Showing 15001 words to 18000 words out of 138998 words
ta zauna ina kallin bakinta na san da akwai magana, sai dai tana tsoron furtawa ganin Habiba na kusa da ni. Murmushi na yi na ce
“Saki jikinki Jidda faɗa min ko minene ai Habiba kamar ni ce, dukan abunda kika sani nawa to Habiba ta rigaki saninsa, abunda duk na ke iya faɗa miki to Habiba ce ta fi cancanta na fara faɗawa, ni da ita abu ɗaya ne bama ɓoyewa juna abu”
Sai ta yi ƴar dariya.
“To ai ban sani ba ko gidan ba su ji ba ne”
“Minene?”
“Cewa aka yi wai kin mari Mustapha”
Habiba ta yi min wani kallo tana jiran ta ji abunda zai fito bakina.
“Ba wai ba ne na mare shi ɗin ɗazu”
Habiba ta riƙe baki
“Ashe da gaske ne”
“Na ɓoye ne saboda na ga kamar ran Inna ya ɓace”
Jidda ta kama hannuna.
“Ke ko miya kaiki? Miya haɗa ku?”
Shiru na yi ina tunanin irin amsar da zan bawa Jidda, domin bata san shine mutumen da ya yaga rigar mutuncin Habiba ba, a lokacin da abun ya faru ban labarta mata ko wanene ba kawai dai na faɗa mata cewar Habiba ta siyar da mutuncinta ta kawo dubu ashirin.
“Ba komai kawai wai dan Mai Napep ya tsaya a bakin hanya shine ya zo yana mana rashin mutunci, ni kuma na mare shi”
“Aka ce mari har uku wai, ai ƙara da kuka mareshi basa ganin mutuncin kowa a unguwar nan”
Na zaro ido
“Ɗaya ne kaji mutane da canja magana kuma, wai yanzu zancen nan har ya kai miki”
“Wallahi ina zaune gida aka kawo min shi, wai ƙawata ta mari Mustapha, ai ko ni kika mara sai zancen ya zagaye unguwa balle kuma Mustapha guda”
Dariya na yi, domin a yanzu duk wani tsoro da ke raina na ɗazu ya gushe. Labarin kamfanin na ɗaukowa Jidda ina ta faɗa mata yadda abubuwan suka, ita kanta da bata je gurin ba sai da abubuwan suka burgeta saboda yadda na tsaya na tsara mata komai kamar anyi a gabanta.
Har muka ci firarmu da Jidda muka suɗe Habiba bata saka bakiba, Jidda kuma bata bar gidanmu ba sai da ta yi sallah magariba sannan na rakata sannan na dawo.
Shikafar ɗazun na ɗauko na ɗumana na zuba mana muka zauna gaba ɗayan mu muka ci, ban da Inna da daman nata daban ake zuba mata balle kuma yau da ta ce ba zata ci ba. Muna cikin cin abincin nokiyar da ke gefena ta yi ringing, abun ka da wanda ya daɗe ba shi da waya tun da na saka layin ba a taɓa kirana da shi ba.
Number Waje ma'ana ba nunber nigeriya ba ce, cikin rawar jikina na ɗauka dan nasan mace ɗaya zata iya kira na da wannan layin wato Salima
“Hello Ƙawata”
Sai ta amsa min daga ɗayan ɓangaren.
“Ƴar'uwata, kin jefar da ni kullum ina kiranki bata shiga”
“Wallahi bana da waya ne a yanzu, wannan ma ara min aka yi na saka layina”
“Allah sarki ya gida? Ina Baba da Inna?”
“Sai dai Inna tana nan lafiya ƙalau, Baba kan Allah ya yi ikonshi”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, yaushe? Miya same shi”
“Rashin lafiya kwana biyu”
Na yi ƙarya saboda ba kowa zaka iya faɗawa dalilin mutuwar Baba ya gasgata cewar Baba be yi satar ba, duba da yadda muke fama da rashi. Bayan ta yi min gaisuwa ta yi ma Inna sannan ta yi ma Habiba, Sakina da Jamila sannan suka maido min da wayar.
“Kin rasa RAI BIYU masu muhimmanci Nawwara mutuwa mai ɗaci , kin rasa Abban Noor yanzu kuma Babanki Allah ya baki ikon ɗaukar wannan lamarin”
“Amin Salima na gode”
“Inshallah idan na dawo Nigeria zan zo har nan na yi miki gaisuwa”
“To Allah ya yarda”
Daga haka muka yi sallama, na amsa mata da to ne kawai ba dan na gamsu zata zo ɗin ba, duk tsawon zaman da muka yi da ita bata taɓa tako ƙafarta sokoto ba ai ba zata taɓa zuwa ba.
Da gudu Noor ya zo gurin yana ƙoƙarin karɓar wayar.
“Momy waya baki waya? Momy kira min Gwaggota Murja kin ji”
Haka yake idonsa idon ganin waya, baya da magana sai ta a kira masa Murja wato Ƙanwar mijina wacce ya shaƙu da ita sosai.
“An ya ma sun ji maganar rasuwar baban ku kuwa?”
Maganar Inna tasa na ɗago kai na kalleta.
“Ina zasu ji tun da ba a nan suke ba kuma babu waya a lokacin”
“Ya kamata dai kan ki faɗa mata”
“Bari na mata please Call me dan ba ni da kati gaskiya”
A take na aikama mata please Call, ko minti biyu ba a ƙara ba sai gata ta kirani, mun gaisa sosai sannan na bata Inna, ita ta labarta mata cewar Baban mu ya rasu, ta shiga ɗimuwa da kiɗima sosai, har da kukanta kamar Babanta ne ya rasu.
Bayan ta yi min gaisuwa ta faɗa min zata shaedawa sauran ƴan'uwan margayi Sadiq zasu zo har sokoto su yi min gaisuwa, duk ƙoƙarin dakatar da ita da na yi akan zuwan sai ta nuna min sam ba zai yiyu sai ta zo, ai daga sokoto zuwa Kebbi ba wani nisa ba ne. Sun daɗe suna waya da Noor sannan bashi yaranta suka yi magana sai ta kashe.
Takwas da rabi wayar Bilal ta shigo, ina ɗauka ya shaida min yana waje. Sai da na faɗawa Inna sannan na tashi na saka Hijab ɗina na fita. Jikingine da ƙofar gida na same shi, ina masa sallama ya amsa fuskarsa da murmushi har wani ƙyali take.
“Nawancy”
“Bilal”
Sai yasa dariya.
“Ina jin daɗin ki kira sunana yana mugun daɗi a bakinki”
Na yi murmushi ina rausayar da kai. Bayan mun gaisa ya bijiro min da fira cikin har da zancen marin da na yi Mustapha, sai na nuna masa ya yi min ba dai-dai ba ne shiyasa. Sai tara da rabi muka yi sallama.
WASHE GARI....
Yau kan ba laifi dukanmu mun tashi cikin walwala, Sakina da Jamila tuni suka wuce makaranta, Habiba ma shirin makarantar ta ke, ni kuma ina gyaran gida, Inna kuma na ɗaki tana bachin safe.
“Nawwara canjin kuɗin Koko yana nan ƙarƙashin fillo, Inna ta ce a siye ruwa”
Cewar Habiba tana tsaye riƙe da littafan makarantarta.
“Yau Fanfan ba zai zo ba ne hala?”
“Yau kwana biyu be zo ba, ruwan da muke amfani da su sun ƙare, ƙara a siya da wuri idan ma ya zo kin ga kaɗan kawai za mu ɗebo”
“Allah ya bada sa'ah”
“Amin na tafi”
Fitarta da kamar minti biyar, wata matashiyar yarinya ta shigo sanye da dogowar rigar atamfa da wani minafukin gyale a kafaɗa, sallama ta fara yi na amsa mata.
“Assalamu alaikum”
“Wa'alaikissalam”
“Sannu ina kwana?”
“Lafiya ƙalau”
“Dan Allah nan ne gidan Musa Kafinta?”
“Nan ne, lafiya?”
“Lafiya ƙalau, Sunana Shafa Ibrahim ni ƴar jarida ce ina aiki da jaridar Arewa a yau, tare da abokin aikina na ke ina son mu tattauna da iyalansa ne akan abunda ya faru”
Ta ƙarasa tana miƙa min katin shedarta.
CANDY ✍️
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
RIJF Mama A'i, ke da kika tafi ba ki yi sauri ba, mu da mika rage ba mu yi nawa ba. Allah kasa mutuwa ta zama hutu gareki Allah ya miki rahama ya gafarta miki kurakuranki. I will never forget you. Allah kayi mana kyakkyawan ƙarshe.
1⃣2⃣
Na kai hannu na karɓi cati na duba, sunanta ne da kuma hotonta a jikin catin hakan ya tabbatar min da cewar lallai ƴar jaridar ƙwarai ce. Na mayar mata da katinta.
“Ba mu san komai a kai ba, waya faɗa miki nan gurin kuma?”
“Jama'a ne suka kwatanta min, kuma na tabbatar min da cewar ƴan sanda suka duki margayin har ya mutu”
Na nuna mata ƙofar fita raina a ɓace.
“Fita ki bar mana gida, mutanen da suka labarta miki abunda ya faru ki je can su ƙarasa miki, mu bamu san komai ba”
“Haba Baiwar Allah...”
“Ki fita Wallahi ko na sa taɓarya na fasa miki kai yanzu”
Da gudu ta juya ta fice daga gidan. Ni kuma na cigaba da aikina zuciya na zafi har na gama gyara komai, ciki na shiga na samu Inna har lokacin tana bachi Hijabina na saka na ɗauki kuɗin da suke ƙarƙashin filo na fita neman mai ruwa.
Karo na ci da Dpo dake tsaye jikin motarsa yana kallon ƙofar gidanmu, ban gama tabbatar da shi ɗin ne ko a'a ba saboda yau a cikin kayan gida yake.
“Assalamu Alaikum Malama”
A maimakon na amsa masa sai kawai na watsa masa wata muguwar harara.
“Ni ba gurinki na zo ba, matar gidan na ke son magana da ita”
“Bachi ta ke”
“Ki taimaka ki tashe ta kuma ki nema minlH izinin shiga cikin gidan”
“Saboda?”
Ya gyara tsayuwarsa yana kallona fuskarsa ba yabo ba fallasa.
“Na ga dai ke ba ƴar jarida ba ce, be kamata ki tsare ni kina min irin waɗannan tambayoyin ba, beside ni ba gurinki na zo ba gurin Inna na zo”
“Gida mallakinmu, mahaifiya bachi take baƙincikin kashe mahaifinmu da ka yi take ragewa saboda hawan jini”
Ban tsaya jiran abunda zai ce ba, na cigaba ta tafiyata. Sai ya zagayo ta gaban motarsa ya sha gabana, cikin ɗaga murya ya fara magana.
“Miyasa kuke rayawa zuciyarku cewa ni na kashe mahaifinki? Mi mahaifinki ya yi min da zan kasheshi? Idan na kashe shi wace riba zan ci?”
Nima cikin zafin rai na zaburo masa.
“Saboda zalincin ƴan sanda, yayarka ta laƙaba masa sata bayan kuma be sata ba, kuka yi ta dukansa har sai da kuka kasheshi akan kawai sai ya amsa laifinsa, wannan ba halinku ba ne? Saboda yayarka tana taƙamar kai dpo ne yasa kuka wulaƙanta mana mahaifi cika tozarta shi sannan kuka ɗauki gawa kuka kawo mana, yanzu kuma kana raina mana hankali har kana wasa da hankalinmu”
Ya matso kusa da ni ya nuna ni da yatsa yana magana cikin jin zafin kalaman da na yi masa, har haƙoransa na ƙasa na haɗuwa da na sama yana cizonsu tare da zaro min ido.
“Karki sake saka bakinki a akan aikina, karki sake yin furucin akan abunda kika jahilta, i hate nonsense, na zo nan ne dan na faɗa muku karku kuskura bada bayanin mutuwar mahaifinku ga ƴan jarida”
Na yi baya-baya ina hawaye, tare da murmushin da ya fi kuka ciwo.
“Kamin ta zo nan ashe sai da ta bi ta gurinka, ka yi nasara ban faɗa mata komai ba, amman yanzu kan ni zan tara ƴan jarida da kaina na labarta musu irin zaluncin da kuka mana, wato so kuka a rufa muku asiri kar kowa ya ji ko? Ta yadda muma zaku samu damar ɓatar da mu, Wallahi Allah ba zai barku ba azzalumai macuta-”
Ya ƙara matsowa kusa da ni har sai da na matsa baya.
“Ki tara ƴan jarida, ki faɗa muku ƴan sanda sun kama mahaifinki sun masa duka har ya mutu, za su tambaye ki dalilin hakan, kuma ki faɗa muku komai karki ɓoye, ni da ke za a ga waye zai ji kunya, idan ba ki yi haka ba to baki haifu ba!”
Yana kaiwa nan ya haɗa hannunsa na dama da na hagu ta taɓa saitin fuskata, har sai da na rufe ido. Sannan ya buɗe motarsa ƙirar 406 ya shiga ya fisgeta kamar zai tashi sama, ko da na ɓuɗe idona ƙurar motar kawai na gani hawaye ya sauko daga idona, lallai wannan shi ne a dakika a hana kuka, kuma a mareka a ƙwace maka jaka!
Kasa zuwa kiran mai ruwan na yi saboda kuka da ya ci ƙarfina, na koma cikin gida da sauri. Bana son na tashi Inna balle har ta ga hawayena hakan yasa na shige ɗakinmu na kwanta saman tabarma, na ci kuka na sai da na ƙoshi sannan bachi ya yi gaba da ni.
Motsin shigowar su Habiba ne ya tasheni daga dogon banchin da ya ɗaukeni, babu komai a mafarkina sai wacan tashin hankalin da ya faru, Baba ne kawai na ke ta gani sai kuma irin zamantewar da muka yi a gidan kamin rasuwarsa.
Ko da na fito na samu Inna ta farka har suna fira da Habiba ma da ke cire safa.
“Nawwara kin tashi?”
Inna ta tambaya tana kallona, sai na zauna bakin ƙofar ina amsa mata.
“Eh ashe rana ta yi”
“Tun ɗazu su Noor suka dawo na ce kar ya tasheki kin gaji da yawa, ƙara ki samu bachi ki ɗan huta”
Kallo ɗaya Habiba ta yi min ta ɗauke kai, kamar ba ta ganni ba, hakan ya karatar da ni da akwai wani abu a ƙasa, sai dai ban ce da ita komai ba na tashi na ɗauki bula na shiga banɗaki, bayan na fito na yi alwala na shiga ɗakinmu dan Sallah.
A ciki na sameta tana ɗaura zane, naje kusa da ita na tsaya.
“Habiba kamar akwai abunda ya ke damunki?”
Ta ɗaga kai ta kalleni a maimakon ta yi magana sai ta kawar da kai ta soma magana.
“Nawwara ɗazu da zanje makaranta na haɗu da Mustapha, na tsayarda shi na bashi haƙuri akan abunda kika masa, sai yake tambayata ke yayata na ce eh, shine ya ce wai tun da yake a rayuwarshi wata mace bata taɓa ɗaga hannu taareshi ba ko da uwarsa ce sai ke, akan me zaki mareshi, bayan da ke yake magana ba, kawai ya buga motarsa ya yi tafiyarsa. Nawwara miyasa kika mareshi? Zaki ƙara ja mana matsala”
“Shiyasa kike jin haushi na? Babu abunda zai faru Habiba, kuma bari kiji na faɗa miki ko da Mustapha zai yanka ni ya dafa namana ya soma ya ci, ba zan bashi haƙuri ba, ke ma kuma kinyi kuskure da kika tunkare shi kika ba shi haƙuri wannan ba halinki ba ne Habiba”
“To ya kike son na yi? Bamu da wani gata sai na Allah mutane kamar jiranmu suke su yi mana abu, yanzu idan wani abu ya sake samun family mu ban san ya zan yi ba, Allah kasa ni ce zan fara bin Baba na gaji da wannan rayuwar”
Ta fashe da kuka. Ni kuma na riƙeta muka zauna tare ina rarrashinta.
“Babu abunda zai sake faruwa inshallahu, na miki alƙawari, share hawayenki kar Inna ta ji”
Ta ɗaga min kai tana share hawayen.
Haka muka zauna cikin jiran tsamanin abunda zai same ni daga Mustapha domin na san ba zai bar ni ba, Habiba ma kullum cikin tunanin wannan abun take, bata ƙaunar ko waje na leƙa saboda gani take kamar zan iya haɗuwa da shi ya yi min wani abu. Wasa-wasa muka kwashe sati uku babu abunda ya faru sai dai tunanin abun zai faru ya hanani sukuni ni da Habiba, a cikin satin ne su Murja da Hajiya Umaima da Hasana suka zo min gaisuwa tun ɗaga Kebbi. Wato Yayar tsohon mijina da kuma ƙannensa, mahaifiyarsa kuma ta yi min aike ni da Noor. Ba su kwana ba ranar da suka zo ranar suka koma bayan mun yi ma Noor tsaraɓar kayan maƙulashe da kuma tufafi, Inna kuma suka kawo mata atamfa da buhun kishinka ƙarami.
Ranar da suka kwana biyu da tafiya ina zaune tsakar gida misalin ƙarfe goma sha ɗaya na safe wayata ta yi ƙara alamar saƙo, ban kulata ba dan na daina ɗaukin aikin a yanzu tunani ba zan samu ba, tun da kullum ina sa ran ganin saƙon kamfanin amman sai na samu saƙon mtn. Sai da na gaji da kwancin da nake na tashi zaune ya miƙa hannu na ɗauki wayar da ke kusa da ni ina dubawa. Ina ganin sunan Kamfanin One-On-One jikina ya fara rawa, cikin zumuɗi na buɗe saƙon Congratulations na ga an rubuta a sama.ban iya tsayawa karanta sauran ba na buga tsalle ina ihun daɗi.
WHO IS READY FOR THE NEXT CHAPTER?
I can't wait to see Nawwara in One-On-One limitless company. 😍
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
1⃣3⃣
Ihun da na yi ne yasa Inna fitowa daga ɗaki da sauri tana kallona.
“Na samu aikin Inna sun ɗauke ni”
Murmushin haukan da na ke ta yi, tana girgiza kai for first time bayan rasuwar mahaifinmu yau na ga murmushin Inna. Zuwa na yi da gudu na rumgumeta ina ta murna kamar babu abunda ke damuna. Haka na wuni cikin farinciki da jindaɗi kamar wacce aka yi ma kyautar kujerar makka. Ban san farincikina kaɗan ne har sai da Habiba ta dawo na sanar mata da labarin sai ta yi kamar zata haɗe kanta dan murna kai kace ma ita ta samu aikin ba ni ba, a ranar Habiba bata iya cin abincin rana ba dan tsananin murna, da maraici ta siye alawa da kuɗin Inna ta yi sadaka. Haka ta ke nunawa kulawarta da damuwa a duk lokacin da wani abun ya sameni, ta kan zauna ta labarta min abunda Inna bata sani ba, zata iya ɓoyewa Inna abu amman ni bata ɓoye min ba, mutune har mamakin yadda muke son junanmu suke, ganin ita take bina amman bama taɓa samun saɓani, ko ma mun samu tun anjima kaɗan zanje na rarrasheta ko kuma ita ta zo ta bani haƙuri ko da kuwa ni ce bana da gaskiya, irin tsabanin da ake samu tsakanin mabiyi da mabiyi ni ban cika samunsa da Habiba ba, muna son junanmu sosai, ko ciwo ɗayan mu yake sai ɗayan ya ji kamar ya cirewa ɗan'uwansa ya sakawa kansa.
Lokacin da Baba na da rai idan ya tashi zolayarmu har cewa yake yadda muke son junanmu bama sonsa haka, wani gurin ma idan mukaje ba dan kamanni ba da mutane za su ce Habiba ƙawata ce ba ƙanwata ba.
Ba zan iya misalta irin son da take yi ma Noor ba, tun da na haifeshi ita ce da ɗawainiyarsa har ya kawo yanzu, babu kuma wanda ya isa ya nuna masa ɗan yatsa a unguwarmu ko ma a cikin gidanmu ni kaina ban isa na hukunta Noor ba indai a kan idon Habiba ne. Ni kaina shaƙuwar ta kan ba ni mamaki, wata ƙila dan akwai tazarar shekara bakwai a tsakaninmu.
Duk farinciki da ɗaukin aikin da nake idan na tuna Baba ba ya raye sai na ji babu daɗi, na so ace na samu aikin yana da rai na san zai yi farinciki sosai, sai dai kuma ƙaddara ta riga fata abunda Allah ya rubuta dole shi zai samu bawa. A daren ranar da na samu aiki sai ga Bilal ya kirana ni a waya na yi zaton zai ce na fito ne sai ya ce na aiko masa Noor yana bakin ƙofar gida,