Showing 30001 words to 33000 words out of 116366 words
hannu.
Abun da ya kara bashi Tsoro shine Tabbss Hasiya ya ke gani, ammh kanta na kasa ta kasa kallonsa Tunda ta Fahimci shine.
Na biyu kuma bakinsa na rawa yace
"Siya."
Ammh kamar ba su ganshi ba, ta gabansa Surayya ta wuce rike da Hannun Siya zuwa shashen Umma ko waiwaye.
Bakinsa a bude har suka shige kafin ya Rufe zufa yaji na keto masa ta ko'ina, sai kawai ya samu kansa da maimaita Hasbullahi wani'imal wakeel.
Ya kara Rikicewa ne sanda Motar Abba shima ta shigo gidan duk sai ya Daburce.
Ya Dauka shima Abba zai yi kamar bai gansa ba ne, ammh ga mamakinsa yana ganinsa shi ya fara washe masa baki ya na fadin"Magajin gida ashe ka iso."
Sadiq sai yaji kamar sai yanzu ne yake jin kara jin Guilty din abunda ya aikata.
Rumgumesa Abba ya yi yana masa maraba da zuwa, sannan yaja Hannunsa zuwa bangarensa suna tafe ya na fadin"Ya wajen aikin naku? Fata dai ba wata matsala ko?
Sai da Sadiq ya Hadiye miyau mai kauri kafin ya iya cewa"Alhamdulillah Abba."
Daganan ya ja bakinsa ya Tsuke, sai dai ya na ta bin Abba da kallo domin ya Fahimci yanayinsa.
Ammh ko a fuska bai ga wani alamun Sauyi tare da shi ba.
Ajiyar zuciya ya saki a Boye a kallah dai ya samu yar salama Abba bai Dauki zafi dashi kamar Umma da Sauran yan'uwansa ba.
*Janafty*
*TMWBK3007*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
Haba Babyn Habiby ya zaki zauna kina ta fama cutar infection, ke ce rashin sha’awa, ke ce jin zafi yayin tarayya, ke xche d’aukewar ni’ima, ke ce kai’kayi ki fitar farin ruwa da sauransu, an yi maganin asibiti da na gargajiya amma duka dai, tau share hawayenki ‘karshen matsalarki ta zo, da Honeydrops infection flusher ko cleanser pro sai kin yi dariya da godiya don zai wanke miki duk wata cutar sanyi. Akwai original sabaya ta gyaran breast su cicciko kamar baki shayar ba, akwai ta hips da mazaunai ki yi ma sha Allah ki samu kaya kema su miki d’as ki bar yawo da doguwar riga.
Na ce ba a nan muka tsaya ba muna da hadaddun kaya irinsu sweeteners, tighteners and wetners na tashin kan oga, wanda zai miki tukwicin dole, ke ko kurma ne sai ya yi magana ranar, don sumbatu ki dai samu abun rufe mai baki gudun ma’kota. Muna nan a garin Sokoto muna aike kowani gari kowacce kasa cikin aminci da rahusa. Kuna iya danna link din nan domin yi mana magana Kai tsaye https://Wa.me/2348167888934 ko kuma a kira 08167888934. Sai mun ji daga gareku isassun mata.
Shi dai Sadiq yana zaune ne kawai a falon Abba, ammh kwata kwata baya cikin cikakkiyar natsuwarsa.
Kunya tare da Nadama, da wani irin abu sun taru sun lullubesa da yasa ya kasa sakewa tare da Abba da ko a fuska bai nuna masa wani abu ba.
Sai ma jansa da Hira kawai ya ke yi, bayan sun gama Hiran aikin sai ya koma masa Hiran abunda za'a fitar Saboda azumi ya gabato.
Tun yana jin kunya har yazo ya sake ya na ba ma Abba amsa tare da shawarwarin da ya nema Daga bangarensa.
Ganin da ya yi Abba ya shanye duka abunda ya aikata sai Kunya ta lullubesa da yasa ya kasa zama a kan kujera sai gashi durkushe gaban Abba a kasa cikin wani Raunin murya yace"Abba don Allah ka yafemin, nasan na yi muku laifi."
Sai kuma ya kasa mgana ya koma ya sunkuyar da kansa kasa yana jin sai yanzu ne ma yaji meyasa ya aikata haka batare da ko sanin Abba ba?
Abba kuma shuru ya yi masa na wani Lokaci kamar bazai yi mgana ba.
Dalilin da yasa ya dago sai suka had'a ido da Abba da ya yi masa kuri da ido ya na kallonsa.
Sadiq ya kara marairaicewa ya na fad'in"Don Allah Abba ka yafemin, ni har ga Allah da kyakyawan Niyar taimako na yi wannan auran. Kuma.."
"Abubakar.."
Abba ya katsesa bayan ya kira sunanshi, da Sauri ya amsa har bakinsa na rawa, Abba cikin muryansa yace"Ni baka yi min komai ba magajin gida, tun ranar da na san kayi wannan auran albarkata ke tare da auran naka, ni laifi d'aya ka yi min da ya fi min ciwo fiye da auran da ka yi."
Abba ya karishe fad'a ya na kallon Sadiq da ke duke gaban Abba kamar zai yi masa sujjuda.
Cikin mamaki ya dago ya na kallonsa kafin yace"Abba wani irin laifi ne wannan, wanda yafi boye muku auran da na yi girman Laifi?
Mirmishi Abba ya yi kafin yace"Girman laifin shine har yau baka Fahimci irin girma da matsayin da ka ke dsshi acikin zuciyata ba Abubakar, girman yadda zaka iya yin abu mai girma haka batare da sanina ba, girman yadda ka ke tunanin ni bazan yi maka abunda ka ke so ba Matukar bai sab'a ma Shaari'a ba."
Sadiq yaji kamar ya fashe da kuka ya na kallon Abba yace"Wlh Abba.."
Abba sai ya dagamai Hannu kafin ya Cigaba da fad'in"Bacin raina d'aya da baka wareni cikin wad'anda za su zama Sirri kan sanin wannan al'amarin ba, Abubakar ko ba a zariya ba ko a birnin sin ne ka ga wata mace kana so batare da sanin kowa ba zan taka naje na nema maka auran ka, kuma nima zan iya sirrinta maka mganar har sai lokacin da ka so kowa ya sani, ai ni mahaifinka ne na fi kowa sanin kyakyawan hallayarka kuma ina da Tabbacin duk abunda zaka yi ko zaka aikatashi mai kyau ne"
Sadiq cikin murya kamar zai fashe da kuka yace"Abba na yi Tunanin baza ku amince ba ne, tunda akwai mganar Sultana."
Abba ya murmusa kafin yace"Ba wanda ya isa yaja da abunda Allah yace ayi, kai ai namiji ne kuma mijin mace Hud'u reras. Ba kuma wanda zai iya hanaka cike sunnar Ma'aiki Magajin gida, ni abu daya na ke so na muna maka shine ka yi kuskure ko a gaba ya kamata ka Fahimci ni nan zan iya tsaya maka a komai na Duniyan nan kuma na baka dukkan Goyan bayana sai dai in dan abun yafi karfina."
Sadiq na sauke Numfashin Salama yace"In sha Allahu Abba, nagode sosai Allah ya kara girma."
Abba ya amsa da Ameen Ameen ya na sake nuna masa kuskuran da ya aikata na Boye musu, tunda shi Lamariin aure ai ya wuce wasa.
Sadiq ya kalli Abba kafin yace"Abba Umma ta Dauki zafi da lamarin, tace sultana ta kwaso kayanta ta dawo gida. Nima kuma da na zo yau ina gaisheta taki amsani daga karshe ma ta Boye ma ganina."
Abba ya gyara zama kafin yace"Kada ka damu da wannan, bazan baka Shawaran ka rabu da daya saboda d'aya ba, duka matanka ne kuma zaka Cigaba da zama da su, na riga na yi mgana da Surayya nace ina bukatar son ganin ita iyalin naka ta Zariya Domin samun masalaha da Daidaito."
Da Sauri Sadiq yace"Ai tazo Abba, na ganta tare da Anty Surayya dazu kafin ka dawo."
Abba sai ya jinjina kai kafin yace"Shikenan ma hakan ya yi, komai zai warware in sha Allahu kada ka damu."
Ya fad'a ya na Dafa kafad'an Sadiq din alamin lallashi, Sadiq sai ya yi Tunanin gwara ya fad'a ma Abba komai daya danganci auransa da Siya Tun yanzu kafin kuma daga baya yaji wata mgana yar Sauran yardan da ke Tsakaninsu ta kara lalacewa.
Nan ya zauna ya fara ba ma Abba Labarin Tun ranar farko da ya fara had'uwa da Hasiya har zuwa yau tare da Labarin duka auranta da kuma Kaddaran da ke cikin Rayuwarta.
Abba ya ji matukar Tausayinta sosai shi kanshi a baya saboda Innani da irin manganunta ya na da dabi'ar rashin Tauhidi ammh godiya ga Allah da ya bashi yaro mai kaifin Basira irin Sadiq shine ya yi sanadiyar da yasa yasan Allah shine mai yin komai a lokacin da ya so, a kuma sadda ya so.
Cikin Tausayin da ya bayyana har a saman Fuskarsa yace"Allahu Akbar kayi babban Jihadi Magajin gida, Allah Ubangiji yasa wannan abunda da ka aikata ya yi sanadiyar shigar ka Aljannah"
Cikin Farinciki Sadiq ke amsawa da Ameen Ameen, Abba ya cigaba da fadin"Uwa ka share ma kukanta, kai ma watarana Allah ya baka ya'yan da zasu same maka sanyin idanuwana su kuma zamo masu jin kukan ka, sannan su kasance mssu share maka hawayen ka."
Sadiq na ta amsawa da Ameen Sai Abba ya yi shuru ya na wani Tunani kafin yace"Mu bar wannan mganar a nan, kasan mata ba lalle su iya Fahimtar irin wad'anan abubuwan da Wuri ba. Kuma kaga innani yanzu ta na ji sai kuma ta Rikita al'amarin"
Kamar Abba ya sani daman shi Sadiq ya fad'a ne saboda Tunaninsa ko har da wannan Labarin suka sani? Mganar Abba sai ta warware masa cewa ba su kai ga sanin haka ba.
Abunda bai sani ba Shine komai da ya Danganci Hasiya bazai zama Sirri ba a yau.
Suna nan falon Abba suna Hira Surayya ta kira Abba kan mganar gashi ta zo da Hasiya, sai Abba yace Sadiq ya fad'a masa ga su ma tarre. Yanzu an kusa kiran sallar azahar bayan sun je masallaci sun dawo su had'u a shashen Innani ta gaya ma su Umma.
Daganan suka yanke Kiran, duk da Sadiq na jin tsoro sai dai yaji gwarin gwiwar samun Abba a kusa da shi, Daya tambayi Abba ko wani ne yazo musu da Labarin auran nasa?
Abba yace Surayya ce da Saddiqa suka zo masa da mganar daganan ya yi shuru yasan Halin Big sis da bin Diddigi ya na da tabbacin har Zariya kila sai da taje.
Daganan masallaci suka tafi suka yi sallar azahar, sun jima a masallacin Abba na ta gaisawa da Mutane makota abokan arzuka, Shi ya bata musu Lokaci suna hanya ma Surayya ta kira Abba sannan ta kira Sadiq.
Sadiq ne ya amsa kiran nata sai tace masa suna shashen innani su kawai su ke jira, shiyasa suna shigowa gidan bangaren na Innani suka nufa kai Tsaye Abba na gaba Sadiq na bin bayansa kamar ya na kirga takun Abban.
Da sallama Abba ya shiga Falon, Sadiq ya yi sallamansa iya a saman bakinsa ammh, Falon nan na Innani a cike ya ke da yan'uwansa mata shi ba su ne a gabansa ba Siya Idanuwansa ke son gani acikin falon.
Bai lura da yadda gabadayansu suka Zuba masa ido ba, domin ya wani had'e rai ya yi, yaso ma yazo da bakin glass din ya Rufe kwayar idanuwansa Sannan wacce ta masa shisshigi ko ta wuce gona da iri ya taka mata Burki, Ahto ai in sun girmesa ai ba su haifesa ba.
Allah ya nuna masa Siya chan gefen Surayya ta Rakube baiwar Allah kanta na kasa, Tausayi ta bashi yasan a takure ta ke ko da ganin yadda ta ke ta mutsu mutsun zaman bai yi mata dadi ba, ko baka da juna Biyu kayi zaman tankwashe kafa na wani Lokaci ya ka ke ji, ballatana ga Ciki kuma ya Tsufa.
Sanda ya biyo bayan Abba zuwa Cikin Falon, kamar zai wuce ta bangaran Siya da Surayya sai kuma yaga Umma gefenta Kuma Mama ce ta inda zai wuce irin kallon da Umma ta yi mssa ne yasa da Sauri yaje ya zauna a gefen kafafun Abba.
Innani na zaune itama akan kujera kusa da Abba, ga sandarta a gefenta da gilashinta sai faman cin magani ta ke yi, Daga gefensa ne yaji ana ta jan majinan kuka da shessheka ya juya sai yaga sultana wajen kafafun Innani ta dunkule kanta ta na kuka.
Mamaki ya kamasa miye abun kuka Fisabillahi in ba gata ne ya yi ma Mutum yawa ba?
Karamin Tsaki yaja a ransa ya Kauda kansa, Innani kuma sai kallonsa ta ke yi ta cikin gilashinta ta na Hararansa, sai kuma ta waiga barayin da Hasiya ke zaune itama ta harareta.
Gani tayi magajin gida ya kalleta ya watsar kamar yaga kashi yasa ta ture Sultana da rabin jikinta ke kusa da kafafunta ta na fadin"Ke ni ja chan sakara mara wayau? Miye kike wani kuka ni da nace miki ki kwantar da Hankalin ki, in dai ina Raye Magajin gida bai isa ya Tozarta ki ba, ke ba ma shi ba Kaf a falon nan ba wanda ya isa, ko da sulaimanun ne da kansa kuwa, Saboda haka ki bar kuka zan karb'an miki yancin ki, ba mai had'a ki zama da yar Bariki Tsohuwar kilaki."
Ta karishe fad'a cikin Kufuluwa Da Sauri Sadiq ya kalleta bai san bakinsa ya Kubce ba sai da yaji yace"Innani wacece Tsohuwar Kilakin?
Innani ko ba tsoro da karfi ta nuna Hasiya da Sandar Hannunta Lokaci daya ta na fadin"Ga ta chan a wannan a bar mai kama da mayun da ka kawo min cikin Zuru'ata mai Tsafta."
Sadiq ya kara girman Idanuwansa ya na kallon Innani ransa na baci da karfi yace"Innani.."
Bai sauke ma numfashi ba yaji Umma ta kira sunansa a fusace"Abubakar."
Dole ya yi shuru ya koma ya na kallon Umma Lokaci d'aya ya na fadin"Na'am Umma."
Cikin gargadi tace"Ka yi ma mutane shuru anan wajen Tunda baka da kunya."
Innani na jin haka sai tayi kayci tace"Da kin barsa ya zageni, da yau kunga illar auran bariki ganin idon ku salamatu."
Abba ne ya yi gyaran murya kafin yace Surayya ta Bude taro da addu'a a gefe daya kuma ya na mamakin ganin duka ya'yansa shi dai bai ce su zo ba, Sadiq kawai ya Bukaci gani da matarsa.
Girgiza kai kawai ya yi, acikin ransa yace mata mata, duk abunda aka had'a da mata sai an yi Hakuri.
Surayya ta yi sallama sannan ta Bude taro da addu'a.
Kafin ta ce"Abba ga Hasiya matar da Sadiq ya aura kafin ya auri Sultana gata nan kusa dani."
Ta fad'a ta na dafani, ni ko jikina ba inda baya rawa, daga fuskata kuma hawaye ne ke diga a saman Hijabin jikina na kasa dagowa duk da naji Idanuwam Assadiq a kaina ba maganganun Innani ne suka sakani kuka ba, Sai tun zuwana cikin gidan nan na Fahimci kaf cikin yan'uwan Assadiq ba wacce ke maraba dani sai Surayya.
Tunda muka je falon Umma ita kad'ai ke kulani, na sha manganun cin zarafi a wajensu In Surayya ta taremun su taso mata, Umma kuma da ta fito Surayya tace na gaisheta bata amsa ba, Daga karshe ma tace duk su koma daki sai aka barni a falo kamar wata almajira.
Daganan wasu suka shigo su Sakeena kenan yan dakin Mama suna kallona suna Tabe baki, na gaishe su suka amsa a wulakance kamar ba sa so, tun a lokacin jikina ya saki na ke kuma da Tabbacin ba lalle su bar dan'uwansu ya cigaba da aurena ba
Ko yanzu da Innani ke ta aibatani bai Dameni ba, ni damuwata d'aya shine Assadiq ina cikin Tsaka mai wuya matukar suka ce zasu rabani da shi.
Ina cikin wannan Tunanin naji Muryan Abba na fadin"Ma sha Allah, ta taso ta zo kusa da ni ta zauna itama."
Sai gabadaya kowa a falon ya bi Abba da kallon Mamaki musamman ma Umma da Innani.
Surayya kuma sai da ta Murmusa Sadiq kuma kamar ya goya Abba, Daman yasan Siya ta gaji da wannan zaman.
Surayya ta taimakamin na mike Tsaye kafafuna sun haye sumtum, jikina na dan rawa ta kalleni kafin tace"Asiya ke ji Abba na kiran ki."
Ba musu na gyad'a mata kai sanman na fara tafiya a hankali zuwa gaban Abba ammh na saka Hannu ina kare Cikin jikina duk da ban isa na Rufeshi ba Allah ya Riga ya bayyanar da shi.
Ba gefen Sadiq na nufa ba sai nufa ta bangaran Damansa zan zauna sai naji Bayana ya kage, ina cije baki wajen na gyara kafata sai naji na Turgud'e kamar zan fadi.
Kamar kiftawan Ido sai gani a Hannun Assadiq ya Rikoni cikin Sauri bakinsa na rawa yace"Siya ki kula fa.'
Ya ke fad'a ya na kallona, Kaina na kasa ganin gabadaya falon ana kallonmu cikin Saurin na zame zan zauna da Sauri Assadiq ya kalli Abba ya na fad'in"Abba ka yi mata izini ta zauna saman kujera saboda lalurar da ke tare da ita."
Da Sauri Abba yace"Ta zauna mana, ai ta na da uzuri, zauna zauna Bismillah"
Abba ya ke fad'a da Sauri ko Sadiq ya zaunar da ni gefen Abba kunya ta kamani cikin sanyin muryata nace"Assadiq.."
Shii..!
Yace ya na kallona sannan ya Girgizamin kai, Dole na yi shuru sai da na zauna sannan ya duka ya mikar min da kafafuwana Lokaci daya ya na fadin"Ki bar su a mike su d'an sake kinga sun kara kumburi."
Ni dai kunya da wani irin nauyi sun hanani Dagowa, shi kuma ko ajikinsa sai ma tashi da ya yi ya koma bangaren Hagun Abba in da ya tashi ya zauna duk da yasan shi ake ta kallo ammh bai yarda ma ya Daga kai ba, ballatana ya kalli wani acikin su.
Sultana ce suka had'a ido ta yi masa wani rin kallon, shi kuma sai ya kafeta da ido domin sai yaga kamar kallon yafi kama da na reni ya na so ya fahimci abunda ta ke nufi ne, sai kuma ya ga ta kauda kanta ta na sharan kwallah.
Abba na zaune ya na d'an mirmishi Innani kuma sai ta hau kad'a kafa ta na Faman Tabe taben baki.
Abba ya juya ya na kallona da naji duk na kasa sakewa cikin muryansa yace"y'ata ya sunan ki?
Muryata na rawa nace"Ha. Hasiya."
Sai Abba ya jinjina kai kafin yace"Sannu Hasiya, ina iyayen ki suke ne?
Kai Tsaye nace"Babanmu ya rasu , sai mahaifiyata Amma ta na garinsu yanzu, sai yayyena guda Biyu da kanwata guda d'aya."
Abba sai jinjina kai ya ke yi alamun gamsuwa kafin yace"Har na tsawon wani Lokacin kika san Abubakar?
Assadiq na dago ina kallo sai naga ya Jinjinamin kai, shi ya bani karfin gwiwan yi masa bayanin Farkon had'uwata da Assadiq har zuwa auren mu."
Abba yaji tabbas yadda Magajin gida ya bashi Labari ne, cikin gansuwa yace"Dakyau, shima haka ya fad'amin"
Sai kuma ya yi shuru kowa ya zauna kawai ya na kallonsa mirmishi ya saki kafin yace"Na saka ma auran ku albarka, Allah ya sauke ki lafiya ina miki sannu da zuwa cikin Ahalina."
Kowa sai da ya Bude baki ya na kallon Abba.
Ni kuma shi na ke kallo idanuwana cike da kwallah nace"Ni?
Sai ya gyad'a min kai kafin yace"Daga yau kema kin zama d'aya daga cikin Ahalina, gobe in