Showing 93001 words to 96000 words out of 116366 words

Chapter 32 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

330

sai an siya mata.
Kai jama'a ni ban taba ganin kishi irin na Sultana ba.
Ka yi da kishiya kuma ka yi da miji Saboda sakarci.

Ni sai na rika Allah Allah ma na tafi katsina Biki duk sai gidan ya isheni, yarinyar nan tsirfarta ta yi yawa.
Sajida kuma ko suna bata zo ba taji Haushin mganar da Abba ya yi mata.
Sadiya dai tazo ta na ta harare harare da jefa manganganu.
Yara kuma sai dare na ke ganinsu suna wajen Umma ko mama, in Abba ya dawo gida suna tare da shi.
In kuma suka ga Babansu su manne masa tunda yanzu su san kowa.
An yi suna Talata, Jumma'a muka tafi katsina tare da Assadiq tun da bai koma ba.
A gidan Amarya Hauwa'u na sauka Tahir ma na garin shi yaje ya tarbemu, ni kaina naga tarba Hauwa'u kamar ta taba ganina.
Ko'ina sai ta nuna ni tace matar Abokin Tahir ne Sadiq.
Su Mama sun ce sai dai mu had'u a Daura har da su Anty Surayya duk za su je ma Hajja Biki Sanadin Tahir.
Abba ma yace zai zo daurin aure sannan 100k ya tura ma Tahir Gudummuwa.
Ranar asabar aka Daura Tahir da Amaryansa Hauwa kuma a ranar suka kwashemu zuwa Daura.
Ankon less ne ya yi das a jikina kamar an auna ni, gwamin ban sha'awa tunda ban wasa da kunin sabaya.
Saboda ni dai ina so na ganni da jiki ba na son ramar nan nawa.
Sai kananun halittun jikina su rika bayyana.
Mutane ma kallon mai ciki suke yi min, Har Anty Surayya sai da tace ko Ciki gareni nace tukunnah dai
Kuma ban saka tsarin iyali ba Tazara ne Allah ya bani, ina fatan sai su Asim sun shekara uku ko da zan samu wani cikin.
Tare muke da Matar Abokinsu Mb, Jb dai bai yi aure ba, bai gama iskancin na shi ba.
Motar Mijina na shiga zuwa Daura tunda suma su Mb kowannen da Motarsa sauran motocin kuma suka kwashi Amarya da Ahalinta.
Acan daura muka hade da Mama da Anty Surayya sai shahida da A gusau taje barkan Sultana daganan ta Biyo su Mama daga kuna nan zata koma katsina.
Hajja da yan'uwan Tahir sun yi ta godiya wannan karan sosai Umma ta ba da kudi da kayan abinci an kawo ma Hajja.
Kwana daya muka yi a Daura muka wuce Abuja ni da Assadiq da yara, wasu kayanmu ma na gusau yace na bari karshen wata in ya koma sai ya Taho mana da shi.
Sallama sai dai ta waya su Anty Surayya daman mun riga su tafiya, yace in ya tafi ya barni wahala ne kuma sai an saka wani ya maidani gida.
A daura muka bar Amarya Hauwa'u da Angon Tahir, sai fatan Allah ya ba au zaman lafiya.
Mun koma Abuja bamu san abunda ya faru a gusau ba.
Ashe a satin  da aka yi Bikin Tahir Mijin Sajida ya dankara mata saki har Biyu.
Rigima ta yi da Danginsa kaca kaca shi kuma ya saketa.
Sakin aure bai da dadi, kuma ba wanda ya kirani ya fad'amin Anty Surayya ce kuma kwana Biyu bamu yi mgana ba.
Siyama kuma bamu yi waya da ita ba.
Kuma Assadiq baya gayamin irin wad'anan abubuwan.
Nima sai da naji suna mgana da Anty Surayya.
Yana cewa"Allah ya kara mata, ba tun yau ba nasan abunda Sajida ta shuka watarana shi zata girba."
Sai da suka gama wayar ne na tambayesa abunsa ya faru.
Shine ya kalleni kai Tsaye yace"Sajida ce mijinta ya saketa saki biyu, Abba ya kirshi sun zauna mganganu ba dad'i ashe acan dangin nasa ma munafunci da Rigime rigime ta ke ta had'awa dara taci gida mahaifiyarsa tace ya saketa."
Cikin jimami nace"Innalillahi Abu bai yi dadi ba"
Mikewa ya yi lokaci d'aya yana fad'in"Ya yi dad'i mana, ai kad'an ta gani wanda yace daman tukunyar wani bazata tafasa ba ai tashi ko Dumi bazata yi ba."
Ni dai ban ce komai ba, har ga Allah jikina ya yi sanyi.
Saki ai ba shi da dad'i, ina ga shiyasa ba wanda ya kirani ya gayamin Labarin ba dadi.
Anty Surayya kuma ke kiranshi inaga kan mganar har cewa ta yi yaje Gusau yace ba inda za shi shi yana da abun yi.
Umma ina ji ta na kiranshi, kan mganar sai ya zille mata da mganar aiki daga karshe dai ba'a samu masalaha ba, mijin Sajida ya zuciya ya kuma ce har Abada duk da ya'yan da ke tsakaninsu.
Dole kanwar naki ta dawo gida ta fara Idda, ga ta  ga Sultanan sai su cigaba da munafuncin na su.
Su dasa daga inda suka Tsaya in ji Surayya.
Take gayamin da muka yi waya da ita, a bakinta naji ba'a daidaita ba, Sajida na gida.





*Janafty*
*TMWB3K018*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/I7uxPXgtPKBHnVQjaEbRlE

*LAME NIG!*

*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*

Daga Sajida har su Umma ba su tab'a Tunanin Sajida zata iya tsintar kanta a cikin zawarcin da ta samu kanta a ciki Dumu dumu ba.
Sajida ta gama sakankancewa da ta kama gida ta kuma fi karfin wani ya tugeta, ta na ganin Yusuf mai Hakuri ne sannan mai kawaici wanda baya maida kai kan wasu abubuwa kuma ta na ganin cewa ta Haihu ga ya'ya uku a tsakaninsu tana ganin babu wanda ya isa ya iya ja da ita.
Ta saki jiki ta na ta rashin mutumcin da ta saba daman tun tana gidan Sajida akwai munafunci sannan in dai ta zauna a wuri ba ta yad'a alheri, kuma bata sulhu sai dai ta kara Hura wuta.
Bayan ta yi aure ma bata daina ba, a makota ne a dangin mijinta ne duk inda ta shiga ta zauna bata yad'a alheri ba sai dai ta fad'i sharri ta Hura wutar wata fitanar.
Bata kuma shiri da wasu kannen mijin nata tun tuni shima mijin nata ya sha ja mata a kunni karya ne su had'u a taro Sajida ba ta watse taron nan da fad'a ba, ita kanta mahaifiyarsa bata son Sajida sabida tace ba mutuniyar kwarai ba ce.
Bata son zaman lafiya, Ta dad'e ta na yin abubuwa Yusuf din da kauda kai sai wannan na karshenta da wa'adin auran na su ya kare.

A gidan sunan matar kanin Yusuf din, Ta yi fad'a da kannensa har suna zaginta ita kuma tace sun san wacce suka zaga wannan Tsohuwar mai Dattin dankwali na gida.
Ai ko ba sanya suna zuwa gida suka gayama Mahaifiyarsu ga abunda ya faru har suna kari, nan ta ke ta kira Yusuf tace ya sauwake Sajida kila in ta d'andani zawarci zata yi hankali.
Shine dalilin da yasa ya saketa sannan Saboda a kara kuntata mata uwar tace duk ya kwaso mata yaran ya kawo mata hadda wanda ta yaye.
Zaman da Abba ya yi da shi sai ya Fahimci Sajida ta canchanci ta zauna a gida ta ga rayuwa kila ko zata yi Hankali shiyasa shima bai kara neman Yusuf ba.
Ballatana Assadiq da yace Allah ya kara gwara da ya saketa kila nan gaba zata Fahimci rayuwa ko Allah zai saka ta zauna lafiya da kowa.
Ita ko Sajida da farko ta dauka wasa ne, Ta na ganin Yusuf bazai iya Rabuwa da ita ba wasa ya ke yi, zai zo da kafarsa ya neme ta ya kuma bata Hakuri ya maidata gidansa.
Shiyasa ko da ta dawo gida da Abba ma ya kirashi Haushi ta rika ji a tunaninta za'a zubar mata da Ajinta, sai da taga har ta shafe wata d'aya a gida har jini daya ta yi ba Yusuf ba sakonsa sannan ba wayarsa.
Daman tun faruwan abun bata kirasa ba ta zauna ne sai ya nemeta da kansa sai ta fara ganin karshenta.
Umma ta damu da wannan Lamarin sannan nadama ya shigeta, In ta zaunar da Sajida ta na mata fad'a sai ta rika Tura baki tana fadin Yusuf zai zo da kafarsa har dakin Umma ya Duka ya bata hakuri.
Sai da ta ga lokaci ya fara tafiya bai zo ba, sannan bai kirata ko a waya ba.
Sannan ga shi ta fara gajiya da zaman gida kewar ya'yanta take ji sosai da gidanta inda ta ke yi duk abunda taga dama ba nan da ba ta da ikon yin wani abu ba.

Sannan abun da ya bata mamaki yan'uwanta kowa sai yace laifinta ne, ita taja ma kanta saki kowa sai ganin laifinta ya ke yi, har Abba haka ya kirata ya yi mata kaca kaca ita kuma a ganinta bata aikata komai ba sai ma gani take yi da mutane ba sa son gsskiya ne.
Yanzu haka a daki d'aya suke kwana da Sultana tunda a bangaren Umma ba wani daki sai nata, ga shi cikin Dare Mai sunam Umma da suke kira da Ummi akwai kukan dare, Sultana juyawa ta ke yi ta sha barcinta ta barta da renon yarta.
In ta tasheta sai ta tashi ta na alamun barci barci in an samu ta bata Nono sai ta sakar mata yar ta koma ta kwanta tana fad'in kanta ciwo ya ke yi, sannan Umma da farko ta na shigowa ta taimaka mata itama in bata bangaren Abba to daga baya ma sai ta rika barin Sajidar da wahala ta bakinta tace tunda ta na kusa ta taya sultana jegon, kuma ma dai ai ta girmemeta a harkan ta rika nuna mata wasu abubuwan
Sajida ta na shuru da farko sai da taga Sultana ta maidata kamar Nany mai renon yarta, komai na ta ba tsari ba gyara ga son jiki da kazanta komai a watse sai dai in Sajidar ne zata gyara, in kuma ta yi mata mgana sai tace"Ni fa Anty Sajida na gaji ne, da me zan ji da kula da yarinyar ko da gyaran daki da kaya? Ai Umma tace tunda kin dawo gida kina zawarci ki rika tayani kina taimakamin mana."
Ranar Sajida ta sha mamaki kuma ba ta tab'a sanin haka kalmar zawarci ke da zafi ba sai da kanwar bayanta Kamar Sultana ta gasa mata mgana.
Abun ya yi mata ciwo kwarai ta samu Umma ta gayamata.
Umma ta yi wata dariya kai Tsaye ta kalli Sajida ta na fad'in"Ai ba karya ta yi ba, gaskiya ta fad'a tunda kin fito zawarci baki da wani amfani sai na Tayata kula da yarta, daman kuma bata da wata abokiyar shawaran da ta wuce ki ke da Sadiya, to tunda ita Sadiya na gidanta ke ce zaki zauna da ita kinga ma shikenan sai ku yi ta bama juna shawarwari ko?
Sajida bata gane mgana Umma ta gasa mata ba, sai da tace"To Umma ya dace ta wani ce na dawo gida ina zawarci?
Ni ai ba sa'anta ba ne, duk kokarin da na ke yi mata bata gani? Ni fa ban tab'a ganin sangantattaciyar kazamiyar mai jego irin ta ba wlh."
Umma dai yar dariya ta yi a ranta kafin tace tun yanzu?
Ai ta dauka da saura kafin zama yasa kowa yasan halin kowa.
Kuma sannan Sultana sai ta fara yi ma Sajida wani abu sai ana zaune sai ta kalleta cikin kamar mamaki ta na fad'in"Yanzu wai da gaske shikenan Anty Sajida kin zama bazawara?
Tambayar irin cikin izgili da Dariya da Renin hankali.
Sannan kuma ko a gaban waye ta kan fad'i haka ko a jikinta ita a dole da sunan wasa.
Tun Sajida na nuna bata jin haushi har ta fara nuna mata, sai tace ita a wasa ta ke mganarta.
Sannan wani karin abun haushin ma Har makaranta in Sultana zata shiga sai Umma tace su je tare da Sajida ta rike mata Ummi in sun shiga karatu.
Abun kuma da ya faru ba'a shiga da yara a ji, ita kuma Sultana tace a daukan mata mai reno.
Ko kuma Anty Sajida ta rika rakata makaranta ta na rike mata Ummi, ita kuma Umma ta amince tace tunda Sajidan na gidan bata komai idda ta ke yi, kuma tunda fitan ta zama ta lalura ta rika raka Sultana cikin makaranta.
Sajida bata kara jin ta raina kanta ba sai ranar da ta raka Sultana makaranta Lokacin har ta yi arba'in sai dai bata koma gidanta ba sai Assadiq ya dawo.
Yafi wata bai zo ba tun tafiyarsu ta bayan suna yana ta kawo uzurin aiki ne ya rikesa.
Tun safe suka zo, ita ta na waje rike da Ummi ta na fama da ita, ga sanyi Lokacin an fara iskar sanyi Sultana kuma ba su fito ba sai Wajen sha daya na safe sai gata ita da zugan kawayenta.
Suna zuwa suka ga Sajida rike da Ummi, cikin kawayen nata wata ta kalli Sajida ta na fad'in"Nanny ko da kika samu mai hankali daga gani zata kula da Ummi sosai."
Sultana ta kalli Sajida ta wani kyalkyace da Dariya kafin tace"Wata Nanny? Ba fa nanny ba ce Yayar mijina nace Anty Sajida da ya ke baki samu suwa suna ba ne shiyasa baki ganta ba, ammh ai su Maryam su santa."
Sajida ta na ji a gabanta Yarinyar tace"Au yi hakuri, na ganta a nan ne lafiya?
Sultana kai Tsaye tace"Zawarci ta ke yi mijinta ne ya saketa."
Ta fad'a ko a jikinta har ta na wani Dariya wani abu ya daki zuciyar Sajida.

Sai a lokacin ta kara jin girman nauyin sakin aure ga Rayuwar y'a mace, Shiyasa tundaga ranar ta fara kiran Yusuf domin ta samu ta lallashesa ko zai maida ta dakinsa.
Ammh ya ce mata umarnin mahaifiyarsa sai sanda tace ko zai iya maidata kuma ma shi ya gaji da hallayanta gwara su rabu gabadaya zai fi.
Hankalinta ya yi bala'in tashi tana ganin tun yanzu ta fara ganin Rayuwa kudi ma sun fara yanke mata, ta fara fuskantar rayuwar da bata santa ba.
Umma ba ta bata kudi Abba kuma bata isa ta tunkare ta ba, komai nata ya kare kayan kwalliya kati ma a waya na fara gagaranta gashi ba wata sana'a ta ke yi ba, da aurenta ta ke takama ba da komai ba.
Data ma yanzu ba ta dashi in kuma ta roki su Anty Surayya ta na ganin tasaukar da Ajinta Sadiya ta kan roka ta wurga mata 1gb daga baya itama sai tace ba kud'i a hannunta.

Sultana kuma ko ta na dashi bazata bata ba, tunda ta taba rokonta 5k tace itama ai d'aya suke tunda Mijinta baya tare da ita yana can tare da kishiya.
Kuma tasan ta na da kudi Sadiq ba mutum ne mai mugunta ba.
Umma kuma bata ko bi ta kanta ta na ta yi ma Sultana Shirye shiryen komawa gidanta cikin satin nan.
Ta kuma siya mata kayan gyara na abunda uwa zata yi ma yarta, daga Shinkafi ma Matan Babanta sun aiko mata da mganin sanyi da Tsumin Amare.
Itama ana ta bangaren da Taimakon  Surayya ta gyara Sultanan sosai, kuma ta yi mata kyakyawan Jego mai kyau ta maida jikinta ta yi sharr  ita da Ummi.
Sadiq ya yi waya da Umma zai dawo ranar jumma'a.
Suna zaune a falo a daran Laraba ita da Sajida ita Sajida wayarta ke hannunta ba ko data game ta ke yi ta na rage zafi.
Ummi na bayan Ummi ta goyata bayan ta gama yi mata wankan yamma sai ta samu barci.
Sultana kuma tunda ta shiga ciki sallah bata fito ba.
Umma ta yi zaune ta na kallon Sajida ta na kara nazarinta kamar ta na bata Tausayi ammh bata so ta nuna mata tana jin Tausayinta.
Kuma har Allah ta ga abunda Mallam da Sadiq suka rika gayamata.
Ba ita ke da littafin kaddara a hannunta ba  Allah ne itama ko ita kanta bata wuce zama bazawaran ba.
To ga shi bai faru da ita ba ya Faru a kan yarta itama Sajida ta na daga cikin masu kyaamatar bazawara da aibata kaddaran da ba mutum ya zana ma kansa ba.
Sajida duk ta rame ta yi baki kamar ba ita ba, Umma ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Sajida wai nace baki kira shi Yusuf din ba ne?
Sajida ta kalli Umma cikin wani yanayi kafin tace"Umma ya ma daina daukan wayata yanzu, yana so na fa duk sharrin kannensa ne da uwarsa."
Umma ta kalleta kai Tsaye kafin tace"Uhm ashe har yanzu da Sauran ki ban sani ba Sajida?
Sajida ta tura baki kafin tace"Umma to ni me na yi? Har da ya'yana sai ya rabani da su?
Sai idanuwanta suka ciko da kwallah tana kaunar ya'yanta Damuwarta akansu ma tafi yawa, tunda ta yi aure ba ta taba kawo ma kanta zata iya dawowa gida ta zauna da sunan wai mijinta ya saketa ba, hasashen da bata tab'a yin kamarsa ba.
Ganin abun ta ke yi kamar a mafarki, kuma tabbacin ba mafarki ba ne.
Suna nan zaune sai ga Sultana ta fito tana fad'in"Umma yaushe zan tafi Shinkafi na kai ma Baba Ummi ya ganta ne?
Umma tace"Sai ki jira mijin ki ya dawo in ya barki duk sanda kika Shirya sai ki tafi."
Kai Tsaye Sultana ta zauna kusa da Sajida ta na fad'in"To Umma shikenan ma sai Anty Sajida ta rakani saboda Daukan Ummi."
Daga Umma har Sajida sai da suka kalli Sultana ita ko har acikin ranta ta yi mganar.
Umma ta kauda kai ta na fad'in"Sai kuje tare itama ta kwana Biyu ba ta je ba"
Sajida na gefe ta bi Sultana da wani kallon Lalle ma yarinyar nan..
Cikin gatsali tace"Ke ba inda zani."
Sultana ta kalleta cikin mamaki tace"Saboda mene?
Kawai sai Sajida ta mike a fusace ta na fad'in"Bansani ba mara kunya kawai."
Ta fad'a lokaci daya ta na wucewa cikin Daki a fusace.
Suka bi ta da kallo Sultana ta kalli Umma Lokaci d'aya ta na fadin"Umma me ya samu Anty Sajida kuma?
Umma ta ce"Ina zan sani, me yasa baki bita kin tambayeta ba?
Sultana ta tabe baki kafin tace"To ni me na yi mata da zata ce min bani da kunya?
Umma na jinta ta na kunkuni bata tsnka mata ba, ta yi kamar ba ta ji ta ba.
Ganin Umma ba ta bata fuska kan mganar Sajida ba yasa ta sauya Hira da fad'in"Umma zan sha yawo har Abuja zani fa."
Umma ta kalleta a karkace kafin tace"Gidan wa zaki je a abuja?
Kai Tsaye tace"Gidan mijina mana, kema Umma da wata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login