Showing 90001 words to 93000 words out of 138998 words
zaki iya zaman aure da shi ba saboda ba shi zuciyarki ke so ba, kuma kaddara ba zata barku ku yi zaman aure ba, ya kamata ki yi tunani karki aikata abunda zai cutar da ke”
Tana gama fada min haka ta kalli Inna ta ce.
“Ni na tafi Allah ya ba Noor lafiya”
Binta Inna ta yi suka fita tare suka barni a dakin ina faman hawaye, ba zan iya bari kalaman Mama Turai su yaudari zuciyata ba, tabbas ni dai na san Bilal na ke so kuma shi zan aura, ba zan zargi Inna ma domin nasan bata cikin irin mutanen nan da ke son yayanta su auri mai kudi, amman wani lokacin ina ganin kamar saboda Jibril yana da kudi ne yasa take son shi, duk da kasancewar Bilal ba talaka ne talak ba, yana da aikinsa kuma ya yi karatu familynsa ma suna da rufin asiri, amman zuciyar Inna ta fi karkarta gurin Jibril.
Motsi Noor ya sake yi a karo na biyu har yana kokarin bude idonsa yana motsi da hannu.
“Momy... ”
Na yi saurin share hawayena na kama hannunsa.
“Na'am Noor sannu ka ji”
“Momy da zafi sun jimun ciwo sosai”
“Kyalesu Allah ya isar maka ya baka lafiya”
Ya kalleni da idanuwansa da suka yi fari sosai, sai kuma ya kalli gefena.
“Momy na yi mafarkin Babana ya zo nan”
Gabana ya fadi.
“Wane Baba kuma?”
“Wanda ya rasu”
Ajiyar zuciya na sauke.
“Wanda ya rasu ai baya dawowa Noor, mafarki kawai ka yi”
Na shafa kansa sannan na mike na fita dan kiran likita.
JIBRIL POV.
Da taimakon Allah ya isa gida, zuciyarsa ta yi masa mugun nauyi, ko parking din kirki be yi ba ya fito ya nufi main house jiri na dibansa, yana shiga falo na fadi a bakin kofa yana tari a wahalce gubar da ya taba ci ta taso masa ta hadu da dattin cocaine dake cikin huhunsa (lung) sai aman jini, har idanuwansa suka canja kala kamar ba zai rayu ba, gashi falon babu kowa sai shi kadai. Tun yana iya gani har ya koma yana gani dishi-dishi sai kuma numfashinsa ya soma nisa hankalinsa ya ba ce 6at.
Ko da ya farka an dora masa kyalle mai sanyi saman kai, yana kwance saman doguwar kujera, Siraj na zaune kusa da shi Zinatu kuma na fuskantarsa fuskarta dauke da tausayinsa. Unkurawa ya yi ya tashi zaune sai ta yi hanzarin miko masa ruwan gora mai sanyi ya karba ya sha.
“Yaushe kuka shigo?”
“Tun dazu, gashi har an yi magariba kana sume, Zinatu ce ta gyara gurin kuma da taimakonta muka doraka saman kujerar nan”
Cewar Siraj, sai Jibril ya tada kai ya kalleta ya ce
“Thank you”
“Never Mention Allah ya sauwake ni zanje gida”
“Ba zaki bari na sauke ki ba?”
Ta kalli Siraj da ya yi maganar ta ce
“No zan je da kaina ya kamata ace ina gida by this time, ka kula da abokinka please”
Daga haka ta dauki jakarta ta rayata ta fice, sai Jibril ya unkura zai tashi kirjinsa ya yi masa wani mugun tsuka hakan yasa shi saurin komawa ya zauna yana yar kara.
Siraj ya dafa shi.
“Ka bari ka kara hutawa mana, Jibril kana matsawa kanka da yawa akan yarinyar nan, direban ka ya fada min ka bi bayanta sai kuma na zo nan na sameka cikin jini, ka rika sassautawa kanka dan girman Allah ina tausayin halin da kake ciki”
Jibril ya kalleshi irin kallon nan da shi kadai ya san fassarasa.
“Miyasa ka ce min ba ni da Nawwara? Bayan kuma ina da shi”
Siraj ya hade yawu da karfi.
“Wane irin kana da shi? Ban fahimce ka ba”
“Na ga dana da idanuwa Siraj dan da na haifa da Nawwara dan me zaka boye min?”
“Wace riba zan ci idan na boye maka? Mi zaisa na boye maka? Amman ka tabbatar dan ka ne?”
“Da na ne, jinina da nasa iri daya ne, kamata da tasa iri daya ce, da ace ba a kade shi ba da ba zan samu ganinsa da wuri ba”
“Amman abun nan ya bani mamaki, sai gaskiya akwai wani a abu a kasa, domin wanda nasa na bincika mana ba zai yi karya ba, shi ya fada mana Nawwara bata da da ko daya, sai idan mutumen dan uwanta ita kuma ta nemi ya boye mana din”
“Taya xaka yi bincike kuma ka nemi dan uwanta? Dan ina ne mutumen?”
“Dan unguwarsu ne, amman abun nan ya bani mamaki amman ka bincike Nawwara ta tabbatar maka da danta ne? Shin yana ma raye?”
“Yana raye wani ya kade shi da mota, and nayi duk wanda ya taba min yaro ko da Nawwara ce ba zan kyale ba”
Siraj ya karkato ya kalleshi
“Amman idan kaddara ce fa?”
“Ban san kaddara akan da na ba, da ce ni ta mai motar ya kade zan dauka ko amman da na? No never da yanzu na rasashi fa? Kasan halin da Nawwara zata shiga ko kasan halin da ni zan shiga? Who's ever that person is i will never forgive him”
Wani gumi ne ya soma saukowa Siraj, Jibril kuma ya mike tsaye yana jin zafin da kirjinsa ke yi ya nufi bedroom dinsa, saurin mikewa tsaye Siraj ya yi ya rufa masa bayan.
“Yanzu ya zaka karbi danka hannun Nawwara?”
“Shine abunda na ke tunani, zan yi duk yadda take so wajen ganin ta bani da na”
“Ni abunda na ke tunani mai zai hana ka fara fake love da Zinatu, so that ka samu kan Nawwara kuma ka gane idan har yanzu akwai soyayyarta cikin ranka”
Jibril ya kalleshi
“Wani lokacin kana yin abu kamar baka san waye ni ba Siraj, am straight forward, if yes yes if no that's means no for sure”
“Baka fahimta ba ne Jibril ai fake love na ce, kuma da sani Zinatu zaka yi”
“Ba zan yi ba, ka tafi kawai zan samawa kaina mafita”
Cikin sanyin jiki Siraj ya juya har zai fita sai kuma ya juyo ya kalli Jibril ya ce.
“Cocaine...”
“No please bar ni na ji da abunda ke damuna”
Ya fada yana daga masa hannu, sai Siraj ya juya kunya kunya da shi ya fice. Bathroom Jibril ya shiga ya sakarwa kansa ruwa sosai sannan ya yi wanka gaba daya tare da alwala ya fito, ya saka jallabiya ya rama sallah la'asar ya yi magariba, yana saman carpet din har aka kira isha'i, bayan ya yi ya taso ya dawo parlor ya shiga kitchen ya hadawa kansa ruwan tea. Sai kuma ya dawo falo ya zauna hoton Noor kawai idanuwansa ke nuna masa, sai ga wayarsa na ringing sai a lokacin ya kula da inda wayar take gefen kofa inda ya fadi dazu. Zuwa ya yi ya dauka sai yaga number Abbah. Gaiswa suka fara yi da Abbah kamin ya rufe shi da fada.
“An fada min baka da aiki sai shan cocaine, ka maida kanka wani kalar mutun, idan ba zaka iya ba zan karbe ragamar kamfanin nan na mika a hannun Siraj tun da ya fika kula”
“Waya fada maka ina shan cocaine Abbah”
“Kai ka fada min, kai kullum abun ka gaba yake ba baya ba”
“Ka yi hakuri Abbah zan canja”
“Da ya fi maka”
Daga haka Abbah ya kashe wayar. A ranar Jibril be gi bachi ba sai ya tashi ciki dare yana ta sallah nafila abunda be taba yi ba a tsawon rayuwarsa, kuka ya yi sosai ya kaima Allah bukatarsa, shiriyace a cikin abubuwan da ya fi roko sai kuma Nawwara, da asuba ma bayan ya yi sallah asuba ya dora da istigifari yana kankantar da kansa yana neman Allah ya yafe masa.
Washe gari ya kira wani abokinsa ya hada shi da mai tattoo ya zo har gida ya wanke masa tattoos dake wuyansa da kuma na sunan Nawwara da ke hannunsa.
Bayan mutanen ya fita ya shiga kitchen ya soma kansa kwai duk da yana da kuku be nemi ya yi masa ba sai ya hada tea da kansa, a dinning room din kitchen ya zauna yana ci sai ga Siraj ya shigo, bayan sun gaisa ya zauna shima ya zuba ma kansa yana ci, bayan sun gama ya budewa Jibril cocaine. Sai da Jibril ya yi kamar ba zai sha ba sai kuma shaeidan ya zugashi ya dauka ya shaka sosai, sannan ya mike tsaye yana fadin.
“Ba zanje office ba, ka yi duk abunda ya dace, Nawwara ma ba zata je ba, saboda dan mu ba lafiya”
Be jira abunda Siraj zai ce ya fito daga kitchen din na nufi bedroom dinsa. Saman gado ya kwanta ya rika bachi kamar wanda ya mutu, be farka ba sai da aka yi sallah azahar. A daren ranar ma sai da Jibril ya raya shi da nafila yana ta rokon Allah ya karkarto masa da hankalin Nawwara kuma ya shiga tsakaninta da duk wani mai son ta bayan shi, abu daya yake ce masa tuwo a kwarya a yanzu ba komai bane face rashin iya karatun kur'anen, haka zai dauko kur'anen ya rike but he can't read it ko baki be iya hadawa balle har ya tada ya karanta aya, and now he need to know his religion more than everything, yana son yasan abunda Allah ya ce da kuma wanda ya hana, zuciyarsa na raya masa idan har ya shiryu ya zama na kwarai Nawwara zata so shi, a duk lokacin da ya tuna da dansa yana asibiti sai ya ji kamar zai mutu saboda yana son naje ganinsa sai dai yasan Nawwara ba zata bari ba. Haka ya jera kwana uku be sake saka Noor a ido ba a duk lokacin da tunaninsa ya taso masa sai ya dauki cocaine din ya sha sannan ya samu sassauci.
Misalin karfe biyu dare yana zaune saman carpet yana istigifari sai ga Abbah ya kirashi, da fari ya ji tsoro dan yasan Abbah be saba kiranshi a irin wannan lokacin ba, sai kuma daga baya wani tunanin ya zo masa na cewar wata kila Abbah zai masa fada ne akan rashin zuwa aiki da ya yi kwana biyu.
“Hello”
“Jibril kana lafiya?”
“Lafiya kalau Abbah”
“Ka tabbata?”
“Lafiya ta kalau”
“Allah ya tsare ka, kawai na yi wani mafarki ne marar kyau ina fatar babu komai ko? ”
“Babu komai Abbah sai damuwa, Nawwara ta ki fahimta ta Abbah kuma akwai da a tsakaninmu”
“Ni ma na samu wannan labarin lokacin da na je zan bawa iyalanta da kuma ita kanta hakuri akan abunda ka yi musu, sai dai ba samu ganin yaron ba”
“Abbah da gaske? Yaushe ka zo?”
“An kwana biyu, kawai dan ban fada maka ba ne”
Abbah ya labarta masa komai daga zuwansa da kuma abubuwan da suka faru, Jibril ya ji dadi hakan ya tabbatar masa da mahaifinsa yana sonsa kuma yana tare da shi.
“Abbah ka taimaka ka min izinin zuwa gidansu Nawwara Dan Allah”
“Ka yi alkawarin ba zaka yi wani abu marar kyau ba?”
“Taya mai neman hanyar gyara zai yi wani abu marar kyau? Wallahi Abbah ina son Nawwara sosai kamar zan hauka ce”
“Amman da muka zaba maka ita ai cewa ka yi baka son ta”
Ya yi shiru be ce komai ba, sai Abbah ya kara da
“Kuma kasan sai dai ka yi hauka dan babu aure a tsakaninku ko? Kasan saki uku ka yi mata fa”
Idanuwansa sun cika da kwalla.
“Yanzu Abbah babu wani gyara da za a iya yi? Ba wata mafita?”
“Babu zan kwanta sai da safe”
Abbah ya kashe wayarsa, sai Jibril ya fara surutai
“Dole akwai mafita Wallahi, dole a samu mafita No no no”
Wannan tunanin ne ya hana shi bachi har garin Allah ya waye, tun da asuba ya shirya ya fita, kai tsaye asibitin ya nufa. Ya taki sa'a yau Nawwara ce kwana asibitin, ko da ya tura kofar dakin ya shiga zuciyarsa na bugawa dan ya yi tunanin zai samu Inna a ciki ne ko kuma ya tararda Nawwara a farke, sai ya tarar tana kwance bayan Noor saman gadon asibitin suna ta bachinsu a tare, karasawa ya yi kusa da su fuskarsa dauke da murmushi yana kallon iyalinsa. Wayarsa yasa ya dauke su hoto sannan ya cire jacket dinsa ya lulluba musu ya zauna saman kujerar da ke facing dinsu yana ta kallonsu cike da shauki.
“Na bata komai, da yanzu muna nan a iyali daya”
Kadan kadan yake maganar amman hakan be hana Noor farkawa daga guntun bachinsa ba, sosai da sosai yake kallon Jibril ganin wani babban mutum mai kama da shi, sai kuma ya unkura ya tashi zaune zai yi magana Jibril ya dora hannunsa saman bakinsa ya yi masa alama da ya yi shiru.
“Shiiiiiiiiiiii”
Sai ya mika masa hannu alamar ya zo, ba musu Noor ya mika masa nashi hannayen sai ya dauke shi ya zaunar saman jikinsa ya rumgume ya lumshe ido. Hawayen farinciki da bakinciki suka cika masa ido lokaci daya.
“Waye kai kai likita ne?”
Noor ya tambaya da muryarsa yar karama.
Sai Jibril ya girgiza masa kai alamar a a ba tare da ya bude idon ba. Shi kuma sai ya sake tambaya cike da mamaki yana ta kallon fuskarsa.
“Kai ne wanda Inna ta ce min zaka zo ka ganki? Kai ne Uncle din?”
Ya gyada masa kai still be bude idon ba dan baya son Noor ya ga hawayensa, Nawwara kam bachi kawai take abinta bama san ana yi ba.
NAWWARA POV.
karar bude kofar da aka yi ne ya tasheni daga dogon bachin da na ke, sai turaren da na fi tsana a duniya ya yi marhaban sannan na kula da jacket din da aka lulluba min saman jiki. Inna na gani zaune tana jan karbi ba Noor a kusa da ni kamar yadda muka kwanta, saurin zabura na yi.
“Ina Noor?”
“Yana gurin Babansa”
“Dauke sa ya yi? Miyasa kika bari ya shigo?”
“Ke ya kamata na tambaya dan nan na shigo na sameshi”
Na sauka saman gadon hankalina a tashe sai Inna ta rike hannuna.
“Ba gudu zai yi da shi ba, sun fita waje ne su sha iska, ina tunanin ya canja Nawwara a nan ya durkusa yana ta ba ni hakuri, wannan abincin karyawar da kika gani daga kamfani yasa aka kawo”
“Wallahi zai iya gudun min da da mugu ne”
Na fita daga dakin hankalina a tashe, ina fitowa harabar asibitin sai na hango Noor saman motarsa zaune shi kuma na jikina jikin motar ya rumgume Noor. Karasa na yi ina masa fada.
“Waya baka izinin fitar min da da?”
Sai ya dago ya kalleni sai ya sauko da Noor da ko riga babu a jikinsa.
“Ki yi hakuri na fita da shi ne ya sha iska”
Daukar Noor na yi na koma da shi ciki, shi ko sai zuba min tambaya yake akan wannan Uncle din nasa da Inna take fada masa zai zo ya duba shi.
A ranar duk wanda ya kawo mana ziyarar dubiya ya tararda Jibril a asibitin saboda nan ya wuni, duk wani tafiyar numfashin Noor yana kula shi hannun kuma maikaraya yana kula da shi sosai, na yi mamakin da Zinatu ta zo ganin Noor ko da yake ba abun mamaki ba ne duba da Jibril yana cikin asibitin, yau kan Bilal dake zuwa kullum duba Noor ya tarar da Jibril wanda hakan yasa shi kin sakewa sosai daman kwana biyu nan na rasa gane kansa, hakan be min dadi ba dan ban jidadin ganin da Bilal ya yi ma Jibril a asibitin ba, ni kuma na raka shi har gurin gate din asibitin sannan na dawo.
A lokacin Jibril ne kawai cikin dakin Jibril ne kawai sai Noor suna rike da hannun juna, daman Inna waje ta koma da zama bata iya zama a cikin dakin matukar Jibril na ciki.
Kamar jira yake na shigo sai ya mike tsaye ya nuna ni da yatsa fuskarasa a kumbure saboda bacin rai ya ce.
“Kar Bilal ya sake zuwa duba min yaro wannan ya zama na farko kuma na karshe...”
Kallonsa na ke sai ma na rasa abunda zan ce masa, daman na san za a rina saboda ya tsargu da yadda na nunawa Bilal kulawa kuma ina ta masa kalamai masu dadi a gaban idonsa, sai dai mai? Ai be isa ya hana Bilal zuwa ganin Noor ba ko dan na bashi dama ya wuni da shi ya bashi damar samun guri har ya fada min wannan maganar? Bana son na yi wata magana a gaban Noor saboda kar ya fahimci wani abu, wannan yasa na kumde maganar da ke bakina har sai ya fita na bishi na fada masa.
Turo kofar da aka yi aka shigo ne yasa dukanmu muka kalli kofar Mustapha ne ya shigo cikin manyan tufafi tare da manyan ledoji Jidda na gafensa.
[11/8, 9:37 PM] +234 703 352 5246: *RAI BIYU...♥🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
4⃣5⃣
MUSTAPHA POV.
Mustapha ya yi farincikin tararda Jibril da ya yi a dakin ko ba komai yasan Jibril ba zai jidadi ba, a farkon shigowarsa ya shigo da fargaba da kuma tunanin irin kallo da wulakancin da Nawwara zata masa, amman ganin Jibril ya sashi sakewa kamar daman can sun saba da Nawwara.
Murmushin fuskarsa ya fadada ya kunno kai cikin dakin tare da Jidda yana kallon Nawwara.
“Pretty ashe Babynmu babu lafiya, Wallahi ban sani ba sai jiya ya jikinsa”
Sai da Nawwara ta hadiye yawu sannan ta amsa masa fuskarta ba yabo ba fallasa.
“Da sauki”
Kana ta watsa ma Jidda harara. Kamar be san an hallici mutum a gurin ba haka ya bi ta kusa da Jibril ya karasa kusa da Noor ya dire ledodin da ke hannunsa.
“Cute Boy waya kade min kai”
Noor ya dade yana kallonsa kamin ya amsa masa bakinsa da nauyi.
“Nima ban san shi ba”
“Am sorry dear”
Ya fada yana zama kusa da shi tare da duba hannun sai kuma ya juyo ya kalli Nawwara.
“Pretty amman da sauki sosai ko?”
Nawwara kamar ba zata amsa shi sai dai ganin Jibril yasa ta karaso gurin tana fadin.
“Eh a hannu kawai ya kare”
“Wallahi ban sani ba sai dazun nan Jidda ke fada min”
Nawwara ta kalli Jidda sai Jidda ta dan zaro idon tana daga kafadarta.
“Ya matsa ne sai ya ganki kin san yadda yake damuwa”
“Sorry na zo ban fada miki ba”
“Ba komai”
Cewar Nawwara. Jibril ya rumtse ido ya sauke ajiyar zuciyar da ta mamaye masa kirji, sai ya juyo cikin facin rai ya ce.