Showing 21001 words to 24000 words out of 138998 words

Chapter 8 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

733

bata daɗe ba ta dawo da kuɗin wai sunje masallaci.
Kayan jikana na tuɓe na koma gaban murhu ina hura wuta domin ɗora girkin rana, har na yi girkin na gama kuka nake a boye saboda bana son Inna ta gano ina kuka hakan zai raunana mata zuciya kuma dole zata tambayeni dalilin kukan wanda ba zan iya faɗa mata ba.
Bayan na gama na shiga banɗaki na yi wanka tare da kuka a can, domin a nan babu wanda zai san da damuwata, bayan na fito na raba abincin na sake aikin Sakina ta je ta siyo mata maganin. Da kaina na ɓalla na bata ta sha na zuba mana abinci sai ita ta kasa ci saboda zazzaɓin ya rufeta sosai, jikinta ya yi zafi sosai. Ni kaina kasa cin abincin na yi, sai mutuwar Baba ta dawo min sabuwa, da ace ƴan sanda nan ba su masa duka ba, da be mutu ba da Habiba da ni da Inna duk ba mu shiga wannan halin ba. Bana son kowa yasan kukana hakan yasa na ɗauki buta na shiga banɗakina na ci kukana sao da na ƙoshi sannan wanke fuskata na fito, a lokacin ana kiran sallah la'asar.

Ba laifi Habiba ta samu sauƙi bayan shan maganin da ta yi, da muƙa gama sallah magariba ba har waje ta fito muna ɗan taɓa fira da ita, har ma ta ci ciwon masarar da na yi, hakan ba ƙaramin faranta min rai ya yi ba, gar na samu sakewa na labartawa Inna zancen Bilal, babu irin ruwan albakar da Inna bata sa mishi ba, Habiba ma sai yabonsa take. Inna ce ta cilasta ni kiransa a waya na sanar masa tana son ganinsa.

Bayan Sallah isha'i ya zo Inna tasa na shigo da shi har cikin gida ta yi masa godiya, bayan mun fito ni nake masa godiya duk da nasan cewar ba da sanin mahaifiyarsa ya yi mana wannan abun ba, da ba zata bari ba domin ta ƙi jinin ta ganmu tare ma balle kuma har kyauta ta shiga tsakaninmu, mun daɗe muna fira shi sannan muka yi sallama.

Bayan na dawo nake labartawa Inna yadda gurin aikin yake da kuma irin ƙa'idojinsa sai kuma zancen yadda kace min Shugaban ya ke, ta yi murna sosai ita da Habiba sun ƙarfafa min gwuiwa kuma suka min addu'ar samun nasara.
Washe gari naje na sanar da Jidda zancen samun aikina, ita ta yi murna sosai kusan sai na ce ta fini farinciki, haƙiƙa Jidda ta wuce ƙawa a gurina mun zama ƴan'uwan juna ni da ita, mun sha fira sosai yadda na ke labarta mata gurin aikinmu ita abun ma burgeta ya yi, wai ban sanar mata da wuri ba da ta kai takardunta na diploma sun ɗauke ta aiki a guri.

Sai yamma na baro gidansu bayan na haɗu ni da kwanon shinkafa da miya, abincin da na ke marmari.


*** *** ***

MONDAY MORNING...

Hankalina ya kwanta sosai a kwanan biyu da Habiba ta yi bata sake ko da ciwon kai ba, hakan ya gamsar da ni lallai malaria ce take damunta.
Dukan mu shiri muke bayan mun gama karyawa, ni ina shirin zuwa gurin aiki su kuma suna shirin zuwa makaranta, ban shafa hoda ba bayan na shafa mai, domin kawaliya bata dame ni ba, balle ni da zan fita tun 6:30am. Uniform ɗin na ɗauko na cire daga cikin leda, dogon wando ne ash color da farar riga, sai kuma wata ƴar ƙaramar riga marar hannu da za a ɗora saman wacan farar rigar ita ma ash, sai da na gama kallo ni da Habiba sannan na saka.
Cas na fito kamar wata ma'aikaciyar banki musamman da na saka baƙaƙen takalmin nan masu kama da cover shoes.

“Wow Nawwara kin wanku”

Cewar Habiba tana kallona, ni kuma na yi dariya ina mai jindaɗi a raina. Ba Habiba kaɗai ba har Noor da Inna sai da suka yaba ni, ni kaona na san shigar ta yi min kamar wata ma'aikaciya, idan ba wanda ya sani ba babu wanda zai ce aikin Mopping zan yi. Wata ƴar ƙaramar baƙar hula na ɗauka na saka a kitson da ke kaina, sannan na ɗora ƙaton Hijabi yaɗi huɗu da rabi na saka, a gaggauci na fito daga gida gudun kar na yi lattti gashi yau ne farkon zuwana, duk yadda Habiba ta so na tsaya mu fito tare ƙiyawa na yi gudun kar na ɓata lokaci. Sai da na kawo bakin titi sannan na tuna da hoton da aka ce na kawo, da gudu na koma gida na ɗauko na sake fitowa ina ɗan jin kunya saboda mutane da ke kai da kawo a unguwat sun ɗan fara fitowa, duk da yake ba za'aga uniform a jikina ba amman sai na samu kaina da jin kunya saboda ban saba saka wando na fita da shi ba.

Ko da na isa kamfanin bakwai sauran minti biyar, yau kan sun tare a bakin ganin suna ɗan bincikata, sai na faɗa musu komai har ma na nuna musu uniform ɗin da ke jikina da kuma katin sheidata, sannan suka bar ni na wuce. Kamar yadda Bilal ya nuna min sai da na fara isa na saka sunana da lokacin da na shigo da kuma rana sannan suka nuna min gurin da zan aje Hijabi da wasu kaya idan na zo da su, na nufi gurin na na cire Hijabina na aje a lokar da suka ba makullinta, na samu kaina da jin kunya sosai ganin babu komai a jikina sai uniform ɗin da kuma ƴar ƙaramar hular da ke kaina, sai da na ɗan jima tsaye a gurin sannan na juyo na fara takowa, sai ɗaya ɗaga mutanen da ke reception ya ɗaga hannushi yana nuna min hular da ke kaina, a dole na juya na je na cire na aje, na juyo ina wani taku kamar wacce bata son saka ƙasa babu komai a tattare da ni sai kunya, shi kanshi ya lura da yanayina, hakan yasa ya sakar min murmushi, nima na sakar masa kaɗan idona a ware, ina kalle-kalle ala-ala na ke kar naga wanda na yasan ni har na nufi Lifted na danna ta buɗe na shiga sai na danna number 3 ta rufe ta soma tafiya da ni, zuciyata sai bugawa take da ƙarfi irin bugarwa nan na ɗoki da kuma tsoro a lokaci ɗaya.
Muna isa number 3 ta buɗe na fito sai na samu masu irin uniform ɗina suna ta aikin gyara gurin, ganin duk mata ne yasa ni na ɗan saki jikina na nufi gurin da aka nuna min da zan ɗauki kayan aikina. A ciki na tarar da wata yarinya mai far'a da son mutane domin ita kaɗai ce ta amsa min sallamar da na yi har ta yi min kyautar murmushi.

“Da alama ke baƙuwace a nan”

“Haka ne, yau zan fara”

“Haba shiyasa”

“Mi kika gani hala?”

“Naga kin yi sallama ne, ai a nan ba a sallama ba a gaisuwa saboda mai Kamfanin baya buƙata, idan kika ga ana fira da juna tau angama aikine ko kuma an fita can waje”

“Tau shi kuma haka yake”

Ta yi dariya tana nuna min camera.

“Ki yi a hankali, Camera tana ɗaukar komai”

Security camera ce daga gabanmu tana ɗaukar komai, sai na yi saurin gumɗe bakina na ɗauki kayan aikina na yi gaba.
Na ji wuyar aikin sosai wata ƙila saboda ina farkom farawa ne, ko kuma saboda ɗakunan da aka haɗani da su suna da girma sosai, ga kuma gyara kofuna da jerawa bayan na gama ƙirgasu, sai da na gama sannan naje gurin da ake rubutawa na rubuta ko nawa na tarar sannan na nufi gurin aje kayan aikin na aje, na aje na kaiwa mutumen jiya wanda yace na kawo mashi ƙananan hotona, ɗaya ka karɓa ya saka a file sannan ya karɓi ɗayan na saka min a katin sheidata na rataya a wuya sannan ya ce min.

“Idan kina da account ki rubuta a nan, idan kuma baki da shi zan cika miki wata takarda sai ki riƙa karbar albashinki hannun kashiya”

“Gaskiya na daɗe ban yi amfani da shi ba, ina tunanin yanzu ma baya aiki”

Wata takardar ya ɗauko ya yi rubuce-rubuce sannan ya bani na saka hannu sai ya maida takardun ya aje, ya ce

“On 25 zaki riƙa zuwa gurin kashiya kina amsar kuɗin albashinki 12k”

“Tau na gode”

Na juyo duk da ban tambaye shi iya kashinyan yake ba, na fito daga gurin gaba ɗaya. A ƙaton agogon da ke reception na ga 12:14pm, lallai na daɗe ina aikin nan, sai da na saka hannu kuma na rubuta lokacin da na gama aikin sannan na nufi gurin da Hijabi yake na ɗauka, ina sakawa na ji mutun a bayana.

“Nawancy”

Da sauri na juyo na kalleshi.

“Ka ganni ne kamin na saka Hijab?”

Sai kawai ya ƙyalƙyale da dariya ya ɗora min ɗari biyar a lokar dana ɗauki Hijabina.

“Allah dai ya bar min ke, ga wannan ki hau Napep, a sauka lafiya”

Sai ya kama gabanshi ya yi tafiyarsa. Cike da kunya na fito na daga cikin kamfanin ita tunanin anya zan iya aikin nan zuwa?

“Sannu ƴar'uwar yau nima na ti latti gama aiki”

Na kalli mai min maganar da ke gefena na dama fuskarta ɗauke da murmushi, yarinyar ɗazun ce, sai dai wannan karon ita ma tana sanye da Hijabi, hakan yasa nima na yi mata murmushi.

“Da wuri kike gamawa kenan?”

“Eh gaskiya ten na ke gama aikina. Sunana Amina ke fa?”

“Nawwara”

“Suna mai daɗi”

Sai duk muka yi dariya, muna ta ɗan taɓa fira da ita kamin motar da ta wuce mu ta dawo dai-dai mu ta tsaya.

“Nawwara”

Jin muryar Zinatu yasa na yi saurin kallon motar, ita ce hakimce a motar idonta sanye da baƙin gilashi.

“Zinatu Ya kike?”

A maimakon ta amsa min sai kawai ta jefo min tambaya.

“Me kike a nan?”

“Aiki”

“Aiki aiki aiki wane irin aiki?”

“Mopping”

“Nice amman yau kika fara ko?”

“Eh”

“Good kowa zai ji muna aiki a guri ɗaya Sai dai ba level ɗaya ba, and people may not know the different, congratulations”

Ta tashi gilashin motarta ta kunna kai zuwa harabar da aje motoci. Maganar ta sosa min rai har Amina ta lura da hakan.

“Kin santa ne hala?”

“Eh tare muka yi primary school”

“Allah sarki”

Kamar ta ce wani abu sai kuma ta yi shiru, muka cigaba da tafiya. A gurin hawan Napep muka rabu ni na ɗauki hanyar gidanmu ita ma ta kama hanyar na su gidan.

Kamar kullum a inda aka sake sauke ni na sauka na ƙarɓi canjina na nufi gida, zuciyata cike da tunanin kalamin da Zinatu ta yi min, bana son fassarata da wata fuskar da kuwa da kasancewar na san halin na tsanar mutane irina da ta yi wato talakawa, haka kawai na samu kaina da faɗuwar gaba wata ƙila na tunanin da nake ne, sai da na shiga gidanmu na fahimcin faɗuwar gaban bana tunani ba ne na abunda zan tarar ne.

______________
SHARE, COMMENT AND VOTE.
Sauran na ji wani ya ce short page ne na buge masa baki 😎

BEST REGARDS 🌹
Khadeeja Candy💜..
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


1⃣5⃣

Habiba ce kwance tsakar gida amai na gefenta da alama yanzu ta gama shi, domin Inna ta ɗauki makwashi da tsintsiya ta je ɗebo ƙasa. Da sauri na ƙarasa kusa da ita jikina a mace na dafata.

“Sannu Habiba mi ke damunki”

“Wallahi kaina ne ke ta ciwo ban ma iya dawowa daga makaranta ba sai da malaminmu ya kawo ni, sai faman aman na ke, kuma bakina babu daɗi”

Samun kaina na yi da kuka marar sauti, hawaye na bin fuskata kamar babu gobe. Na samu kaina cikin wani irin tashin hankali wanda ban taɓa samun kaina a ciki ba.

“Ai zata samu sauƙi ina jin malaria ce bata sake ta ba”

Inna ta faɗa ganin ina kuka, sai faman rufe aman take.


“Allah yasa malaria ce, Allah yasa ta tabbata malaria ce ba ciki ba”

Maganar ta fito daga bakina kamar antseni. Hakan yasa Inna ta kalleni

“Nawwara, akwai abunda ya kamata na sani ne?”

Na yi saurin girgiza mata kaina hankalina a tashe.

“Babu babu komai”

Ta saki tsintsiyar hannunta, ta kalli Habiba da ta soma kuka daga inda take kwance.

“Akwai abunda kuke ɓoyewa ne?”

Na girgiza mata kai alamar a'a. Amman bata yarda ba. Ta soma ƙirga da hannunta.

“Tsaya dakata, Habiba tana da ciki kenan?”

Habiba ta yi saurin tashi zaune ta matsa gefena kamar zata shige jikina tana girgiwa Inna kai.

“A'a Inna”

Ta faɗa cikin kuka, kamar yadda nima na ke kuka. Sai ina ta kalleta idonta cike da hawaye ta nunata da yatsa.

“Kina da ciki Habiba, na lura da haka domin yanayinki ya canja gaba ɗaya, amman saboda karna munana zato a gareki yasa ban bari zuciyata ta ƙawata min wannan ba, ashe yaudara kuke ke da ƴar'uwarki, na shiga uku na lalace ina kika samo shi?”

Ta ɗora hannu saman kai ta nufi ɗaki tana kuka. Hakan yasa na cire Hijabin da ke jikina na aje a gurin tare da wayata na rufe mata baya. Safa da marwa na tarar tana yi a cikin ɗakin tana kuka, kamar jira take na shigo sai ta rufeni da maganganu marar daɗi.

“Kun cuce ni Nawwara, wannan ba tarbiyar gidan nan ba ce, ina kuka ɗaukota? Kun ƙara shafa mana baƙin fenti acewa mahaifinku ɓarawo ku kuma a kiraku ƴan iska, wayyo Allah na”

Ta faɗi tsakar ɗaki tana kusar kuka. Kusa da ita na ƙarasa na ɗafa ina kuka na ce

“Wallahi ba mu watsar ba Inna, ita ma yaudararta aka yi”

“Waya yaudareta? Faɗa min waya rusa mana ɗan farincikin da ya rage mana?”

A nan na feɗe mata daga biri har wutsiya akan abunda ya faru, sai dai ban labarta mata cewar Mustapha ne ya aikata mata haka ba, saboda bana tabbacin cikin nasa ne ko ba nasa ba ni dai abunda na sani ba shi kaɗai na ya yi lalata da ita ba, nasan kuma duk na faɗa mata cewar shi ne zata iya zuwa ta samu iyayensa wanda hakan na san ba zai mana daɗi ba, domin zasu iya ɗauka ko wane irin mataki a kan ɗan su ƙwalli ɗaya da suke ji da shi.

Can ƙasa-ƙasa na hango muryar Inna tana cewa.

“Habiba ta ci amanata kuma ta ci amanar kanta, ta zubarda ƙima da duk wani mutuncin da yake gidan nan, a yau na yi nadamar haihuwarta, baƙincikinta zai kasheni, ni ma nice na tafi ba mahaifinku ba, Allah be ƙaddara ya ga wannan abun kaico da wayyo a rayuwarsa ba sai ni, Habiba kin cuce mu...”

Duk wannan furucin da Inna take akan kunnuwan Habiba saboda tana jikin ƙofa tsaye ne, sai da Inna bata iya ganinta saboda ta bata baya ne. Muna haɗa ido da ita sai ta bar jikin ƙofar ta nufi ɗakinmu. Da sauri na tashi na bita saboda irin hawayen da na hango suna zuba a idonta.

Ko da na shiga na tarar tana ta saurin cire uniform ɗin jikinta ta saka wasu tufafin. Jin motsina yasa ta juyo da sauri ta kalleni.

“Nawwara guduwa zan yi, ba zan zama dalilin mutuwar Inna ba, ba zan rasa Baba kuma na rasa Inna ba-”

Ta juyo ta cigaba da haɗa kayanta. Ƙarasa na yi kusa da ita ya miƙar da ita tsaye na kama hannyenta da ke zafi sosai saboda zazzaɓi na riƙe gam, ina kuka kamar yadda itama take yi har ɗayanmu baya iya yiwa ɗan'uwansa magana.





GOOD NIGHT.... 🤧
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


1⃣6⃣

Haƙiƙa akwai ƙurciya a rayuwar Habiba, yana ɗaya daga cikin dalilin da yasa ta aikata abunda ta aikata, wanda take tunanin kamar mafitane, sai gashi ya zame mana matsala, yanzu kuma tana ganin kamar guduwa ta bar gida shi ma mafita ne, ni ko nasan duk yarinyar da ta gudu ta bar iyayenta lallai tana tare da na sani da kaico a rayuwarta.
Ba zan bari ƴar'uwata ta aiwatar da wannan ƙudirin nata ba, ko da kuwa haka yana nufi salwantar rayuwar mahaifiyata ne, ba zan bari ta sake aikata wani kuskuren ba. Ƙoƙari nake na tsayarda kuka ta yadda zan ƙarfafa mata guiwa da rarrashi amman hawayen da ke min zuba sun ƙi bani haɗin kai.
Idan har ban yi ƙarfin halin shiga tsakaninta da wannan kuɗirin nata ba, lallai zamu iya rasata wanda na san hakan zai iya sama sadiyar rasa Inna.
Hannayenta na saki na share hawayena ina kallonta, cike da ƙarfin hali na ce

“Babu inda zaki je Habiba, irin wannan tunanin na ki ne yaja miki kika jefa mu cikin wannan halin, yanzu kuma zaki sake aikata irinsa? Kina tunanin aikata wannan abun shine mafita? Ba zai canja komai ba, sai dai ma ya ƙara ɓata ran Inna har ta kasa yafe miki, mu kuma ki ja mana ɓacin suna, haka kike so?”

Ta girgiza kai alamar a'a, muryarta a shake ta ce.

“Ta ce ta yi nadamar haihuwata ni ce ajalinta, ba zata yafe min ba”

Hannu na kai na sake riƙe hannayenta.

“Zata yafe miki Habiba, ni ma uwace na san halin da Inna take ciki, akwai zafi idan wani abu ya samu ɗanka musamman mace, idan wani abu ya sami Noor bana iya yafewa kaina, bana iya controlling kaina bana iya juriya, kin san saboda me? Saboda Ina ƙaunar Noor, a duk faɗin duniya babu wacce zata gwadawa ɗa so kamar uwarsa, duk abunda Inna ta yi miki saboda tana ƙaunarki ne ke kanki kin san Inna tana son ki, karki yarda ki gudu idan har kika gudu babu ni babu ke har abada!”

“Ba zan gudu ba, ba zan je ko'ina ba na miki alƙawari, ko da kuwa Inna zata yanka ni ne”

Ya faɗa cikin kuka. Sai na zaunar da ita ina share mata hawayenta, tare da yi mata wasu kalaman da zasu ƙarfafa mata guiwa.
Ban bar ɗakinba sai da na tabbatar kuka da take ya tsagaita, sannan na fito na shiga ɗakin Inna.
Gurin da barta a nan na sameta sai wannan karon tana daga kwance ne, gurin da fuskarta take ya jiƙe da ruwan hawaye kamar an zuba ruwa a gurin. Daga inda na ke tsaye na soma mata magana ciki da ƙarfin hali.

“Habiba ta aikata abunda ta aikata ne saboda tana tunanin kamar hakan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login