Showing 72001 words to 75000 words out of 116366 words

Chapter 25 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

313

da sultana."
Kallon Umma ya yi, sai dai bai yi mgana ba kad'a kai kawai ya yi kafin yace"to Umma shikenan."
Ita kuma tace hakane saboda bata son su Asim din su yi nesa da ita.
In suka koma Abuja ai sai ta Dade bata gansu ba, kuma yanzu yadda take kaunar yaran nan bata jin ko iyayensu suna da iko a kansu yadda take jin tana da shi.

Daganan Shima gida ya koma sai dai yana ta auna mganar Umma, ya Fahimceta Saboda su Asim ne, shima kuma yana Tunanin haka Siya ta fara zama Gusau in ya samu Ma'aikatansu sun saka hannu a takardan ba su Loan gida da Mota shi sai ya karb'i na gida duk wata za'a rika cirewa a albashinsa.
Gwara dai ya fara natsuwa waje daya shi kanshi ya gaji da duk bayan sati yana Hanyar Zariya ko hanyar Gusau.
Ya kamata ya natsu waje daya ko shima ya samu cikakiyar natsuwar da ya ke fata.
Har daki ya bi Sultana ya yi mata sallama ta na kwance, ko dago kai batayi ba ta amsa masa kamar bata son ta yi mgana.
Shi kuma bai damu kansa ba ya ijiye mata kud'i saman Side drower d'in gadon da ta ke kwance ya ficewarsa lokaci daya yana girgiza kansa, shi a tarihin zamansa da Siya ba tab'a masa irin wannan ba, shi fa a zamantewarsa da Siya sai dai shi ya ji kunya in ya yi mata laifi ammh ita bata taba yi masa laifin da yaji ta bata masa rai ba.
Sai dai abunda ba'a rasa ba, na zamantakewar yau da gobe.
Share Tunaninta ya yi saboda Tuki zai yi kada taje Tunanin ya yi masa ya kara samun matsala.
Kafin ya tashi sai da ya kira Siya ya gayamata zai kama hanyar Abuja cikin yanayin mganarta tace"Assadiq yau da rana kuma zaka tafi?
Kai Tsaye yace"Zan shiga Office da wuri ne Siyata."
Bata damu sai ta kara jin wani Dalili ba, ta shiga yi masa addu'an fatan isa lafiya har ta na kara masa gwarancin su Asim.
Kafin su yi sallama haka ya Dauki hanya cikin Farinciki tuni ya shafe Tunanin Sultana ballatana Sakarcinta.
Sai bayan mangriba ya isa Abuja Abba ya yi ta kiransa yana hanya sai da bayan ya natsa ya yi sallah yaci abinci sannan ya kira shi suka yi mgana.
Bayan nan ya kira Siya ya gayamata ya isa, itama ta na ta kiranshi yace bai Sauka ba.
Umma kuma daman tana tare da Abba domin yaji muryanta Lokacin da suke waya.
Sultana ma ya kirata Saboda ya fita hakkinta kira Biyu sai ana uku ta Dauka tana wani cin mgana shi dai bai Tsaya nuna ya gane fushi ta ke yi ba yace mata ya isa lafiya.
Kawai Ok tace ta kashe wayarta sai ya yi Sororo a fili ya Furta"Yarinyar nan ta yi nisa."
Danne bacin ransa kawai ya yi saboda hakane ma sai kawai ya Kira Tahir ai sai yaji Tahir na amfani da wayar. sabodq yakuresa yasa ya yi ta kara kiransa wajen sau biyar duk bai gama wayar ba, wajen awa daya sannan sai gashi ya Biyo kiran Sadiq din yana Dauka yace"Wai lafiya ka ke ta min kira ba daga kafa?
Sadiq yace"Allah ya baka Hakuri ai bansan ka fara Serious Soyayya ba ne."
Sai Tahir ya yi shuru bai yi mgana ba, Sadiq ya sha Mur kafin yace"Ina taya ka Murna, sannan barka iyayen yara za su huta da tsabar yaudaran musu ya'ya da ka dinga yi a baya."
Tahir ya yi dariya kafin yace"To nagode, kasan komai Time ne nima ina ji a jikina Lokacin da zan yi aure ya kusa in sha Allahu."
Sadiq na dariya yace"Eh lalle to Ameen."
Daganan suka cigaba da Tattaunawa kan lamarin na wani Lokaci kafin su yi sallama.
A ran Sadiq yana jinjinama wannan yarinyar da ta iya sace zuciyar Tahir farat daya haka akanta ne kawai yaji Tahir ya nuna cewa lokacin da zai yi aure ya kusa.
Tunda ya koma kullum da Safe in ya Kira Siya itama Sultana zai kirata yaji Lafiyanta.
Ko da bazata amsa dakyau ba, shi dai daman Saboda ya Fita hakkinta ne.
Ranar alhamis da ya kirata da daddare bayan sun gaisa ya ke kara mata Tunin inda Siya zata sauka.
Kai Tsaye Sultana tace"Ni fa na gayamaka bani da masaukinta a gidana, kuma duka kayan da ke cikin gida nawa ne naga ba Dakin da bakomai a ciki ballatana kace na Sauketa aciki."
Mamakinta ya kara kamashi Saboda Haushi sai kawai yace mata"Sulatana ki yi duk abunda ki ke so, lokacin ki ne."
Daga haka ya katse wayarsa, Sai ya kira Big sis ya so ya fad'a mata abunda ya Faru tsakaninsa da Sultana ne sai kuma ya fasa a ransa yace ai shi Namiji ne shi zai Dauki matakin da ya Dace.

Kawai sun yi mganar sai ranar lahadi zai zo gusau tunda sai Ranar asabar zai je zariya ya kwana washegari ya Dauko Siya su taho tare.
Duk da Surayya sun yi waya da Hasiya ammh bata nuna ma Sadiq ba Tunda wannan kuma sirrin su ne ita da Matar kaninta kamar yadda shima kanin nata akwai sirri a tsakaninsu sun yi mganar Umma har ya gayamata abunda Umma tace masa Ranar da zai koma.
Surayya ta yi dariya kafin tace"Ai Umma na kaunar yara nan ina jin nan gaba ana yayesu zata kwace muku su."
Shima cikin dariyan yace"Sai mu bata, ina fatan mu samu wasu kafin a yaye sun."
Surayya tace"Kai Sadiq, gwarne ka ke so Hasiyan ta rika yi?
Yana yar dariya yace"Matar so fa ita ke gwarne kin manta ne Big sis.!
Ta hararesa kamar yana ganinta kafin tace"Bansani ba sai ka fad'amin."
Sai ya kwashe da Dariya ta na tayashi.
Sun yi mgana Sosai akan Umma Surayya ta nuna mai su cigaba da addu'a in sha Allah Umma zata dawo yadda suke so.
Daman har da zugan su Sajida kuma yanzu ta daina Biye musu.
Sultana me suke samun nasaran yi mata Famfo son ransu.
Shi fa Daman Sadiq ya sani Abubuwan da Sultana ta ke yi ba Wayonta ba ne.
Shifa har mamakin Sajida ya ke yi, matar nan ko shed'an in ya ganta sai ya sara mata wajen Tsabar Munafunci.
Duk zai kyalesu yanzu daman ya yi musu iyaka da matarsa su je ita kuma ta Biye musu su kaita su barota shi dai in ya gaji da tarata ya Faceta har Abada ta facu kenan bazai maida Dattin abunda ya fitar a hancinsa ba.
kamar yadda yace Ranar asabar da misalin sha daya na Safe ya dira a Zariya ya iskeni na yi masa kyakyawan Tarba kamar yadda na Saba ni da ya'yana.

********

Daran yau dai su Asim ba su yi ma Babansu kara ba kwana suka yi kuka, bamu yi barci ba daga karshe ni yace naje na kwanta ganin akwai barci a idona.
Yace naje na kwanta tunda ina jin barci shi zai kula da su, Allah Sarki bawan Allah duk farkawan da zan yi yana Rike da su duka yana Faman jijjiga in ya gaji ya koma ya zauna a gefen gado ya kwantar da su, ya Fara Daukansu d'aya bayan d'aya yana basu Madaran su.
Ni uwace kukansu yasa na kasa natsuwa na yi barci dole na mike na isa garesa na mika Hannu ina Fadim"Assadiq kawo su, kaje ka kwanta ka yi tafiya akwai gajiya a jikin ka"
Kallona ya yi cikin so da kauna kafin yace"ni nace kije ki kwanta Siya zan kula da su kinga ai sun fara rage kukan na su ko?
Cikin wani yanayi nace"Haka muke fama da su, ammh na yau yafi na kullum wlh, kawo su kaje ka kwanta Tunda gobe muna da tafiya a gabanmu."
Kin bani su yayi, yace sai dai na basu Nono na koma na kwanta.
Haka na zauna yana rike da Asim na fara ba ma Asif Nono sannan na karbi Asim na bashi shima.
Gaahi sun koshi sun kuma daina kuka ammh yaran nan sun ki yin barci idanuwansu kyar suna kallon kowa.
Cikin Tausayinsa na kallesa Wlh akwai gajiya tare da shi, tare da barci ammh yaki zuwa ya kwanta.
Cikin taushin murya nace"Kaga fa kana jin barci kawo su don Allah."
Cikin Kaushinsa yace"Nace ki barsu ko? Ni da ba na zama ke fa kadai kike wahala da su yanzu na dawo ki bari nima na tayaki mana Siya."
Yadda ya yi maganar ne yasa wani kaunarsa ya kara kamani naji wani Shauki na Dibana.
Kawai sai na saka kaina saman kafad'arsa ina fad'in"Ina sonka Assadiq, na tabbata cikin maza Dubu sai an tona an kara Tonawa kafin a samu kamarka, Allah na gode maka Sannan yau na kara godema Amma da ta yi min kyakyawan zabi a Rayuwata.".
Yana yar dariya yace"Ba kin ce baki so ba? Alokacin har rashin kunya kika so ki yi ma Amma wai baki sona?
Dariya na saka ina fadin"Ba rashin so ba ne, kawai ina Duba manganun da ke kaina ne. Ina sonka Tun a Lokacin ka Fahimci mganata ba na son wani mummunan abu ya sameka ne ta Sanadina."
Mirmishi ya yi mai Tsada kafin yace"ba abunda ya isa ya sameni face abunda Ubangiji ya kaddaromin acikin kaddarata."
Kwanciyar da yaso na yi ban yi ba, hira na zauna muka yi ta yi, yaran nan kuma sai gabda asuba suka yi barci.

Shiyasa sai bayan ya Dawo masallaci ne muka kad'aice da juna ta inda na kara sara ma magungunar gyara na marubuciya Surayya dee shine yadda Assadiq ya ke min rawan kafa da na Jiki in muka had'u da juna.
Daganan na Bata Makin dari bisa dari kan duka mgangunanta na Sanyi da na gyara ga Gimbiyar kaza, tare da Tabntabaru Shiyasa ni yanzu ba na siyan kowani kayan gyara sai ta hannunta, kayanta masu inganci ne sosai +234 803 277 3332.

Da safe kuma sai shirin Tafiya Daman na gama shirya akwatina da na yara.
Tare da Tsaraban da zan tafi da shi da ko Assadiq bai sani ba.
ya dai ganni da Ledoji har sai da ya yi mganar na Dauki a ledoji kamar wata bafullatana.
Ina Dariya nace"Ita ce baka yi b'atan kai ba."
Karfe goma saura muka bar gida na yi sallama da Maman suhailat da Ummi da ke gida daganan muka Biya gidan Adda Fati na karbi sako, ba ma mu shiga ba ita ce ta leko muka gaisa da ita har ta leko mota ta na yi ma su Asim wasa da suke kan jikina sai Faman ware ido suke yo suna gane gane.
Watansu fa Biyu ne da wani abu ammh har sun yi wayau, ga shi sun yi Kiba gwanin ban sha'awa.
Haka muka Dauki hanya muna tafe muna Hirarmu ta masoya gwanin ban sha'awa kuma kamar yara nan su san tafiya tsit sukayi daga karshe ma sai barci suka yi ta yi, sai gabda zamu isa sannan suka Farka.
Muna hanya Ramatu ta kirani nace mata mun kusa isa ma, sai ta yi mana Fatan sauka lafiya.
Kafin isarmu Umma ta kirani shima ta kirashi yafi sau uku tana tambayan muna ina? Muka ce muna hanya.
Tace to mu fara sauka ta gida tukunnah.
Alokacin har ya kalleni yana Fadin"Siya kinga abunda na ke fad'a miki ko? Watarana Umma zata kaunace fiye da tsamnanin ki."
Sai na yi mirmishi kafin nace"Hakane,  daman ka sha fad'amin watarana komai zai zama Labari."
Mun isa Gusau Biyu da wani abu na rana Tunda Assadiq bai yi gudu ba Sosai.
Tarba da na samu a gidansu Assadiq ban taba Tunanin zan sameta ba, Umma da kanta ta fito ta tarbanmu, ta fara kwasan jikokinta bakinta har kunne, ni kuma Siyama da Farida na yi min barka da zuwa.
Shashen Umma na fara sauka ni da kaya, ta kaini dakin da Sultana ta zauna tace na yi sallah kafin a kawo abinci.
Su Asim kuma Tunda muka zo suka bar hannuna, suna hannun kakarsu sanda Su Siyama suka kawo min abinci naga asif a bayanta ta Goya tace min Asim na bayan Umma shima sai barci ya ke yi.
A raina nace Lalle yan Biyu kyautar Allah, Assadiq kuma ashe gida ya tafi sai da muka yi waya ya ke gayamin.
Har yana Tsokana da cewa"Gwara na bar ki da surukarki ku gaisa da kyau."
Ina gama cin abinci na fito falo na kara gaida Umma ta amsa cikij yar sakewa, har tana ce min me na ke bama su Asim sun yi wayau da girma haka?
Kaina na kasa nace mata madara ce kawai.
Ita kuma kai Tsaye tace"Kina da nono mai kyau ne."
Na dad'e zaune ita ta na Dauke da Asim sai faman jijjigaahi take yi da ya Fara kuka ni kuma ina zaune a kasa cikin Ladabi.
Ganin ya ki daina kuka yasa ta Saukoshi ta bani shi tace na bashi Nono, kunya ta saka na kasa bata a gabanta da ta Fahimci haka sai ta Shige ciki ta barni sai da na gama bashi ta fito.
Da kanta tace naje na gaida Mama da innani na kai musu yaran su gansu.
Kila ma naga su siyama shaahen mama ko na Innani Asif na Hannunsu.
Ban yi musu ba na mike, gani ta yi ina Kokarin ijiyesa saman kujera da Sauri tace"Ya zaki ijiyesa?
Cikin Ladabi nace"Zan dauko wani abu ne Umma."
Da sauri ta kariso ta karbesa ta na fad"in"Sai ki bani shi na rike miye amfani na?
Ni dai ina jin kunya na mika mata shi, ta karbeshi ni kuma na shiga ciki na dauko Tsarabata na ciro na Umma da na Mama sai na Innani, sauran kuma na Abba ne da su Siyama har da Sultana ma na yi mata tsaraba.
Ina fita falo da leda a hannuna na duka a gabam Umma na ijiye mata ina fadin"Umma tsaraba ce ba yawa."
Sai naga ta washe baki kafin tace"Ah harda wahala?
Masha Allah Allah yasa albaarka.*
Bata Bude ba sai da ta bani Asim na rike a hannuna sannan ta zauna ta Bude ledan.
Yaji ne da ya ji  dakada Nama da Tarfanuwa gashi yaji maggi.
Sai Turaren Wuta na daki da Humra.
Umma ta washe baki ta dago ta na kallona kafin tace"Wa ya gaya miki duk abunda na ke so haka?ko magajin gida ne?
Mirmishi na yi mata batare da na yi mgana ba, Anty Surayya na kira na Tambayeta ta fadamim Umma na son Yaji sannan a bata Turaren kamshin Daki da Humra ta na Daraja wannan kyautar.
Kuma naga haka, Domin ta nuna min jin Dadinta Sosai ta na min godiya karon Farko da ta kalleni tace"Nagode Hasiya Allah ya yi albarka."
Na amsa da Ameen cikin jin dadi, Sai ta Bude yajin ta lasa ta fara Santi ta na kara min godiya.
Shigowar Farida yasa Umma tace ta rike ledojin mu tafi bangaren mama.
Farida na gaba ina baya rike da Asim zuwa bangaren Mama.
Na iske Anty Sakeena a bangaren Siyama ma ta na ciki Asif na Hannun Mama itama ta reno.
Tana ganina ta washe baki ta na fadin"Kaga fara mai Farar Aniya, ana zencen ki sai kuma a ganki."
Mirmishi kawai na yi, Sakeena ta tashi ta karbi Asim a hannuna..
Ni kuma sai na Duka kasa ina gaisheta ta amsa cikin kulawa.
Na juya na gaida Anty Sakeena itama ta amsa cikin Fara'a kafin tace"Yara nan fa girmansu ya bani mamaki kamar sun yi wata Hudu' wai sannu da kokari."
Mirmishi na yi ban yi mgana ba, na karbi leda guda daya hannun Farida na tura gaban Mama ta dauka ta na fad'in"Me kuma muka samu?
Sai taga Turaren rushi sai na Tsinke masu kamshi Tafiyayye d'an maiduguri wajen makociyar Adda Rukkaya na siye shi."
Mama ma nata godiya har Anty Sakeena sai da ta yabi Turaren nan tace Umma zata san mata.
Siyama na kallah ita da Farida kafin nace"Kuma tsaraban ku na nan sai kun zo amsa."
Sai suka fara Murna, na jima a bangaren Mama sannan Sakeena ta Rakani har Bangaren Innani.
Mun isketa kwance baiwar Allah ashe bata jin dadi zazzabi ta kwana dashi ta kuma hana Farida ta fad'a ma kowa .
Shuru shurun da ta yi mana ne yasa muka san bata da lafiya.
Sakeena ta aika Farida ta kira Umma tazo ta gani.
Sadiq ta kira ba jimawa sai gashi yazo Tunda Abba baya gida.
Innani bata son asibiti dakyar ta yarda Sadiq ya bata abinci a baki ya kuma bata maganin ciwon kai.
Yana ta ma Faridan fad'an ta daina Biye Innani da ta ga wani matsala tazo ta yi mgana.
Yarinyar ta bani Tausayi sai sharan kwallah ta ke yi, a bagaranta muka zauna da Sakeena ashe ta na da mgana muna ta Hira da ita.
Mune har mangariba,Allah Sarki Innani sai gashi taji Sauki har ta na Daukan su Asim.
Ita Nama na kawo mata soyayye Saboda Anty Surayya tace ta na so, aiko na sha addu'a da Godiya.
Anty Sakeena ta tafi gidanta ni kuma ina Tare da Innani a bangarenta tare da su Siyama.
Bayan isha'i sai ga Assadiq da Abba sun shigo Dubata anan muka had'u da Abba na duka ina gaishesa.
Assadiq kuma ya kwashi su Asim ya kai masa ya rikesu yana Dariya.
Mun gaisa dashi Cikin sakewa kamar yadda muka Saba.
Ya saki jiki muna ta Hita daga karshe har Umma da Mama nan shashen  suka dawo suma.
Anan kuma suka ci abincin dare ni dai Saboda kunya ina cikin Dakin Innani ni da Farida.
A falo kuma Abba na ta yi ma su Umma Tsiyan sun ga fararen maza sun yi masa kishiya.
Mama taja Asif tace shine mijin Robanta Umma kuma ta rike Asim.
Innani na zaune tana dariya a ranta tana jin wani Farimciki ganin Sulaimanu cikin Annushuwa.
Sadiq ma ransa Fes sai mirmishi ya ke yi.

A daran Surayya ta zo min Sannu da zuwa, Abba ne ya yi ta fad'an me yasa ta fito bata bari sai da Safe ba.
Shiyasa bata dade ba ta tafi gida, ni kuma Assadiq yace na shirya mu karisa can gidan, Kafin mu tafi na bama su Siyama Tsarabansu na mayafai sai kayan kwalliya.
Abba kuma Turare mai kamshi na kawo masa ya yi ta saka min albarka.
Su Umma sukaji kamar kada su barni na tafi da su Asim suna ta cewa Gobe da Safe suna jiran magidanta nasu.
Sai goma na Dare muka isa gidan Assadiq.
Gidan ya yi min kyau, madaidaici da Shi da zamu shiga megadi na gaisheshi ya amsa yana gayamasa ni ce uwargidansa ga ya'yansa nan.
Megadin bahaushe ne ya yi ta saka ma su Asim albarka.
Bansan cewa Sultana bata so saukata a gidanta ba sai da muka iso muka iske ta Rufe kofar falo.
Sai dai ta manta yana da key din gidan tare da keys din motarsa ya ke a had'e da shi ya yi amfani ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login