? Kasan na san waye kai ka gwadani baka samu ba shine zaka dawo gurin ƙawata? Ko kuma bayan ka gama da ita ne ka dawo kaina?”
“Babu komai a tsakanina da shu Nawwara nan ma ya zo ne saboda ke...”
Cewar Jidda hawaye na mata zuba.
“Saboda ni ko? Ki cigaba da biye masa har ya kaiki ya baro, waya sani ma ko ya lalata miki rayuwa kema”
Ina faɗar haka sai na juyo na kamo hanyar dowowa, zuciyata cike da zargi kala-kala. Sai da na yi nisa sosai na kai bakin titi ina ƙoƙarin tare Napep sai ga Mustapha ya sha gabana da Mota ya fito da sauri ya fuskance ni.
“Wallahi ba abunda zargi ba ne, na canja na Nawwara Wallahi na miki alƙwari ba zan sake yin wani abu marar kyau ba”
“Ka dawwama a cikin abunda kake aikatawa ko kuma ka tuba babu ruwan Nawwara a ciki wannan farincikin iyayenka ne da kuma masoyanka, Kuma dan Allah ka fita daga hanyata mahaifiyarka ma ta yi mana cin mutunci saboda kai tace muna zugaka kana ci mata mutunci akan gida, dan Allah ka ƙyale karka sake jamin wani bala'in gida dai zamu tashi mu bar maka abunda very soon In Shaa Allah”
“Ba ni na siye gidan ba Nawwara, wani ne ya siya sunansa Jibril ya ce shi mijinki ne”
Mamaki ne ya cikani.
“Ina ka ganshi?”
“Malam Haruna ne ya faɗa min na je na sameshi yace shi mijinki ne”
“Daga kai har shi baku da hankali, Kuma na faɗa maka ka fita hanyata”
ina kaucewa ya sake shan gabana.
“Nawwara mi zan yi ki yafe min mi zan yi ki yarda da ni? Faɗa min ko minene zan yi Nawwara ki yafe min?”
“Zaka iya dawo min da Habiba?”
“Wanda ya mutu baya dawowa kuma...”
Sai na tari Numfashinsa.
“Tau ba zan taɓa yafe maka ba”
Ina faɗar hakan na kauce na cigaba da tafiyata na bar shi nan tsaye yana kallona fuskarsa kamar wanda zai fasa kuka.
Na yi sa'ar samun Napep da wuri, ko da na isa gurin aikin takwas da ƴan mintuna, tun a bakin gate na haɗu da Amina abokiyar aikina, a tare muka ƙarasa ciki muka rubuta suna tare har tana cemin yau kan munyi latti ita tama daina ganina kwana biyu ina wasa da aikina, nikan dariya kawai na yi na ɗauke kai na nufi gurin aje Hijabina sannan na muka shiga ciki tare.
“Khadija Musa Kafinta”
Daf da za mu shiga lifted na ji an kirani sai muka waigo tare, wata ƙabila ce ta kira sunan nawa tana sanye da suit.
“Please Follow me”
Sai da muka haɗa ido da Amina sannan na bita ita kuma ta shiga Lifted, wata lifted muka nufa muka shiga tare sannan ta danna 5 lifted ta rufe muka fara tafiya. Ni dai ban kalli inda take ba itama bata ce da ni Uffan har muka isa sannan ta fita nima na fita muka doshi wani gurin daban.
Ina hango inda na bi shekaranjiya na shiga office ɗin Jibril na yi tunanin kalwaɗowa zata yi mu shiga office ɗin sai naga mun iso wani ƙaton ɗaki mai cike da computers da kuma files.
Muna shigowa sai matar ta juya ta fita wannan abokin nasa ya miƙe tsaye yana ɗaukar documents ɗin dake gabansa ya yi min magana ba tare da ya kalleni ba.
“Congratulations Miss Nawwara, kin samu baban promotion zuwa office ɗin Oga Jibril you're now his new PA, Rabi zata zo ta miki bayanin komai”
Mamaki ne na cikani new pa haka kawai bayan bana da dogon karatu?
“Amman ban yi wani zurfin karatun da za a bani wannan matsayin ba”
Kamar daga sama na ji muryar da nafi tsana a duniyar nan wato muryar Jibril ashe yana bayana ta gurin kujerar da ke farkon shigowa, ni ban ma san da shi ba kasancewar ban kalli gurinba tun da na shigo idona yana kan abokin nasa.
“Shi kuma ga damar baki idan kuma ba zaki yi ba you can leave”
Ba yabo ba fallasa ya faɗi haka ya kana ya miƙe tsaye suka fice tare da abokin nasa suka barni nan tsaye ina mamaki.
__________________________________________
Kalamaina sun yi ƙaranci su gode muku fans akan irin soyayyar da kuke nunawa littafin nan.
#Team RB
#Team Nawwara
#Team Jibril
#Team Mustapha
#Team bilal
Na gode na gode sosai Nawwara ta ce a gaishe da masoyanta.😜 Soyayyar da kuke nunawa littafin nan a yanzu Allah yasa ku nuna min irinta a littafi na gaba mai suna HAFSATU MANGA labarin ƙauye. Ina muku son so Fisabilillah a duk inda masoyin littafin nan yajke. 😍
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
3⃣6⃣
Wata kyakkyawar mace ce ta shigo mai far'ar fuska da kuma ta ruhi domin kuwa muna haɗa ido da ita sai naji kamar na santa, hannu ta miƙa min.
“Sannu sunana Rabi Ismail”
“Nawwara”
Na faɗa ina miƙa mata nawa hannun.
“Zo muje zan nuna yadda aikin naki yake”
Tana gaba ina biye har muka isa office ɗin Jibril, a gaban computer ta fara isa ta nuna min yadda zan danna na buɗe ƙofar farko ta shigowa, sannan muka ƙarasa ciki ta nuna abubuwan da zan yi da zarar na iso da safe, sai kuma abubuwan da Jibril yake buƙata da kuma tsarin yadda zan jera masa komai.
“Aikinki ne ki sanar da shi idan zai yi meeting kamin lokacin ya cika, da zarar ya shigo da wuri saki sanar shi duka abubuwan da zai yi, wayarsa da ke nan office ke zaki riƙa amsa ta, idan wani na buƙatar ganawa da shi ke zaki tabbatar da tsaro kuma ke saki saka time, yanzu kan ba zaki tashi aiki ba sai 4:00pm, kuma dole ne ki shigo 8:00am, masu kowa ƙorafi ko wani bayani na cikin kamfanin nan ke zaki kula da su shi kuma sai kije ki masa bayani a tsanake, aikinki ne gogewa da kuma gyara ɗakin nan, idan na shigo dole ne zaki tashi ki gaishe kuma ki tambayeshi abunda yake buƙata”
Ya juya ta ɗauko wata leda dake saman teburinsa ta miƙa min.
“Wannan kuɗi ne naira dubu ɗari biyar zaki siye tufafin da zaki saka masu kyau saboda Oga baya son ana saka tufafi marar rsada musamman yanzu da kike new PA ɗinsa, wannan kuma makullin gida ne dake Abdullahi Fodio Road a gidan zaki zauna komai akwai a ciki”
Na sauke ajiyar zuciya ina kallon makullin data fiddo daga aljihunta tana miƙa min.
“Daman idan mutun ya fara aiki haka kuke masa a wannan kamfanin?”
“A'a Karamci ne kawai irin ya Oga Jibril ina tunanin kina da muhimmanci a gareshi sosai shiyasa”
“Ki bar kuɗin ki aje makullin kuma ki faɗa masa ba zan yi aikin ba”
“Amman miyasa?”
Ban bata amsa ba na juyo na yi tafowata zuciyata na ta raya min abubuwa da dama, idan har na yarda na yi aikin nan tau Jibril ya ƙwareni kuma duk wulaƙancin da ya yi ya tashi a banza kenan, taya mutun zai wulaƙanta ni sai kuma na dawo na fara aiki a tare da shi? Ya samu danar wulaƙanta ni saboda kuɗin da yake da su, yanzu kuma sai na yarda ya yi amfani da kuɗin ya maye gurbin abunda ya aikata? Lallai ni wawuya ce.
Haka na ke ta tunanina har na iso reception na ɗauki wata a inda na aje tare da Hijabi na saka na nufi ƙofar fita ba tare da na saka lokacin da na tashi ba.
“Nawancy”
Da sauri na juyo jin muryar Bilal, sai na sakar masa murmushi kamar yadda shi ma yake min.
“Ashe kin shigo?”
“Ee amman yanzu zan koma”
“Har kin gama aikin ne?”
“Ee yau baka kirani ba, duk na damu”
Ɗan murmushi ya yi muna fara takawa tare yana faɗa min akwai abunda ya ɗauke masa hankali.
“Amman ko minene ai ya kamata ka min ko da massage ne”
“Haka ne am sorry my dear ba zan sake ba”
Hango Jibril da na yi a tsaye a gate ɗin garden yasa na washe haƙura ina kallon Bilal.
“Ma yafe maka ammam karka yarda ka ƙara”
“Allah ya Huci ran sarauniya ba zan ma sake ba”
Haka mike tafiya tare muna firarmu sai dai yadda na ke dariya sai ka ɗauka wani labarin ban dariya ne yake ba ni.
Muna dosar gate Jibril kuma ya doso cikin kamfanin tare da mutumen da suke magana tare.
“Good Morning Sir”
Bilal ya faɗa cikin girmamawa a lokacin da Jibrilya kawo kusa da mu, ni kan ko kallonsa ban yi ba har sai da na ji maganar da ke fitowa daga bakinsa.
“Miye tsakaninka da wannan yarinyar?”
Ƙasa Bilal ya yi da kansa ya kasa amsawa kamar mai tsoro sannan ya buɗe baki xai yi magana sai na yi karaf na karɓe duk da ba ni ya tambaya ba.
“Wanda zan aura ne”
Sai ya juyo kaina ya kalli fuska a ɗaure ya ce
“Bamu gina wannan kamfanin domin masoyaba, idan zaku yi soyayyarku sai ku yi ta a can waje nan kam domin aiki muka ɗaukeku dan haka bama buƙatar ganin wani abu daya alaƙancin soyayya a nan. Ku wuce gurin aikinku”
Kallona Bilal ya yi ya sakar min murmushi.
“Sorry Nawancy zan kira ki”
“Okay Dear I love you”
“I love you too”
ya mayarmin da martani sannan ya juya ya koma ciki. Ina kallon yadda Jibril ya ɗauke kai ya haɗe yawu da ƙarfi, ya saka hannunsa ɗaya a aljihu ɗayan kuma ya jimƙeshi sosai.
“Wuce kije office”
“Ba zanyi aikin ba”
Na bashi amsa kai tsaye, sai ya ɗaga kafaɗunaa alamar ko a ajikinsa. Ni kuma na kama hanyar fita daga harabar kamfanin.
Ina cikin Napep kira ya shigo wayata da fari na ɗaukar Jibril duk kasancewar baƙuwar number ce, hakan yasa na ƙi ɗauka, sai dai har na isa gida ba a daina kiran ba da zarar ta tsinke sai a sake kira ni kuma na ƙi na ɗaga. Ko da na shigo Inna na wankin tufafinta na sakawa, da sauri na cire Hijabina na aje na tsuma hannayena cikin wanki ina faɗin ta cire nata.
“Amman dai yau ma kin yi saurin dawowa”
“Na gama aikin ne da wuri”
“Bayan fitarki Ɗansandan nan ya zo be tararda ke ba ya ce zai sake dawowa”
“Ya yi wata magana ne?”
“Cewa Ya yi suna nan suna cigaba da bincike amman yana son ganawa da ke, ya kuma tambayeni akan yadda muka tararda Babanku lokacin da muka je duba shi”
“Uhmm su dai suka sani”
“Wayarki tana ƙara”
“Barta a can kiran bashi da muhimmanci”
Na faɗa ina ɗauraye kayan da ta fara wankewa, a hankali na ji ta kira sunana.
“Nawwara? Kwana biyu nan kin chanja kamar akwai abunda ya ke damunki, ki daina barin damuwa a ranki ki riƙa sanar da ni abunda ya kamata na sani tun wuri”
Na tsayar da abunda na ke na kalleta.
“Babu komai Inna, kawai ina tunanin Noor ne da makomarsa”
“Makomar Noor tana hannun Allah da kuma shi kansa, ki daina damuwa da matsalarsa idan ya girma zai nemi mahaifinsa da kansa ko kuma shi mahaifin nasa ya nemeshi, amman ki daina damuwa arzikinki Noor na mijine ba mace ba”
“Amman ni Inna ina ganin kamar ba zan iya ƙyale Noor yaje gurin mahaifinsa ba, bayan wulaƙancin da ya masa ya yi min sai kuma ace na yarda na bada ɗan gaskiya ba zan iya bari Noor ya kusanci wannan mugun mutumen ba”
“Ko da ya gane kuskurensa ya nemi yafiyarsa? Ba a shiga tsakanin ɗa da uba Nawwara yanzu kin ga duk wannan abun Noor be san da shi ba aiko abun farincikin ki idan har yau Allah ya kawo babansa ya nemi ɗansa da kansa”
Idona ya cika da ƙwalla.
“Amman Inna kamar akwai ƙwaruwa a ciki, ku kuka raini yaron nan sai kuma a ɗauka a miƙawa uban bayan uban be san darajarsa? Gaskiya ni ba zan iya yafe masa ba”
“Ban ce ki yafe masa ba kuma ban ce karki yafe masa ba, amman bashi ɗansa kan dole ne indai har ya buƙaci haka, yara su tashi a gidan iyayensu maza yafi daraja da ƙima fiye da iyaye mata, ke kanki zaki fi jindaɗi na san ba zaki so Noor ya yi agolanci ba, saboda ba ko wane uba ne yake son a kawo masa ɗan wani a gida ba, ba duk miji ba ne zai so ki ya so ƴaƴanki, ni kuma ba burina ki yi ta zama a gida ba bana da natsuwa Nawwara har sai kinyi aure kin zauna ɗakin mijinki”
“Amman ai be zo karɓan ɗansa ba kwata-kwata be taɓa sakashi a ido ba, kuma irin wannan mutumen kike goyon bayan na bashi ɗansa?”
Na faɗa ina kuka, ji nake kamar da gaske rabani za'ayi da ɗana.
“Misali ne kawai na ke baki, ba wai na tabbatar zai zo ba ne, amman zuwansa yana da muhimmanci Nawwara domin zai wanke zargin da mutane suke miki, kuma Noor zai san waye ainahin ubansa na gaskiya”
“Ni gaskiya zan maida Noor gurin Gwaggonsa”
“Wace Gwaggonsa kuma? Zumuntar uwa suka haɗa ko ta uba da zaki ɗauki yaro ki kai mata saboda kawai kin auri yayanta? Faɗa min abunda kike ɓoyewa Nawwara ko shine yake kiranki?”
“Ni ma ban sani ba, amman Inna Noor zai iya rayuwa ko babu babansa a kusa da shi ko da ma ace Ubansa ya mutu”
“Allah ya kyau”
“Amin”
Na amsa ina kuka sosai har da mazina. Ban gama wankin ba sai da aka yi azahar, a lokacin su Sakina suka dawo makaranta, Noor da ciwo a ƙafarsa wai yaje buga Boll ya buge da dutse har jini ya fita.
A ranar ba tare da shi suka je Islamiya ba saboda ciwon ƙafan, da suka dawo ne suke labarta mana wai yau sun yi babban baƙo a makarantar su har ya saka gasar karatun sirratul nabiy wacce ta yi ta ɗaya za a bata gida ta biyu kuɗi dubu ɗari biyar ta uku kuma dubu ɗari biyu da hansin, kuma su uku kawai aka zaɓa Sakina sai wasu ƙawayenta biyu.
Inna ta yi murna sosai kuma ta nuna jindaɗinta har tana addu'ar Allah yasa Sakina ta ci, ya yinda ni kuma na ke ta tunanin kamar ba gasar Allah da Annabi ba ce.
JIBRIL POV.
Shi kansa ya san ya cancanci a yaba masa akan namijin ƙoƙarin da ya yi na ɗauriyar sauraren kalma mai tsada da Nawwara ta furtawa Bilal. Sai dai tun daga lokacin baya jin sukuni har yanzu, kalmar kawai yake ta ji a kunnensa tana masa yawo kamar wanda zai haddace sautinta.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Shine abunda ya fi furtawa a duk lokacin da yaji abun ya haye masa zuciya. Safa da marwa yake ta yi a ɗakin ya kasa natuwa guri ɗaya.
“Am so so sorry Naj am so so sorry please forgive me”
Ya furta yana janye hannun rigarsa sai ga sunanta shimfiɗe a ɗamtsensa da tattoo, shafa gurin ya shigayi ya lumshe ido sai ga hawaye.
“I love you so much bana son na zama wani kalar mutum Ya Allah help me”
Zaunawa ya yi bakin gado yana ta tunanin abunda zai fissheshi, can ya miƙe tsaye ya saka hannunsa ɗaya ya saka aljihu ya fiddo wayarsa ya danna number Nawwara, haka ya jera mata kira biyar bata ɗaga ba sai ya sake kira na shida ya bar wayar saman madubi ya fita zuwa kitchen ɗan haka wa ƙansa tea.
“Hello Momina tana banɗaki idan ta fito zan faɗa mata”
Noor ne yake maganar sannan ya katse kiran jin ba a amsa masa ba, a daidai lokacin Jibril ya dawo ɗakin ɗauke da kofin tea, wayar ya sake ɗauka ya duba sai ya ga anyi picking, da sauri ya sake kira sai aka kashe ya sake kira aka sake kashewa sai kawai ya yanke shawarar aika mata da saƙon karta kwana wato sms.
Da kansa ya tsara rabutun ya tura mata sannan ya jefar da wayar ya miƙe tsaye ya nufi window yana ta kurɓa tea ɗin zuciyarsa na mugun zafi, ji ya yi ba zai iya jurewa ya aje