Showing 36001 words to 39000 words out of 116366 words

Chapter 13 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

324

Allah ne ya Halliceki kuma baki fi karfin kema Allah ya Jarabceki ba."
Sai Sajida ta kasa mgana Tunda tasan gaskiya ya fad'a.

Ni kaina na zauna na sunkuyar da kaina ina sauraran Assadiq ina sharan Hawaye acikin zuciyata na cika da alfaharin kasancewarsa Mijinta.
Hannayensa duka ya zura a cikin Aljihun wandonsa kafin ya cigaba da fadin"
Allah da kansa yace Annabi(SAW) man ikira'a suratul ilkasi, Suratul Iklasi salatalmanrat, Duk wanda ya karanta Qulhuwallahu har sau uku kamar ya karanta Qur'ani gabadaya ne.

_Qulhuwallahu Ahad  Allah Ahad guda d'aya ne,  Allahu Samad Allah mai sama lam yalud walam yuulad bai haifa kuma ba'a haifesa ba walam yakun lahu kufuwan Ahad_ shine abun bukata kuma cikin Biyan Bukata._

_Walam yakun lahu kufuwan ahad kuma k bashi da kishiya acikin Bautarsa, Shi Ubangiji shi kada'i ne in kun yarda da shi da imani da duka Sahabbansa da littafansa zaku Fahimci abunda na ke nufi_

Gaban Umma yaje ya duka kafin yace"Umma ki yi hakuri ki yafemin, sannan ki karbi Ziya ki sakama auren mu albarka na yi miki alkwarin zan rike miki sultana da Amana kuma zam zama mai adalci a gare su."
Umma dai kanta na kasa ta kasa mgana.
Sai kawai ya mike Surayya ya kallah kafin yace"Big sis ki tafi da Siya gidan ki don Allah.'
Harara ta makamai kafin tace"Ai da ya ke kai kazo da ita."
Mirmishi ya yi bai yi mgana ba Abba ne ya mike sai da ya yi gyaran murya kafin yace"Ina nan akan matsayata, Ku karbeta da zuciyarku daya d'a na kowa ne sannan cikin mu ba wanda yafi karfin kaddara."

Innani ta kallesa kafin tayi mgana Abba ya Duka gabanta ya na fadin"Ki yi Hakuri Innani ki saka ma magajin gida albarka, da ace ba aure ya yi ba akazo akace miki yana chan ya na lalacewa fa? Ko akawo miki yaro ace d'an gaba da Fatiha ne? Zaki so haka?
Innani sai ta saka kuka ta na fadin"in sha Allahu haka bazai faru b Allah na Tuba ai gwara auren, ni fa daman Gayyar Tsiya ce ban so ammh tunda ya yi mana nasiha ni na saki sai dai Sulsana nake ji kada Ubanta yaji yace Saboda ba yarka bace shiyasa kayi shuru ammh tuni na saduda yar nan ki yafemin"
Ta fad'a ta na jan majina, Abba ya mike ya na fadin"Kada ki damu kowa yaji yasan an yi abunda ya kamata, Abubakar muje a kawo mana abinci bangarena."
Daga haka Abba da Sadiq suka Fice Surayya kuma ta zo ta kama hannuna muka mike ta na ce ma su Saddiqa su riko Umma zuwa bangarenta.
Ni dai ina ta kuka muka fita Surayya na ta bani baki da lafiya komai fa ya wuce Abba ya saka albarka shi da Innani.
Cikin kuka nace"Umma fa?
Sai kawai tace"Itama zata sauko har ta saka musu albarka in sha Allahu"
Saboda tasan halin yan'uwanta sai ta kira Sadiq yazo ya bata makulin Shashensa ta kaini chan tace na yi sallah za'a kawo abinci.
Kuma da kanta tace min na saki jikina ina bangarem mijina ne'
Na shiga Tiolet din bedroom na yo alwala na zo na daidaici gabas na yi sallah.
Bayan na sallame na zauna na mike kafafuwana ina Tunani.
Wayata ma achan gidan Surayya na barta, ajiyar zuciya na ke ta saukewa a kai akai, ta wani bangaren nasamu salama ta wani bangaren kuma ina cikin Tsaka mai wuya.




*Janafty*
*TMWB3K008*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/I7uxPXgtPKBHnVQjaEbRlE

*LAME NIG!*

*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*

Anty Surayya da kanta ta kawo min abinci tare da ruwa da lemu, farar shinkafa da miyar Naman rago.
Kuma ta zauna tare da ni ta na lallashina har sai da naci abincin na sha ruwa ammh ina yi ina zubar hawaye saboda in na tuna kalaman Umma sai naji gabadaya na sare.
Ta gama fahimtar abunda ke sani kuka shiyasa kafin ta fita ta dafa kafad'ata ta na fad'in"Asiya ki daina wannan kukan in ba so kike wannan Masifaffan mijin naki ya zo yaga kina kuka ya taso min ba."
Idanuwana sun tara kwallah na kalleta ina Fad'in"Don Allah ki ba ma Umma hakuri kada ta rabani da Assadiq"
Tausayina ya kama Surayya ta saka Hannunta ta na sharemin hawaye kafin tace"In sha Allahu zan iya bakin kokarina."
Ko da bazata yi ba yadda ta nuna kula da Tausayina yasa na daina kuka sannan na tabbatar mata zan kwanta na Huta kafin mu tashi tafiya kamar yadda ta Bukata.

Ficewa ta yi ta dauke da Farantin abincin da ta kawomin, ni kuma sai na Rarrafa na hau kujera na kwanta sai naji na kasa sakewa sai na tashi ina jan kafa na shiga cikin Bedroom
Na sha kallo komai daman na Assadiq mai kyau ne da Tsari sannan duk da ya jima baya kwana a dakin akwai kamshin Turarensa sannan ga takalmansa nan da wasu kayan.
Gefen gado na samu na d'an kwanta ta gefen cikina na Dama, da gasken kuma na gaji wlh sannnan ga kaina ya fara nauyi, bansan barci ma ya kwasheni ba ina chan ina Tunane Tunane makomar Rayuwar aurena da Assadiq.
Cikin barci naji ni ajikin mutum sannan naji an zare min hijabin jikina, Hancina na kara Budewa ina shakam kamshin Turarensa, ina jin kamshin na ganesa, da Sauri na Bude idanuwa na sai ko fes acikin nasa ya na rankwafo ta kaina ya na kallona cikin Tattausan mirmishinsa.
Cikin muryan barci na kira sunansa"Assadiq."
Shima cikin wani sauti ya amsamin da cewa"Na'am Siya ta."
Kawai sai na yi Ririmi na taso na fad'a jikinsa na Rumgumesa sai kuma na saka masa kuka ina fad'in"Assadiq bazan iya rayuwa babu kai ba, don Allah kada ka rabu dani zan zauna dakai na yi maka biyayya na yi ma yan'uwanka Biyayya sannan ka gayama Umma ni zan yi ma Sultana Biyayya wani abu bazai tab'a had'amu da ita ba, in dai har ni zan zauna dakai na amimce na yi komai Saboda kai Assadiq."
Na karishe fad'a ina gunjin kuka shi kuma sai ya rumgumeni ta baya na. lokaci d'aya kuma ya na bubbuga bayana alamun lallashi.
Bai hanani kukan ba sai da na yi ya isheni sannan ya dago ni ya saka Hannayensa tattausa ya sharemin hawaye Lokaci d'aya ya na fadin"Shii. Nace ki daina wannan kukan ko? Ko so kike wani abu ya samu Bbyn mu?
Sai nayi shuru na koma na lafe a kirjinsa ina jan numfashi.
Rumgumeni ya yi kam lokaci d'aya ya na sauke ajiyar kafin ya fara fad'in"Nace ki kwantar da hankalin ki matukar ina raye ni nan zan tsaya miki siya, ba wacce cikin yan'uwana da zan bari ta tozartamin ke zaki yi musu ladabi a matsayin su na yayyena ammh kuma ni ma bazan bari su wuce iyakarsu ba Mganar Umma kuma kada ki damu zata sauko in sha Allahu."
Sai ya dakata kafin kuma ya gyara zamansa ya na dauke dani akan jikinsa sannan ya cigaba da fad'in"Sultana kuma ba ke ce zaki yi mata Biyayya ba itace zata baki girman ki, ko taki ko ta so ke ce na Fara aura kuma kina gaba da ita so a wajenta ya zama Dole ta girmamaki kamar yadda zata girmamani."
Ina jinsa ammh na kasa mgana a raina ina fadin ai itace ke da kai ni ai yar karo ce.
Fad'i ya ke yi"Zan kare ki da dukkan iyawata wajen ganin kin samu daraja acikin Ahalina fatana kawai ki yi hakuri ki gani, ki ki gani, ki ji kuma ki ki ji, kinsan gida in akwai mata da yawa sai a hankali balle ni kinga kanin mata ne sai a hankali ammh duk da haka zan yi kokarin na zame miki Garkuwa."
Dago kaina na yi ina kallonsa kafin nace"Ka tabbata bazaka rabu da ni ba.?
Na fad'a cikin Rauni, Shi kuma sai ya gyad'amin kai alamun hakane sai kawai na kara Rumgumesa ina fad'in"I love u."
Shima cikin wani irin Shauki ya rikeni sosai lokaci d'aya ya na fadin"Love u too, and i miss u Siyan kuka i need u sosai."
Ina jinsa ya fara shinshinar wuyana Tunda kuma ya Furta nasan abunda ya ke Bukata sai na dago kaina na kama wuyansa na rike, da kaina na Fara Sumbutar bakinsa.
Kamar ya na jira shima ya Rike kaina ya na taikamamin wajen ba ma bakunan mu hakkinsu
Mun shagala shagalar da ta saka muka manta da inda muke, Duk da nauyin cikina ban yarda na Juyama Assadiq baya ba, sai da komai ya wakana ina kwance a gefensa a tare muke maida numfashi.
Tudun cikina ya shafa jin kamar Motsi yana mirmisshi yace"Shi kanshi ya na murna da zuwan Daddynsa."
Mirmishi na yi ban yi mgana ba mun jima tare muna shakan numfashi juna kafin ya tashi shi ya fara shiga wanka ya Tsarkake jikinsa.
Sai da ya fito nima ya taikamanin na yi nawa na fito na maida kayana, ammh shi sai da sauya wasu Tunda wad'ancan sun gama yamutsewa.
Muna tare muna hira har wajen La'asar shine ma ya ke fad'amin zai fad'ama Abba gobe tare dani zasu wuce Zariya gwara na koma zan fi sakewa achan Tunda ga makaranta kada na yi wasa.
Ban yi masa musu ba ni kaina gwara na tafin ko na ba ma wasu zuciyoyin daman samun Salama saboda zuwana.

Kiran sallar la'asar yasa ya barni ya fita shima sai da ya taimakamin na yi alwala ya shimfid'amin Darduma ya zaunar dani yace tunda ya gajiyar dani na yi sallar a zaune sai nace masa kada ya damu zan iya.
Allah ya taimaka ina idar da salla sai ga Anty Surayya ta shigo Cikin Shirin Fita ta na ganina na zaune tace"Au kin ma yi sallar kenan? To taso mu tafi gida sai gobe, tunda Abba yace tare da ke za su wuce."
Ban mata musu ba na mike dakyar ina gyara Hijabina, da muka Fito Haraban gidan sai naga ta Nufi motar ta Cikin sanyi na nace"Bazamu shiga na yi ma Umma sallama ba ne?.
Kai Tsaye tace"Muje gobe in zaku tafi kya shiga ki yi mata."
Ban yi musu ba ta bude min gidan gaba na zauna sai dai ina ta waigen ganin Assadiq.
Itace ta Lura da haka kai Tsaye tace min"Sadiq ya na bangaren Abba suna mgana, kina son ganinsa ne?
Da sauri na girgiza mata kai ina kokarin kauda kaina Saboda kunya.
Mirmishi ta yi kafin tace"Zai zo anjuma ina da tabbacin haka Tunda Siya na tare dani ta bakinsa"
Tare muka yi dariya ni da ita , sai dai kuma Tundaganan har muka isa gida bata kara mgana ba.
Abunda na Lura kamar ranta ya na bace ne shiyasa yara ma na mata Oyoyo mommy bata tsaya ta kansu ba, Tunda ta rakani daki tace na kwanta na kara Hutawa ta fice ta koma Dakinta.

Ran surayya ya gama baci da sauran yan'uwanta marasa fahimta musamman Sadiya da Sajida da Subai, Saddiqa ce bata zafafa ba har Sa'adatu ta bata mamaki yadda taga ta Dauki zafin kan al'amarin..
Kuma illar shine daukan zafin su To kara Harzukan Umma suke ta so ne su taru su ba ma Umma baki ta karbi wannan kaddaran ammh su sun ki gane haka sai kara Zuga Umma su ke yi suna fad'in kada ta yarda Sadiq sai ya zab'a ko Sultana ko Mayyar matarsa.
Kuma abun haushin harda karamar yarinya suka zauna suna ta zugata, ita sai ta koma kawai ta yi shuru Saboda sun ce ta na Goyon bayan Sadiq ne.
Shiyasa da ta bi Umma har Daki zata ba ta shawara da mgana.
Ta koreta tace ta fita ta bata waje har ta na cewa Daman tasan bakinsu d'aya da Sadiq abunda ya sa har ta yi kwallah shine sauran yan'uwan nata har suna zargin daman tasan Sadiq ya yi auren Tuntuni taki fad'a.
Shine ya sakata kuka ta na Rantsuwa ta na bata san komai ba Saddiqa na tayata gayamusu in da taga Hoton Sadiq da matarsa.
Kuma har Umma ta aminta da mganarsu Shiyasa ta zo ta ja Hasiya suka yi tafiyarsu.
Kuma ita abunda yasa tace abi komai a sannu shine ta riga ta gama Fahimtar Matukar aka matsa to Sadiq zai zabi Hasiya ne ya bar Sultana domin alamominsa sun nuna haka, kuma wlh zai yi iya fad'a da kowa akan Hasiya to in suka zo suna zuga Sultana taje ta yi masa rashin kunya fa? Yadda Sadiq ya tsani Reni ai sai a samu matsala Shiyasa ta so abi komai a sannu a Hankali kowa sai ya samu abunda ya ke so.

Ni bata gayamin ba ammh rashin walwalwarta ya bayyana har saman Fuskarta, tunda muka dawo ba ta da walwala ta ma shige ciki ba ta fito ba.
Nima kuma ina inda na sauka na iske kiran waya Rututu har da na Amma ga na Ramatu sai na Adda Fati.
Adda Fati kawai na kira, nasan itama ta na cikin Fargaban kawai sai nace mata ta bari na dawo gobe in sha Allahu.
Amma na kira gabana na fad'i na Dauka ko sun yi wata mganar ne da Adda sai naji kawsi mun gaisa ta na tambayan lafiya da kuma lafiyar Assadiq nace mata dukkan mu muna cikin koshin lafiya.
Shine ma ta ke fad'amin Adda bata ji dadi ba hawan jini ya taso mata kwanaki biyu kenan, sai nace ta bani ita na gaisheta.
Adda da karfin hali ta tambayeni Cikina watansa nawa? Nace bakwai da wani abu sai tace In Hamma Isuhu zai Shigo Zariya zata bashi wasu saiwowin itattace na Dafa na rika sha mganin zaki ne, ni dai sai na bita da Toh kawai.
Bayan Amma Ramatu na kira muka gaisa itama mun kwana Bamu yi waya ba tambayata tayi ina gida gobe sai nace mata a'a sai dai jibi, nan take gayamin Jibi zata shigo da haka muka yi sallama.
Da daddare Khalil ya kawo min abinci Tuwon Semo miyar Kubewa d'anya, kuma naji dadi Sosai naci da yawa Sannan ga Zobo mai sanyi ga dad'i.

Bayan na gama ci ne na yi sallar Isha'i daman kuma sai da na yi mangariba na ci abinci bayan na idar da salla ina zaune naji tashin murya kamar ta Assadiq a falo kuma chan sai naji kamar harda muryan mijin Anty Surayya.
Ban ko kai da tashi daga inda na ke ba sai gashi ya shigo.
Ina ganinsa na sakar masa mirmishin jin dadin ganinsa.
Shima sai ya maidamin martanin mirmishi kusa dani ya zauna Lokaci Daya ya na kallon kwanukan gabana kafin yace"Lalle kin zama yar gata a wajen Big sis."
Mirmishi na yi kafin nace"Ai ta na da Kirki ne."
Kai Tsaye yace"Shiyasa na fi sonta duk cikin su, ita da mijinta suna da kirki yanzu ma afalo da ita nake yi, Matar nan fa wai batamin magana yanzu Saboda taga agaban mijinta ne har da kukanta wai naja mata zargi a wajen Umma da Sauran yan'uwana."
Ido na zaro kafin nace"Zargin me kuma?
Yana Mirmishi yace"Zargin suna Tunanin Ta san nayi aure ammh ta Boye musu."
Jinjina kai na yi kafin nayi magana ya Rigani da fad'in"Sun ce hakane Saboda susan ba abunda na ke Boye mata  abunda ba su sani ba itama yadda suka ji haka itama taji sa.'
Kai na lamgwabar kafin nace"Ai kai ne baka kyauta ba"
Mirmishi ya yi kafin yace"Nasan ban kyauta ai na karb'i Laifina ko?
To ba sai a Tsaya a saurareni ba."
Ni dai ban ce komai ba, sai naji ya Rungumoni ta gefen kafad'ansa Lokaci d'aya ya na fadin"Matar Sadiq ya nauyin jiki kuma?
Dariya na yi ina dukan kirjinsa nace"Nauyin jiki ko Nauyin ka?
Gira ya dagamin kafin yace"Duka na ke mgana."
Dariya muka saka gabadaya ni da shi, ina gefen kafad'ansa ya dafani kamar wata kawarsa ya na min Hira shiyasa na ke son Assadiq saboda Halinsa na kwarai da sanin yakamata.
Acikin Hirar ne ya ke gayamin Abba yace da wuri zamu dauki hanya.
Ina kallonsa nace"abokin naka fa, ka kirasa ne ?.
Kai tsaye yace"Tahir ai ba shi da kirki gaba ya ke yi dani, na yi ta kiransa bai Dauki wayata ba sai na Tura masa sako in yagani shikenan in bai gani ba Shiya sani."
A marairaice nace"Duk Saboda ni ne ko? Ni dai don Allah kada ka bata da abokinka saboda ni."
Da Sauri yace"No kada ma ki saka wannan Tunanin a ranki, ni da Tahir mun saba kada ma ki yi wannan Tunanin."
Ya fad'a daidai Lokacin da wayarsa dake gaban Aljihunsa ta fara Daukan Tsuwwa.
Ni na saka Hannu na Dauko masa wayar na mika masa, ya na Dubawa sai yaga Tahir ne.
Ni ya kallah cikin mirmishi kafin yace"Kinga Mutumin ki ko?
Tahir ne"
Yana fad'a ya na daga wayar kamar Tahir na jira yace a kufuluce"Mallam wani irin sako naga ka Turomin?
Sadiq na jin haka sai ya saka wayar a Speaker ya na Danne Dariyansa.

Shima cikin kai Tsaye yace"Ka karanta mana, ai da Hausa na yi maka Sakon."
Shuru Tahir ya yi kafin yace"Naga wai kace Abba na nemana zamu je Zariya, Mallam baka ji abunda na fada maka Tun Farko ba ne? Ni ba ni cikin wannan Rigimar taka, tunda tun Farko kasan bazan barka ka aikata haka ba shiyasa ka Boyemin Saboda haka Count me out acikin Rigimar ka na gayamaka."
Da Sauri Sadiq yace"Haka zan gayama Abban?
Tahir yace"Bangane ba"
Sadiq na danne dariyansa yace"Abba ne yace na kira ka na fad'a maka zamu je Zariya gidan Baffan Siya."
Tahir yace"Saboda mene? Meyasa sai da ni kuma?
Kai Tsaye Sadiq yace"Saboda kai ne waliyina."
Tahir ya yi shuru bai yi mgana ba, Sadiq yace"Me zan gayamasa? Bazaka je ba?
Tahir yace'"Ban ce ba, d'an sharri sai dai mu Had'u a zariya tunda baka gayamin da wuri ba."
Sadiq yace"Better.."
Daga haka suka yanke kiran ya kalleni ya na fadin"Kin jisa ko? Tahir ai dan renin sense ne."
Mirmishi na yi sai dai ban yi mgana ba, hira ya cigaba da min yana bani Labarin Diramansu da Tahir ina ta Dariya.
Bamu san lokaci ya ja haka ba sai da Mukaji muryan Surayya daga sama kanmu, cikin cogewa a bakin kofar dakin tace"Mallam kazo ka tafi zamu Rufe gidanmu ne".
Ta fad'a lokaci d'aya ta na hararansa, dukkanmu muka kallesa ni kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login