Showing 45001 words to 48000 words out of 116366 words

Chapter 16 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

315

Abba ka hana su zuwa gidan nan basa yad'a komai sai sharri akaina da Matata."
Abba na dariya yace"Ka kyalesu duk su yi su gama, ai ba su isa su ja da ikon Allah ba."
Jin abunda Abba yace ne yasa sai ya bar mganar.

An riga an yi sallar azahar Abba kuma ya tsaya a chan ya yi tashi, shi kuma sai ya yi nashi a bangaren Abba.
Sai da ya idar da sallah ya Kira Big sis yace sun iso shi da Hasiya Tun dazu.
Surayya tace shine bai kawo ta gidan ta ba? Shi kuma yace ya na Tsoron ya kara yin laifi.
Dagachan Bangaren Surayya tace"Ba wani laifi, bazata sake acan ba ne, zan zo anjuma sai mu taho tare wajena daganan ma sai taga kayan da na siya mata ko?
Kai tsaye yace"Shikenan sai ki zo kawai ki Daukemu tunda nima Umma ta daina ya yina."
Surayya tace"A'a chan kai da Mamanka ni kanwata kawai zan dauka kaji ma na gayamaka."
Daga haka ta katse wayarta yana mata Dariya.
Sai da ya koma Bangarensa sannan ya kirani a waya yana jin kunya shiga Dakin Mama.
Ni ko sai da na yi mgana aka bani daki na shiga na kama ruwa na yi sallah ina zauna na yi tagumi kiran Assadiq ya shigo wayata.
Shi ya debemin kewa da Hiransa yana bani Labarin yadda suka yi da Tahir ya kirasa yana tambayansa wai daman ciki ya yi min?
Sadiq yace"Eh mana na yi kankanta da yin cikin ne?
Tahir ya yi tsaki kafin yace"Dan iska, kawai."
Na yi ta dariya ina fadin bai kyauta ba, shi kuma yana cemin Tahir ne yaja domin ya yi masa tambayan Renin wayau.
Sai da muka fi awa muna waya sannan yace naci abinci sai na yi masa karyan naci, jin haka yasa yace na kwanta na huta.
Daganan muka yi sallama kamar kuma yadda yace sai na kwanta sai barci Saboda gajiyan mota. sai bayan la'asar na tashi Lokacin ne naji ana ta Hidima na gobe sallah.
Ina bangaren Mama har bayan shan Ruwa sai lokacin Siyama ta kawomin abinci ta na min wani kallo.
Tuwon shinkafa miyar egusi, sai kuma Ferfesun kayan ciki da lemun kankana.
Naci kad'an saboda bana jin yunwa sai na sha lemun, bayan na idar da sallah na kira Assadiq na yi masa barka da shan Ruwa sai yace na fito zamu gaisa da Abba.
Da Tulin Cikina gaba na sanyo Hijabi na samu Mama da Siyama afalo nace mata Assadiq na kirana zan je na gaida Abba ta bi ni toh shikenan.
Ina fita haraban gidan na Hangosa shi yazo ya rikeni har bangaren Abba.
Muka had'e da Umma achan ta na had'a ma Abba kayan Bude baki..
Zan duka yace na zauna a saman kujera na zauna muka gaisa cikin Sakewa yana tambayana ya karatu nace masa mun gama jarabawa.
Kai Tsaye yace"Ki saki jikin ki fa, nan ma duk gida ce kuma zaki ki ji dadin salla tare damu."
Mirmishi na yi kafin nayi masa godiya umma kuma tana gama abunda zatayi ta fice ko amsa min barka da shan ruwan da na ke yi mata bata yi ba ta Fice.
Abba da Assadiq tare suka yi Bud'e baki, ni kuma sai nace bari na taka zuwa bangaren Innani.
Na gane gidan yanzu kuma na kai kaina bangaren Innani ina shiga sultana na fitowa ta dawo kai Innani Ruwan zafi.
Muka kusa cin karo sai muka tsaya muna ma juna kallon kallo
Ni ce ma na kauda shurun ina Mirmishi nace"Sultana."
Duk da ina jin wani abu a raina ammh sai na Danne.
Ita ko wani irin banzan kallo ta yi min kafin kawai ta bangajeni ta wuce a bakinta naji tace"Banza mai kwacen miji kawai."
Ni ba wannan na damu ba sai bangazar da ta yi min kamar bata ga bani kad'ai bace.
Bango na Dafe yasa ban fadi ba, na bita da kallo ina jinjina kai.
Da sallama na shiga Falon innani suna zaune da Farida.
Da farko bata ganeni ba sai da na yi mata bayani tunda itama Faridan bata sanni ba.
Aiko sai ta washe baki ta na ta min Dariya ta fara min fira labarai harda na Umma da ta hana sultana komawa gidanta.
Tace min"To ni in na saka baki sai ayi cewa na zabe ki naki jikata, kinsan mutane ba'a iya musu. Kuma ni na saduda ne na bi Allah Tunda sulaimanu da magajin gida suka min nasiha na yi shuru da bakina kada na Tofa ace na yi munafurci."
Ni dai sai dariya na ke yi mata, Innani akwai dadin zama.
Dan zaman da na yi a bangarenta na sha Labarai kala kala harda na chan mutanen shinkafi.
Sai zuwan Surayya ne ya tada Hirarmu tace daga wajen Su Abba take Sadiq yace ina sashen Innani.
Ta zauna itama ammh bata dade ba, tace na taso mu tafi na yi ma Innani sallama sai da muka fito ne muka had'u da Sadiq.
Sai da na shiga mota sannan suka koma gefe suna mgana da Anty Surayya na wani Lokaci sannan suka yi sallama ya lekoni yana fadin"Siya Good Night"
Sannan ya sumbaci goshina Surayya na fadin"Sadiq ba kunya a gabana."
Ya matsa baya yana dariya.
Tun a mota muka fara hira da Anty Surayya da muka je gidanta ma na jima afalo muna Hira har da mijinta sai da na fara jin barci ta kaini inda na ke sauka tace na yi wanka na Huta.
Ta kuma kawomin man zafi na shafa aiko ina yin haka sai barci.

Da safiyar idi kuma an tashi da hidima duk yadda naso na taimakamata hanani ta yi, tace na shirya in zan iya mu tafi masallacin Idi nace mata zan iya.
Ta bani kayan da Assadiq ya yi min kala uku leshi daya Atamfa biyu.
Atamfar na saka an dinkamin Buba kamar an aunani Cif dani.
Sai bakin Hijabi sabo saboda Fatata sai ya yi min bakyau kamar wata baturiya. itama ita da mijinta da ya'yanta sun yi kyau sosai shi ya tukamu zuwa masallacin idi.
Chan muka had'u da Assadiq da Abba bayan an sauko masallaci sun sha Fararan kaya har da manyan Riguna.
Sama sama muka gaisa yace sai ya zo gidan.
Da muka koma gida abinci muka ci Sinasir Anty Surayya ta bada aka yi mata, ni kuma bayan na ci na koshi na koma daki na kira yan'uwana da abokan arziki na yi musu barka da Sallah da Ramatu ne muka jima muna waya.
Bayan mun gama na ijiye wayar na kwanta sai bayan azahar na tashi Anty Surayya tace na sha barci har Sadiq yazo ya tafi.
Sai da na yi salla ta kwasomin kayan da ta siya na jarirai shago guda ina ta kallo ina saka albarka
Mun dade muna Hira da ita ta na kara bani baki akan Umma ta na tabbatar da zata sauko watarana.

Sai Dare Assadiq ya dawo bamu wani jima muna Hira ba ya tafi saboda na fara jin barci washegari ma Dangin mijin Anty Surayya ne suka zo.
Shiyasa bamu je gidan su Assadiq ba sai Washegarin sallah da kwana Biyu.
Na sanya leshin nan Shima dinkin Buba ne, ya zauna a jikina sai na sanya Hijabi kalan adon leshin.
Muna mota Anty Surayya ke fadamin Saboda ni yam'uwanta wannan sallar ba wanda yazo gidanta. Kuma sun saba a jiya kannen nata suna zuwa wajenta su yini.
Muna zuwa gidan ko suna nan a shashen Umma, Sadiya da Sajida sai Sa'adatu Saddiqa kuma Tunda ta koma bata zo ba, ya yi kusa da yawa.
Shashen Mama duk ya'yanta ne su Sa'ima da su Shahida har Salima ma tazo sallah.
Dukkansu kuma a shashen Innani muka gansu dukkansu kuma na bi su na gaishesu suka amsa min a wulakance, wasu ma ba su amsani ba.
Innani kuma ta karbeni cikin Fara'a kamar yadda ta saba min na riko mata Turare daman tundaga Zariya na bata ta karba ta na ta saka albarka su Sajida nata tabe baki.
Umma kuma har bangarenta mukaje na gaisheta sai a ranar ta amsamin da lafiya.
Daman kuma bangaren Mama muka fara zuwa muka gaisa, Abba kuma baya nan sun fita da Assadiq.
Anty Surraya tace mu zauna a bangaren Umma, ita kuma ta bi Umma ciki ban san me suke Tattaunawa ba.
Na jima zaune ni kadai sai ga Sultana ta shigo da irin less din dake jikina.
Kallon kallon muka yi ma juna ina shirin na gaisheta naga ta yi tsaki ta wuce kawai.
Kiran sallar mangariba yasa su Sajida suka baro bangaren Innani zuwa Falon Umma.

A d'ayan bedroom din Anty Surayya ta kaini na yi alwala na yi sallah.bina zaune ina addu'a Sultana ta shigo ta yi kuma mamakin ganina sai da ta Tsaya shuru sannan kuma ta koma da baya.
Sai da na natsa sannan na fito falon Anty Surayya bata falon ashe waya aka kirata sai ta fita.
Ina shigowa falon sai na tafi kujeran chan nesa da su zan zauna har ga Allah ban ga Tahowar Sultana ba.
Sai da naji ta min wani bangaza kamar na ranar.
Na kusa faduwa da yasa hankalina ya tashi sai da na Dafa kujera.
Cikin sauri nace"Sultana kamar baki ganina?
Sai gabadaya Hankalin su Sajida ya koma kaina.
Kallon cikin ido ta yi min kafin tace"Au Allah? To ban gan ki ba."
Sai alokacin na Lura ta sauya kayan jikinta.
Batare da na kara mgana ba na gyad'a kaina na koma na zauna ina daidaita yanayina.
Sajida ta yi tsaki kafin ta kalleni ta na fadin"Ko da ta ganki ke ya kamata da kika ganta bayan kin kauce mata sannan ki ramkwafa ki gaisheta da ladabi."
Sadiya tace"Tabbas tunda ita kika yi ma kwacen miji."
Na yi shuru ban yi mgana ba Sadiya ta dakamin tsawa ta na fadin"Bazaki duka ki gaisheta ba?
Sai kawai na sauko daga kan kujera na Duka kan kafafuwana ina cije baki na kalli Sultana dake tsaye nace"Ina yini sultana?
Idanuwana sun ciko da kwallah.. shewa suka saka gabadayanau suna min dariya.
Sajida tace"Kowa ya tuba  don wuya.".
Sadiya ta karishe da fadin"Ba lada."
Ba su sam shigowarsa ba  ni kaina kamshin Turarensa naji da kuma dagoni da ya yi daga durkushen da nayi.
Sai jin muryansa suka yi ya na fadin"Are u ok?
Sai na gyad'a masa kai.
Shuru suka yi sun sha jinin jikinsu, kallonsu ya yi a fusace kafin ya Tsaida kallonsa kan Sultana da wani hade rai tana marmari da ido.

Har gabanta ya taka bayan ya sake ni, ya tsaya kam sannan ya daga hannu ya nunani kafin yace"Kinga wannan?
To itace matar da na fara aura kafin ke, saboda haka daga yau ya kamata ki sani tana gaba da ke, ke zaki fara girmamata kafin ita ta girmamaki."
Sultana ta kallesa kafin tace"Tab."
Ta fad'a ta na Tura baki.
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Eh haka nace saboda haka daga yau in kika ganta ke zaki gaisheta ki, ya kamata ki haddace cewa ita na fara aure kafin ke, ni kuma ba sakaran namiji ba ne da zan zauna kina wulakantamin mata ba, Sonta na ke yi shiyasa na aureta kamar yadda kema ina sonki ne yasa na aureki."
Sultana sai hawaye ta na so ta saka kuka.
Sajida ta gaji da shuru tace"Ammh Sadiq baka da kunya wlh."
A fusace ya daga mata Hannu kafin yace"Ban saka da ke ba mallama ki Rufemin baki, ko ina ruwan ki da shiga Hurimin iyalaina.?
Ya karishe fad'a yana nuna ta da yatsarsa.
Ai sai ta kasa mgana ganin ya harzuka Sadiya ma na shirin magana a harzuke yace"Kada wace ta kara sakamin baki acikin magana ta da iyalaina. In ba haka ba  ran mata zai baci na rantse da Allah."
Surayya ta shigo tana gefe ta na mirmishi.
Kan Sultana ya koma yana fadin"Sabosa haka ki shiga taitayinki, in kikace zaki yi ma matata fitsara maganinki zan yi bana son reni kin sani."
Sultana ta mike ta saka kuka ta na Fadin"Ai ba sai ka nun ma duniya baka sona ba, auren hadi aka yi mana shiyasa ka ke kare ma wannan banzar matar taka mai kwacen miji kawai"
Taso mata ya yi kamar zai Daketa ta yi baya sai kawai ga Umma Tsulum a falon.
Shi ya hanasa kara wani motsi ni kaina gabana sai fad'uwa ya ke yi
Sajida na ganin Umma ta Nufeta ta na karanta mata Assadiq ya zagesu saboda ni.
Har yana nufar Sultana zai daketa.
Umma bata wani tsaya Bincike ba ta nuna ma Sadiq kofa tace ya fita ya bata wuri yana Hucin ta hanashi mgana ya fita.

Ni kuma ina Tsaye kafafuna na rawa Surayya ta taso ta wankeni Umma ta d'aga hannu ta na karisowa cikin Falon lokaci daya ta na kallona kafin ta juya ta kalli Sultana tana fadin"Share hawayen ki, matukar ina raye ba wanda ya isa ya Tozarki."
Sultana ko kuka take yi sosai daman ganin kayan mu iri daya yasa su Sajida suka kara Zugata da cewa ita bai Dauketa da Muhimmanci ba muraranta ya ke nuna yafi kaunata sma da ita, ita kuma bakin kishi ke dawainiya da ita.
Umma ni ta kalla a fusace kafin tace"Ai in baki had'a fada tsakanin yan'uwana juna ba baki ci sunan ki  bakar Annoba ba, kin ji kunya kuma kin yi asara ke yanzu a dad'in ki ne ki zo ki raba kan zuru'a? Ki saka d'ana ya na jayayya dani sannan ki sakashi yana Sa'insa da yayyensa to ki saurareni dakyau har Abada bazan taba karbanki a matsayin matar Abubakar ba, Sultana na sani kuma in dai ke ya zaba wlh sai dai na sallama miki shi, shi kadai Annobarki ta kona sa, Fita ki barmin falo kafin raina ya baci na saka ayi miki koran kare."
Daman tun da ta fara mgana na fara kuka ina jin tace na fita na juya ina jin cikina na Juyawa na fita ina kuka.
Surayya ta kalli Umma ba dad'i kafin tace"Umma m."
"Ke ma bita ki fitar min daga falo."
Surayya ta kalli Umma kafin ta kad'a kai kawai ta juya ta bi bayana su Sajida suka rakata da wani kallo aransu suna tunanin Big sis bata kishin Umma.
Ta na fitowa ta ganni ina kuka, sai ta rikeni zuwa mota itama ranta a bace yake Sadiq ta kira tace yazo ya Tukamu zuwa gida.

Ya shiga damuwa ganin yadda nake kuka sai ya fara cewa ita ta lallasheni.
Da damuwa a saman fuskarta tace"Lamarin Umma ya fara nisa, Su Sadiya suna kara zugata ni yanzu kwata kwata ta daina bani fuska."
Sadiq yace"Nima wlh abun duk ya Dameni."
Surayya ta sauke Numfaashi kafin tace"Mallam na gummi zaka je ka sanar ma abunda ke faruwa na tabbata in ya yi mata magana zata ji."
Sadiq yace"Na yi tunanin haka, ammh cewar Abba ne na bata Lokaci Shiyasa ban je na samesa ba"
Surayya tace"Ai kada ka jira, ammh kafin nan gobe ka maida Hasiya gida, zamanta a wajena ni kaina Umma ta fara fushi dani kuma bata da sakewa kwata kwata anan."
Ya aminta da shawaranta yace haka za'ayi in zai kaini Zariya zamu Tsaya anan Gummi din.
Haka ko akayi, tun safe muka tafi Abba kawai da Innani ma yi ma sallama da kanshi ya hanani Shiga wajen Umma, fuskata har ta Kumbura saboda kuka da kuma duka siyayyan da Anty Surayya ta yi min muka taho da su.
Sai da muka fara biyawa Gummi Gidan su Umma kamar yadda yace min suka gana da mallam zakari na wajem awa d'aya.
Da kanshi ya yi mishi bayanin komai, mallam zakariya na ta fad a yace kuma sai ya saba Umma har Abban ma da ya Biye mata.
Sam a gidan ba'a nuna min wani kyama ba nan muka yi azahar muka ci abinci sannan muka dauki hanya.
Sai bayan la'asar muka shigo Zariya ganin yamma tayi yace sai da safe zai wuce Abuja.
A daran ina jinsa ya Kira mahaifin Sultana shima ya karanta masa abunda ke faruwa.
Ran mallan Shitu ya baci yace gobe goben nan zai je ya samu sultana sai ya sab'a mata itama.

Sadiq daman so ya ke daga Umma har Sultanan a yi musu fad'a alokaci daya.
Kwana ya yi yana lallaahina tare da alkwarin  bazai taba barina ba.
Ni na ma b'ata masa Lokaci sai wajen goma ya bar gidan ya kama hanyar Abuja.
Sadiq ya fita cikin Damuwa ga koken koken da na kwana yi.
Ga kuma matsalan su Umma da Sultana gabadaya sun chazamasa kai.
Ya bar kaduna kenan da kad'an baisan yadda aka yi ba motar sa ta kwace masa ba, shi dai yaji mota na Tamaula dashi akan Titi daganan Hankalinsa ya gushe.
Yaji sanda motar ta Tsaya ya kuma san ya jisa zaune a inda ya ke
jini na bin fuskarsa tunda ya saka Seat belt.
Daga nesa nesa yaji ana salati da sallallami tare da mganganun mutane daganan yaji Duniyar ta tsaya masa cak.



*Janafty*
*TMWBK3010*
P

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*



Duk sammakon da Mallam Zakari ya buga daga Gummi zuwa Gusau sai da ya zo ya iske Mallam shitu ya rigasa zuwa daga Shinkafi domin ana idar da sallar asuba ya kamo hanya so ya ke ya yi abunda zai yi. In ya gama ya kama hanya koma can har kuma yaje ya yi yan Harkokinsa.
Sultana sai da ta raina kanta, ta sha Fad'a kamar me, dukanta ne kad'ai Mallam Shitu bai yi ba, bata tab'a sanin cewa ya iya fad'a haka ba Tunda wani abu bai taba had'a su ba, sannan kuma ba ta girma a gabansa ba sai dai zuwa ta na dawowa.
Umma kuma sai ta so ta kareta ita ma Mallam Shitu ya kalleta yana fadin"Maganar gaskiya Hajiya ki daina mara ta baya, da ke har ita baku taki gaskiya ba abunda ku ke son ku aikata ba gaskiya ba ne kuma ba Shari'a bace."
Sannan ya kara kallon Sultana da ke gefen Umma ta na ta faman kuka, har Abba na wajen shi da Innani tunda a shashen innanin ne ake zaman.
Cikin daga murya yace"Ke kuma ki sani in dai kika Boyema zuciya kika ce zaki wulakanta mijin ki, ke ce a kasa matukar kika rasa miji kamar Abubakar ba baki na yi miki ba ammh Wlh tallahi bazaki taba samun kamarsa ba, kuma ina so ki sani bai kamata ki zama Butulu ba, in mahaifiyarsa ta nuna fushi a kansa ta na da gaskiya itace uwa a garesa ammh ke baki da wannan Hurumin tunda kina karkarshinsa ne daidai da rana d'aya in kika sab'a masa sai Allah ya Hukuntaki akan laifin da kika aikata."
Sultana na kuka Fuskata duk hawaye ta dago ta na fad'in"Baba aure fa ya yi bansani ba."
Dakuwa ya yi mata kafin yace"Kin ga naki, ana rabaki da kiwon awaki kina kokarin gayamin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login