Showing 57001 words to 60000 words out of 138998 words
ya kasa fahimta ta, wannan ƙorafin da na kaima yasa ya kira mahaifin Jibril ya yi masa magana akan tarewar mu.
A cikin watan nan aka yi kawo lefena kayan masu kyau da tsada, bayan sati ɗaya aka yi walimarta Daddy ya aika da ƙaramar mota aka ɗauko Mama da wasu daga ƴan'uwanta da kuma ƴan'uwan Baba.
Ranar da akayi walimar aka kaini gidansa bayan anyi min huɗuba sosai ciki har da Mama da take ta kukan rabuwa da ni, ni kaina ba zan iya misalta irin kuka da na yi a wannan ranar ba. Tun tara na dare aka kaini gidansa amman abokansa basu shigo da shi ba sai ƙarfe goma sha biyu, su kansu kamar sun sam baya son auren suka mana addu'a suka fice tare da wasu ƙawayena.
Misalin ƙarfe ɗaya na dare ya bar gidan, ban saka shi a ido ba har garin Allah ya waye, haka na kwana na wuni be shigo gidan ba har sai da aka kwana huɗu tsoro duk ya kamani saboda ƙaton gida ne gashi ni kaɗai ke ciki sai ƴan aiki da safe ne kawai ake aiko mana da abinci daga gidan Momy, yau ma da yake rana da huɗu ne ba a kawo ba ni na girka da kaina. Sai a ranar na biyar ya shigo shi ma kuma tare da budurwa Aisha, a gidan suka wuni suka kwana idan yana buƙatar wani abun ko kuma tana buƙata sai ya aiko min da saƙo a waya na tashi na yi musu, ni dai na yi ma kaina alƙwarin ba zan taɓa nuna masa ina jin zafin abunda yake ba, ba kuma zan taɓa saɓa umarnin iyayena na cewar na yi duk abunda ya saka ni.
Ranar da na gaji da zama gida na fita maƙota, gidan wata matar na shiga wacce gidanta ke kusa da nawa sosai, ba laifi matar tana da son mutane da far'a Cikin ƙanƙanen lokaci muka sabu har ta kai gidan naje gidanta sai dare zan dawo shi ma kuma idan mijinta ya dawo, ita da kanta ta fara fahimtar irin zaman da nake da miji har ta tambaye ni na labarta mata kaɗan sai ta bani shawarwari akan na daina biye masa kuma na nuna wayeta sosai saboda shi yana shiga ƙasashen turawa ne dole idonsa zai buɗe da yawa.
Gaskiya Ummi Faisak na da kirki na koyi abubuwa da dama a gunta ciki har da girki da kuma iya kwalliya, sai dai ban taɓa gwada ko ɗaya ba saboda na san irin mijin da na ke aure.
Wata rana ina gidanta har dare sai gashi ya kira ni na ce masa ina maƙota yanzu zan so, ko da na fito sai na same shi bakin titi yana jiran ƙarasowata shi da wani abokinsa, ina isowa ya wanke min fuska da mari da har sai da na ga wasu ƙananan taurari, har abokinsa ya yi ƙoƙarin riƙeni saboda tangal-tangal da na yi zan faɗi, abun mamaki sai ya fara faɗa da abokinsa kamar zai cinye sa wai taya zai yi ƙoƙarin riƙa masa mata ai ko baya so na yasan zafina na matarsa kar an ya sake masa haka.
A ranar na wuni da zugin marin shi kuma ya wuni yana ta mitar fitar da na yi, hakan yasa ya kulle kitchen kuma ya karɓe wayar da ke hannuna, wai naje gurin matar da nake zuwa ta bani abinci. Daga lokacin kullum da yunwa na ke wuni na kwana sai ya ga dama zai dauko wani abun ya bani jiki na rawa na karɓa na cinye, sai na koma abar tausayi, da na masa laifi kaɗan sai ya dakeni kamar wata ƴarsa, yana yawan shigowa da Aisha ta kwana a gidan ko ta wuni yasa na dafa musu abinci na kai musu ruwan wanka idan sun gama sai naje na ɗauke kwanukan, sai dai duk da haka ko da wasa be taɓa sakewa Aisha fuskar da zata rainani ba baya bari ta sakani aiki ko ta faɗa min wata maganar marar kyau idan ma an wulaƙanta a gidan to shi ne kawai yake da wannan damar.
Wata rana ina zaune falo cikina na kukan yunwa, shi kuma yana ɗaki sai gashi ya fito ya jefo min wayata wai zan yi waya da Mama, sannan ya juya ya fice daga falon.
“Babanki ba lafiya Nawwara, kuma bamu da komai, shine na ce idan da wani abu a hannunki ki aiko mana dan Allah, ko abinci sai mu siya”
Shine abunda Mama ta roƙa ni kuma na ce mata zan aiko mata, bayan na kashe wayar na soma raira kukan da ban san ta inda yake fito min ba, ina haka abokinsa ya shigo hakan ba ƙaramin ɓata ran Jibril ya yi ba saboda ƙananan kayana ne jikina kuma abokin nasa ya ganni, ya yi min masifa sosai har da dukana ya yi akan haka.
Muna cikin wannan halin Daddy ya yi rashin lafiya ya rasu, sai komai ya koma min sabo domin ganin Babu Daddy ya bawa Jibril damar azantar da ni da kalar azabar da yake so, sai dai bayan rasuwar Daddy sai Mahaifinsa ya kira ta wayarsa ya riƙa tambayata ko da wani abun ni dai ban taɓa faɗa masa ba.
lokacin da Ya Jamal zai koma Jos sai ya biyo inda na ke dan mu gaisa, kamar ƙaddara sai ga Jibril ya dawo a ranar na sha duka wai akan me zan shigo masa gida, ya yi faɗa da Ya Jamal sosai har Ya Jamal yake masa faɗa akan yadda ya maidani kamar wata tsohuwa saboda wahala.
Na sha fama a gidan Jibril ga shi baya son Sallah akan lokaci idan kuma na tasheshi sai ya yi ta masifa da ni, wata rana sai kamo tashar musulunci dake cikin receiver wa'azi wani babban malami yake akan irin azabar da ake ma masu wasa da sallah da kuma halin da suke shiga tun nan duniya, da gangan na cika murya dan yaji ashe kuwa saƙon ya isa dan tun daga wannan lokacin be sake wasa da sallah ba, wani lokacin da asuba har tashi na ke na tarar da ya riga ni tashi.
Abun da na lura da shi Jibril yana da rayuwar turawa saboda zama da ya yi a can tun yana da ƙurciya har girma, gaba ɗaya rayuwarsa ta turawace, sai dai a wannan lokacin Jibril ba ya cin goro ma balle taba, rashin ilmin addinin islamiya ne yake ta cutar da shi, idan ina karatun ƙur'ane ya kan natsu yana saurarena musamman da asuba, akwai ranar da ya taɓa tambayata wai waya koya min karatu manyan surori haka na ce makarantar islamiya, daga ranar kuma be ƙara tambaya ba, ni kuma na maida tashar wa'azi ta zamo abar saurarena kullum, sai dai hakan be hana shi zalunta ta ba, be kuma hana shi yin fasiƙanci da Aisha ba, be kuma sanya shi ciyar da ni ba, ni dai iya abunda zan iya shidunsa da shi shine kishi, Jibril yana kishina sosai dan ko abokansa baya bari su gan ni, idan kuma wani ya yi magana da ni ko ya nuna kulawarsa akaina ranar zai wuni yana masifa kamar ya cinye kansa.
Haka na bi na lalace ba ƙarfin yau bare na gobe, wata rana mahaifinsa ya aiko da mota aka ɗauko ni aka kaini gidansa, muka gaisa ya ɗauki wayarsa ya kira Jibril yana zuwa ya fara masa akan yadda ya ga na lalace sai Jibril ya yi tunanin ko na faɗa masa wani abun ne, bayan ya sallame ni da kuɗi mai yawa muka fito ni da Jibril na shiga motarsa muka kama hanyar gida.
Sai da ya tabbatar na yi nisa da gida sannan ya faka motarsa ya fisgoni da ƙarfi ya jefar a gefen titi ya koma cikin motar ya yi tafiyarsa ya bar ni a gurin. Haka na zauna a gurin har aka kira magariba sai da wani mutun ya zo zai wuce ya tsaya ya tambayeni na nemi ya taimaka min ya taimaka ya ɗauko ni a motarsa ya kawoni gida, a ranar sai da Jibril ya mareni kuma ya yi min duka mai kyau. Washe gari sai ga Momy ta zo gidan ta karɓu kuɗin da Daddynsa ya bani, ni dai na roƙeta akan ta raba biyu ta aikawa Baba rabi duk da nasan ba zata yi ba.
Jibril ya kan kirani da ko wane irin suna, idan na yi masa wani abu ba dai'dai ba sai ya ce min annoba ko baƙin maciji, yana yawan faɗar cewar ya fi son mutuwarsa da ni. Tun da ya aureni be taɓa bari naje gida ganin Baba ba, gidan momy kawai na yake kaini shi na kuma da dare yake kaini bayan ƴan mintuna ya ce na taso mu dawo gida.
Ranar da zamuje raka daddynsa zuwa airport ya mareni a bainar jama'a saboda kawai na zubar da ice cream ba da gangan ba, aiko ranar ya sha faɗa a gurin mahaifinsa har sai da ya raina kansa.
Bayan mun dawo gida ya wuce ɗakina na yi kuka har na gode Allah, daga nan bachi ya yi gaba da ni ina cikin bachin na soma jin ana shafani, hakan yasa na farka a firgice ina ihu, sai ya ji haushin ihun da na yi ya mare ni ya riƙa ya jefar ƙasa har sai da kaina ya bugu da madubin gadon, sai kuma ya taso ya doso inda na ke gadan-gadan ya dake fiskgata ya jefa saman gadon.
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
*Dedicated to My Asmee*
3⃣2⃣
A ranar Jibril ya maidani cikankiyar mace, da safe ni na taimakawa kaina na shiga banɗaki da kaina na haɗa ruwa na yi wanka sannan na ɗora da alwala na fito a wahalce na yi sallah.
Da safe be shigo ya tambayi ya na tashi ba duk da yasan halin da ya barni, ban fito daga ɗakin ba sai tara da rabi na safe kai tsaye na nufi kitchen sai na samu ya aje min makaroni da mai da tumatir da sauran kayan da zan sanrafa na dafa makaroni ɗin, cike da tausayin kaina na dafa makaronin ɗin ne na dawo ɗaki ina ta aikin kuka.
Haka nake wuni na kwana babu ruwan Jibril da ni a gidan, tun daga ranar kuma be saki kuni da sunan zamantakewar aure ba, idan baya nan gidan Ummu Faisak na ke zuwa na zauna musha fira ta haka nake samu na cika cikina da abincin gidanta, ban taɓa labarta mata irin yadda Jibril yake azabtar da ni ba, sai dai tasan irin zaman da nake a gidan ko da yaushe tana ƙoƙarin koya min abubuwan da zan yi na burge Jibril ko kuma na janyo hankalinsa akaina.
Ranar wata lahadi yana zaune gida na same shi a garden inda yake zaune yana hutuwa na risina har ƙasa na roƙoshi akan ya taimaka ya sake ni, amman ya ƙi har ma ya soma iƙirarin shi yanzu ya fara zama da ni, sai dai ya taimaka min ya ba ni makullin kitchen, daga ranar kullum abinci kala uku na ke girkawa wani lokacin ya ci wani lokacin kuma ko kallonsa ba ya yi.
Yana zaune falo shi da abokinsa ni kuma na nufi kitchen saboda miyar da na ɗora karta ƙone, ina nufar kitchen ina jin yadda yake faɗawa abokinsa wai Aisha tana da ciki and he's so happy and excited akan cikin da aka samu babu aure, ina kitchen ɗin na tarar da ni ya shaƙe ni yana tambayar ina Hijabina taya zan fito haka babu mayafi a gaban abokinsa, da kansa yaje ɗakina ya ɗauko min Hijab na saka sannan na wuce ta gaban abokinsa, har abokin yana zolayarsa wai shi yana ganin matan wasu amman shi ba a ganin nasa.
Ma samu sasauci sosai daga lokacin da ya bani makullin kitchen ɗin saboda kullum zan girka na ci, sai dai wata rana sai na gama girkin na ji bana so ko kuma na ji wannan na ke so bana son wannan abu a kaɗan sai amai, nan da nan zazzaɓi ya rufeni haka na kwashe kwana uku ina fama da rashin lafiya kamar zan mutu amman ko da rana ɗaya Jibril be taɓa shigowa ya duba lafiya na ke ba.
Ranar da na samu sa'ida na ɗaure na fito falo saboda na gaji da zaman ɗaki, ranar sai ya shigo ya sameni falo yadda ya ga na rame shi kansa ya bashi tsoro, da kanshi yana zo yana tambayar me ke damuna cikin nuna halin ko in kula saboda kawai na ce be damu ba.
Bayan na faɗa masa ya ɗauko min roba ya ce na yi fitsari sai kuma ya ɗibi jinina, ya bani wasu magunguna. Washe gari sai gashi ya dawo cikin gidan a rikice kai tsaye ɗaki na ya nufa.
“Ina kika samu ciki?”
Shine abunda ya fara tambayata fuskarsa na nuna tsantsar ɓacin rai da ke tare da shi, ni kuma na ɗago kai a hankali na kalleshi na maida kaina domin bana iya amsa masa.
“Ni ban shirya haihuwa yanzu ba, saboda haka ki san yadda zaki yi da cikin nan, daga yin abu sau ɗaya sai ace ciki ya shiga, zubar da shi zan yi ko kuma ya zama ƙarshen auren mu”
Ni dai uffan ban ce da shi ba ina ta aikin kuka, ban san miya aikata ba bayan kwana biyu ya shigo ɗakina ya bani lemu ina sha hankalina ya ɓace ban farko ba sai da aka kira assalati. A week later ya ɗauki ni zuwa gidan Daddynsa ashe ya kira Baba ni ban ma sani ba sai da muka isa, a falon ya yi min tozarci da ba zan taɓa mantawa da shi ba, ya tozarta ya yi min ƙazafi a gaban Mahaifina da mahaifinsa ya fiddo wasu hotuna na tsiraici tare da wani ya nuna musu kuma ya yi min ƙazafin cewar na aikata zina da wani a waje kuma da aurensa.
Ban iya cewa komai ba sai aikin kuka, har ga Allah ban san inda ya samo wannan hoton ba amman ni dai nasan babu wani namiji da wata mu'amala ta taɓa shiga tsakaninmu sai shi amman ya juya baya ya murje ido ya ce ba nashi ba ne, a ranar na riƙa hannunsa na riƙe shi akan ya karɓi cikin nan sai ya tureni yana faɗin taya zai karɓi cikin da ba nasa ba.
“Ni kan ban haifi ƴar iskaba kuma na san irin tarbiyar da na bawa ƴata”
Shine abunda Baba ya faɗa, Shi kuma ya sakeni saki uku mahaifinsa ya ce idan an saki mace a lokaci ɗaya kamar saki ɗaya ne dan haka ya maida aurensa ya yi haƙuri, sai kawai ya ce ya sani saki ɗaya ya sake ni saki biyu ya sake ni saki uku saboda kawai kar na koma gidansa sai Baba ya kama ni muka fito daga gidan, gidan aurana na koma na ɗauke duk abu na wa mai muhimmanci daga nan kai tsaye muka nufi tashar mota, sai dai ba mu kawo sokoto ba sai washe gari saboda ko da muka taso yamma ta yi sosai a zaria muna kwana, dawowata ta bawa kowa mamaki musamman da aka fahimcin ina da ciki sai aka fara zancen cewar ba aure na je yi ba iskaci naje yi wasu kuma su ce daman haka sai ya faru tun da Baba ya nuna kwaɗayinsa a kan abun duniya, har ma da masu cewa babu makarantar da na tafi. Baba ne yake ta dawainiya da ni shine ci na shana har na haihu da ƙarma ƙarama ya samo aka yanka rago ranar suna, yaro ya ci suna Muhammad Noor.
Bayan na haihu Inna ta ce ya faɗa masa sai azo a auna jininsa da na yaron amman Baba ya ce ba zai yi ba, ai namiji idan ya girma shi zai nemi ubansa, kuma yasan komai daren daɗewa sai Jibril ya dawo gurin ɗansa. Da wannan na zauna a gida ina rainon ɗana har ya cika shekara biyu da wasu watanni, a lokacin ne muka fara sabo da Bilal saboda gaisuwar arziki da take haɗa ni da shi, abotarmu da Jidda kuma ta ƙullu sosai, a gunta na ke jin labarin ai mahaifin Zinatu yana ɗaukar aikin local government har da masu ssce, haka na ɗauki takarduna naje gidansu Zinatu neman ta yi ma Babanta magana akan aikin amman sai ta tsaya tana kallona har ma da zolayata wai ina karatun da aka ce ina yi a waje har tana dariya, daga baya take faɗa min cewar mahaifinta ya ce sai masu degree yake ɗauka.
A hanyata ta dawowa daga gidansu na haɗu da da Faruk, tun daga unguwar yake bina har sai da na iso gida sannan ya yi min magana, ya kuma gabatar min da kansa ni kuma na faɗa masa ko wacece ni ban ɓoye masa komai.
Daga nan sai alaƙa mai ƙarfi ta ƙullu tsakaninmu har ta kai ga neman aure duk da ban so haka ba Baba da Inna suka buƙaci na aureshi tun da har ya nuna yana son aurena. Faruk mutum ne mai hallaci da kawaici yana so na tsakani da Allah, da kansa ya ce na daina cewa Noor babansa ya mutu saboda na yi masa ƙarya tun farƙo na faɗa masa cewar Baban Noor ya rasu ne, wasu mazan basa yarda mace ta yi aure da ƴaƴan wasu a gidansu amman shi kan ba zaka taɓa gane cewar ba shine ya haifi Noor ba, duk abunda ya kamata uba ya yi ma ɗansa shi yake ma Noor ba dan kuma baya da ƴaƴanba, domin yana da aure har da yara biyar, sai dai yana aiki ne a sokoto amman mutumen kebbi ne, acan yake zaune da duk familynsa, sai ya bar ni nan, ita kuma yana zuwa can inda take a kebbi. Iyayensa basa jindaɗin zama da matarsa irin matan nan da basa ragawa uwar miji da ƴan'uwanta ko kaɗan duk da ba guri ɗaya suke ba, wannan dalilin yasa mahaifiyarsa ta buƙaci ya maidani kebbi kusa da ita saboda ta yaba da tarbiyata a ɗan zuwan da muke ina gaisheta.
Sai ya tattara ya maida ni a kebbi