Showing 117001 words to 120000 words out of 138998 words

Chapter 40 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

752

ji shikenan zan masa magana”

“Ba hauka na ke ba Jibril ka tambayi Rabi ka ji ita ta fada min komai, shiyasa na koma aiki tare da kai nasa ka karbe kamfanin daga hannunsa ya dawo hannunsa shine yake kiran Abbah ya fada masa komai saboda ya lalata maka rayuwa yasa ka fara shan cocaine, kuma shi ya kade Noor da mota lokacin da suka taso makaranta, Noor ya ganshi shiyasa ya ki yarda su yi ido hudu da Noor saboda karya nuna shi”

“No Nawwara Bilal ne ya kade Noor”

“Ba shi ya kade ba, lokacin da Noor ya yi hadari Bilal yana kamfaninka yana aiki, shine duk ya tsara wannan Jibril ka karda da ni, Rabi ce ta fada min komai idan bata fada min ba babu yadda za ayi na sani”

Wayarsa ya dauko ya kira Rabi tana dauka ya ce.

“Duk inda kike ki zo ki same ni yanzu nan gidansu Nawwara”

Be tsaya jiran abunda zata ce ba ya kashe wayar ya kira Siraj.

“Siraj ka zo nan gidansu Nawwara gani nan na iso”

Nan ma kashe wayar yayi sannan ya kalli Nawwara.

“Siraj ba zai min haka ba, babu dalilin da zai sa Siraj ya sace Noor”

“Wallahi da gaske nake Siraj ne ya sace shi”

Siraj ya riga Rabi isowa duk da kasancewar ta fishi kusa da unguwarsu Nawwara, bayan ya shigo cikin gidan ne sannan Rabi ta iso, Nawwara na ganinsu ta mike tsaye tana hawaye

“Rabi fada masa gaskiya fada masa abunda kika fada min akan Siraj”

Rabi ta nuna kanta.

“Ni Kuma? Mina fada miki ne?”

Nawwara ta girgiza kai.

“Karki min haka dan Allah ki fadi gaskiya”

“Gaskiyar me zan fada? Ni ban san komai akai ba”

Inna ta matso kusa tana kallon Rabi da mamaki ta ce

“Yar nan ki ji tsoron Allah ki fada gaskiya, ke fa kika sami Nawwara a cikin gidan a nan kika fada mata cewar Siraj so yake ya kashe Jibril da ita kuma shi ya kade Noor”

“Haba Inna da girmanki be kamata ki yi wannan maganar ba, bata dace da ke ba, ni gaskiya ban san komai a kai ba”

Jibril ya kalleta

“Look Rabi ki fada mana gaskiya”

“Sir Jibril ban san komai a kai ba, idan ma wani abun ne ai kai zan sama na fadawa gaskiya ba Nawwara ba”

Faduwa Nawwara ta yi kasa tana kuka da tureturen kasa kamar mai aljanu, hakan yasa Jibril zargin tana kokarin fita hayyacinta ne. Sai ya kalli Siraj

“Siraj yi hakuri dan Allah ka je gida yanzu zamu kaita asibiti Rabi ku wuce kawai”

Siraj da tuni gumi ya gama keto masa ya juyo a firgice ya fice, sannan Rabi ita ta fice hankalinta sam baya jikinta.

Sai Dsp nan ya kira Jibril gefe yana tambayarshi alakar da shi tsakaninsa da Siraj, Jibril be boye masa komai ba ya fada nasa sannan Dsp ya bi bayan Rabi.



NAWWARA POV.

Ba zan iya cewa ga halin da na ke ciki ba, ni dai nasan bayan abunda ya faru a gidanmu Inna da Jibril sun kawo ni asibiti shi ma sama sama nake gani kamin Jibril din ya shigo ya yi min allura, sai yanzu da na farko sai na ke ganin komai kamar a mafarki hudun da na hango a window ne ya tabbatar min da cewar dare ya yi domin ko da abun ya faru da safe ne misalin tara zuwa goma.

Tashi na yi zaune sai naga drip a hannuna, tunawa da Noor yasa idanuwa cika da kwalla, dakin babu kowa sai kayan tea da dan karamin freezer, ina haka Jibril ya turo kofar dakin ya shigo.

“Sannu”

Ya fada yana cire min drip din a hannu.

“Ka yarda da ni Jibril Wallahi Siraj ne”

“Na yarda Nawwara”

Ya fada sannan ya cire safar hannunsa ya shi ya shiga hada min tea. Wayarsa ce ta yi ringing sai ya aje hada tea da yake ya yi picking.

“Eh miya faru? Da gaske? Okay gani nan zuwa”

Haka kawai na ji ya fada sai ya juyo ya kalleni.

“Anga Noor police sun tafi da shi asibitin Uduth za a duba shi”

Da sauri na sauka saman hospital bed din hankalina a tashe.

“Jibril zan je”

Tare muka fita, a waje muka hadu da Inna sai duk muka dugunduma gaba daya muka nufi Uduth din dake gawon nama.
Kamin a isa har jin na yi kamar na runtse idona na ganni gaban asibitin. Muna isa parking space din na asibitin na bude na fito da sauri ni da Inna sai dai duk da haka jibril ya rigamu isa Emergency din kasancewarsa Namiji kuma ya hada da gudu, muna isa muka tararda Dsp din nan na dazu tare da wasu yan sanda sanye da uniform. Muna isa sai ya tare mu wai Jibril kawai zai shiga ya ga Noor ba tare da ni ba.

“Kamar ya ni ce mahaifiyarsa fa”

“Na sani amman shi zai shiga”

Zan kara magana Inna ta rike ni ta ce ta Jibril din ya shiga, sannan ta shiga kiran yan'uwa tana sanar musu a waya. Jibril ne ya fara shiga ni da Inna muka tsaya ina ta jin kamar na yi tsalle na shiga na gani. Muna haka Jibril ya fito a daya daga dakunan dake Emergency din fuskarsa da hawaye, kamin ya karaso kusa da mu ya zame kasa ya fadi yana kokarin rike wata kofa dayan hannunsa na danne da zuciyarsa.
[11/11, 10:56 PM] Farar Mace...: *RAI BIYU...♥🖤*

Wattpad @KhadeejaCandy


5⃣4⃣

JIBRIL POV.

Wani irin nauyi zuciyarsa ta yi masa har ta kai kafafunsa ba sa iya daukarshi, yadda ya ga Noor yana ta masa yawo a idanuwa, but Nawwara da ya hango ta fadi zaune tana hawaye, sai tausayinta ya lullube masa zuciya, a kokorin mikewa ya yi tsaye ya tunkareta yana kokarin buye damuwarsa.

“Ya mutu ko?”

Ta tambaya cikin rawar muryar da kuka ya dakishe mata ita.

“No lafiyarsa kalau”

Ya fada yana kokarin tare hawayen da suke son zubo masa. Daukar Numfashi Nawwara ta fara yi idanuwansa na kokarin rufewa kamar wacce za a cirewa zuciya. Inna kuma ta dora hannu saman kai ta fashe da kuka tana rika Nawwara.

“Help us please”

Jibril ya fada yana karasawa kusa da ita, hankalinsa a tashe dan shi a yanzu ba nata yake ji ba na Nawwara yake ji, sai wasu Nurses suka zo da gudu suka rikata suka dauketa suka dorata saman gado suka nufi wani bangare da ita, shi kuma ya juyo ya dawo dakin da Noor yake kwance kamar gawa likita biyu ya tarar a gurin sai Nurse daya da ta mika masa wasu takardu Jibril ya saka hannu sannan suka dauki Noor din suka fita da shi zuwa dakin tiyata.

Jinginawa Jibril ya yi da kofar gurin ya lumshe ido hawaye suka zubo masa, zuciyarsa na ta raya masa kamar Noor ba zai rayu ba, an yanka masa ciki da wuka har hanjinsa sun bayyana ga gefen fuskarsa ma ya kumbura. Sai da ya share hawayensa sannan fito daga dakin ya nufo gurin da Dsp din yake wani irin bakinciki da bacin rai na fisgarsa.

“Dsp taya haka ya faru? Na fada maka idan har kun gano inda yaron nan yake ku fada kamin ku yi komai”

Dsp be ce masa komai ba sai da suka fito daga Emergency din sannan ya kalleshi ya ce

“Aikinmu muke yi Jibril da ace na tsaya kiranka da wata kila yaron nan be rayu ba, domin a can cikin daji muka dauko shi, can cikin arkilla tanki can cikin dajin nan dake saman dutse”

“Ina Siraj din yake?”

Ya tambaya yana sauke ajiyar zuciya.

“Yana can station nasa a tsare shi, karka damu da wannan”

“Rabi fa?”

“Am sorry jami'an mu gawarta kawai suka samu”

“How”

Ya tambaya a rude.

“We don't know yet but idan komai ya laba zamu bincika”

Kansa ya daga sama ya kalli taurari zuciyarsa na mugun quna.

“Siraj...”

Sai yasa yatsansa ya share hawayen da ke gefen idonsa. Juyowa ya yi ya dawo ciki, tafiya yake amman ji yake kamar ba taka kasa yake ba, numfashinsa ba ji yake kamar ba a jikinsa yake ba, yana karasowa kofar Emergency Inna na isowa cikin tashin hankali.

“Noor ya mutu ko?”

Dsp ne ya shiga mata bayani Jibril kuma ya doshi dakin tiyata yana safa da marwa, gabansa sai faduwa yake.

Awarsu biyu a dakin tiyatar sannan suka fito da Noor unconscious, da sauri Jibril rika gadon da Noor yake ya kai hannunsa ya taba gefen wuyansa sannan ya sauke ajiyar zuciya. Daya daga cikin likitan biyu da suka masa tiyata ya san Jibril farin sani saboda sun yi aiki a tare asibitin Abuja, shi ya dafa Jibril ya ce

“Ka kwantar da hankalinka, tiyata ta yi kyau sai dai ka masa fatar samun sauki”

Kai kawai Jibril ya iya dagawa ya saki gado ya rike ginin gurinsa saboda mugun ciwo da zuciyarsa take, daker ya mike tsaye daidai ya bi bayan Nurses din har suka isa icu suka canjawa Noor gado saka dora masa oxygen sensor sannan suka masa wata allura a hannu mai hade da drip, sannan likitan ya dauko wani abu mai guda biyu mai kamar iron ya hada shi ya goga sannan ya kurga 1 2 3 ya danna gaban Noor dai dai zuciyarsa.
Sai ga Noor ya numfasa da mugun karfi sai kuma ya lumshe, numfashinsa ya shiga nunawa a sensors.

“Al-hamdulillah”

Shine abunda Likitan ya fada da duka Nurses din kasancewarsu musulmai. Wani irin lumshe ido Jibril ya yi ya bude bakinsa kunshe da godiyar Allah.



NAWWARA POV.

ban san iya awa nawa na yi a sume ba ni dai na farka na ganni saman gado oxygen na sanye a fuskarta, abunda ya faru ne ya soma dawo min zuciyata na ta nuna min cewar da na ya mutu. Ban san akwai mutum a kusa da ni ba har sai da na fara hawaye.

“Am sorry Nawwara Noor yana nan raye an masa tiyata kuma an yi nasara”

Kallo daya na yi masa na kawarda fuskata, sai na rika kokarin sauka saman gadon.

“Babu inda zaki iya zuwa a yanzu karfe uku na dare ne, kuma babu wani karfi a jikinki a yanzu, Inna tana tare da Noor ni ma bata san ina nan ba, Sakina aka sa ta kwana da ke tana waje”

“Ya mutu ko?”

Na tambaya ina kuka duk da nasan amsar ba zata min dadi ba amman ina da bukatar jinta, sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce.

“Be mutu ba”

“Dan Allah karka boye min Jibril ka fada min gaskiya”

“Zan raka ki yanzu ki ganshi”

Saukowa na yi daga kan gadon duk da babu kwarar kuzari a jikina, sai dai na samu gwarin guiwar tafiya ne saboda jin cewar zan ga Noor ne hakan ya tabbatar min da cewar basu kashe shi ba kenan. Hankalina ya tashi sosai lokacin da na ga halin da Noor yake cikin, duk kokarin da Inna da Mama Turai suka yi na hana ni kuka hakan be yi tasiri ba sai da kuka sosai kamar Noor din ya mutu ne.

“Ina aka ganshi? Waya masa haka?”

Na tambaya ina kallon Jibril a zuciyata kuma ina jin cewar zan iya daukar ma dana fansa a kan duk wanda ya yi masa wannan abun. Be bani amsa ba sai ya juya ya fita ni kuma na bishi duk da babu wani kuzari a jikina Inna ta biyoni tana kirana sai ya juyo ya daga mata hannu alamar ta bari hakan yasa ta juya ta koma.
Haka na cigaba da binsa har muka koma dakin da aka kwantar da ni wanda ya kasance babu kowa a dakin sai ni da shi.

“Siraj ne”

Ya fada ba tare da ya kalleni ba.

“Amman da na fada maka karyata ni ka yi, da ace ka dauki mataki tun a lokacin da haka be faru da Noor ba, amman sai ka maida ni mahaukaciya”

Kallona ya yi da idanuwansa da suka rine suka yi ja sosai saboda kuka da kuma bacin rai ya ce

“Kin riga kin kira Siraj kin tuhume sa, ni kuma na kirashi tare da Rabi ne saboda na tabbatar da abunda kike fada, da ace na sa ana rike Siraj a lokacin nan da har yanzu Noor be bayyana ba, da ganga na kai shi asibiti saboda ya yarda cewar haukace take son kama ki, amman ban boyewa Dsp komai ba a game da Siraj, hakan yasa ya bi bayan Rabi saboda ni da shi duka mun lura da yanayinta, da ace ban turki Rabi a wannan lokacin ba da ba zata taba fadin gaskiya kamar yadda ta yi a yanzu ba, ashe all this while Rabi ta san inda Noor yake amman ta kasa fada saboda tana tsoron abunda zai biyo baya, Siraj ya bata yarda shiyasa ya fada mata inda ya aje Noor, and Nawwara na san idan har Rabi bata fada miki ba babu yadda za ayi ki san wani abu daya shafi kanfanina ko kuma rayuwata kuma na san idan har bata fada ba babu yadda za ayi Inna ta goya miki baya, i do believe you sai dai babu yadda za ayi na nuna hakan a gaban mutumen da na daukeshi kamar dan'uwa, Rabi da kanta ta fadawa Dsp inda Noor yake a lokacin da komai ya kure saboda isha'i ta yi a lokacin kuma ta fadawa police cewar rayuwarta tana cikin hatsari, but ko da suka je sun yi latti an riga an kasheta, Noor kuma suka same shi a cikin gidan da ta fada musu an yanka masa ciki”

Hannu nasa na rufe bakina saboda kukan da ke son ya ci karfina, sai na rika gadon na zauna ina kuka a hankali.

“Komai ya faru saboda ni Nawwara”

Ya fada yana hawaye tare da danne kukan da ke son kubuce masa.

“Rabi ta rasa ranta saboda ni, an yanka cikin Noor saboda ni, kin sake shiga tashin hankali saboda ni, da ace ban dawo rayuwarki a karo na biyu ba da duk haka be faru da ke ba, kina da gaskiya Nawwara, kina da dalilai na ki na, a duk lokacin da na kusance ki sai wani abu marar kyau ya faru da ke, ni ne silar lalacewar rayuwarki a karon farko, na dawo a yanzu da tunanin zan iya gyarata na saka miki farinciki saina sake bakanta miki wanda ba hakan raina ke so ba, but komai ya kare yanzu.

Na miki alkwari daga ranar da Noor ya ji sauki ya tashi, ba zaki sake sani a idanuwanki ba, balle na dame ki ba zaki sake kuka da ni ba, kowa ma ba zai sake kuka da Jibril ba, zan tafi wata duniyar wacce babu wanda na sani kuma babu wanda ya san sai na yi rayuwa a can har ta Allah ta kasance, saboda ciwon da ke jikina yana tabbatar min da cewar mutuwata tana kusa da ni a yadda na ke ji a zuciyata na san ko da wane irin lokaci zata iya bugawa na mutu, ina tsoron sake kusantarku ke da Noor wai Nawwara saboda kar wani abun ya same ku... Ki yi hakuri da duk abunda ya faru, but no matter what Nawwara har gobe ina son ki, ko da na mutu a yau na mutu da ciwon son ki ina son ki san wannan, ina son zuciyarki ta gansu cewar ni masoyinki ne ba makiyinki ba”

Yana fadar hakan ya juya ya fice be damu da ya share hawayen da suka bata masa fuska ba, ni kuma na bishi da kallo zuciyata cike da tausayinsa da na kaina da kuma na Rabi da Noor...
[11/13, 6:25 PM] Farar Mace...: *RAI BIYU...♥🖤*

Wattpad @KhadeejaCandy


5⃣5⃣

JIBRIL POV.

Haka ya fito harabar asibitin hawaye na bin fuskarsa, babu komai a zuciyarsa na sai tausayin dan sa, kansa kuma empty har ya rasa da ina zai fara tunani akan Siraj. Be damu da tsakar dare ba ne ya shiga motar ya kamo hanyar sama road. A bakin gate dinsa ya tsaya cikin mota ya kira mai gadinsa a waya ya zo ya bude masa gate sannan ya shiga ciki ya faka motarsa ya fito jikinsa babu gwari ya shiga falonsa, saman sofa ya jefar da makulin motarsa ya shiga bedroom ya cire kayan jikinsa sannan ya daura tawul ya shiga bathroom.
  Gaban madubin da ke bandakin yaje ya tsaya ya kallon still hawaye ba su daina masa zuba ba.

“Why Siraj mi na maka?”

Ya tambaya kana ya fashe da kuka sosai ya fadi kasa zaune ya dafe kansa. Kuka ya yi sosai mai sauti kamar mace sannan ya tashi ya nufi shower ya sakarwa kansa ruwa, ya lumshe ido yana ra sauke ajiyar zuciya a hankali. Sai kusan hudu da rabi na asuba ya fito daga bathroom din shi ma dan wayarsa dake ta ringing ne. Gaban madubi ya karasa inda wayarsa take ya dauka ya duba, number Abbah ce yana ta kiransa cikin hanzari ya yi picking.

“Assalamu Alaikum Abbah”

“Jibril kana lafiya?”

“Lafiya kalau”

“Am sorry na kiraka da dare, na damu ne kawai and Jibril ka yi hakuri da yadda rayuwa ta zo maka dan Allah, dsp ya yi min bayanin komai nasan kana cikin tashin hankali dazu shiyasa ban kiraka ba, gobe muna nan zuwa tare da yan'uwan Rabi ka kwantarda hankalinka ka ji”

Sai kawai ya fashewa Abbah da kuka.

“Ba ni da wani sauran kwanciyar hankali Abbah, na rasa komai kuma saboda ni komai ya faru Abbah ni ne silar komai”

“Aa Jibril ba kaine ba, haka Allah ya tsara babu yadda za'a yi ka tsalleke karka sa komai a rana ka”

“Toh Abbah thank you”

Ya fada yana share hawayen idonsa, sannan ya aje wayar ya kalli kansa a madubi.

“Al-hamdulillah Allah na gode maka, komai ka yi daidai ne, Allah kai ka tsara min haka a rayuwata ban isa na tsalleke ba, Allah ka bani hakuri dauka abunda duk ka rubuto zai faru da ni, ka yafe min abunda na maka Allah, ka karbi rayuwata ina mai shauki da murnar haduwa da kai, Allah karka karbi raina ina mai bakinciki da damuwa kusantar ka”

Yana gama fadar hakan yaji wani irin rahama da natsuwa sun sauko masa a zuciya. Komawa ya yi bathroom din ya yi alwala ya fito ya saka jallabiyarsa ya yi nafila sannan ya tsaya jiran assalati ya dora da asuba, bayan ya gama ya zauna ya yi azkar na safiya tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login