Showing 3001 words to 6000 words out of 116366 words

Chapter 2 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

304

karamin gado na marasa lafiya.
An dibi jinina sannan Wata Nurse ta rakani Tiolet na yi fitsari a wani Roba sannan na dawo na kwanta Safiya da wannan yar'uwanta na ta ke ta Shiga ta fita a kaina har sai da aka sakamin Drip, abu d'aya ke damuna miyan bakina da baya yankewa, sai da Safiya ta sama min leda ina tofawa aciki, ko fa Barci na ke yi in miyan nan ya Taru sai na tashi na zubar da shi na ke samun sukuni.
To yau din ma haka ya faru barci ya kwasheni ammh bi ni bi ni Miyan bakina ke tadani, kwata kwata na kasa gane kaina, zuwa yammah sai na samu karfin jikina sosai har Safiya ta fita bakin asibiti ta siyomin kayan marmarci naci, kuma tace ta Duba wayata ba Chaji balle ta gayama yan'uwana.
Ni kuma sai nace ta kyalesu kawai tunda naji sauki, sai da ruwan ya kare na koma gaban likita, daman kananan Roba biyu aka sakamin sai babba guda daya.
Abunda Likita ya fad'amin ya sandar dani, ya na mikamin Result din da suka gani acikin jinina da fitsarina, ammh na kasa karb'a saboda Tashin Hankali da mamaki.

"Ciki gareni ni Hasiya, haka likita ke fad'amin har na Tsawon wattani biyu da kwanaki."

Sannan ya Cigaba da bani shawarwarin cin abinci ko da zan yi amai sannan da samun cikakken Hutu da natsuwa, sai kuma yace ina da maleria a jikina sai na kiyaye, ya Rubutamin maganin karin jini na samu ciki sai paracetomol sai mganin Maleria.
Na fito rike da Takarda a hannuna ina tafe miyau ya cika bakina, har mganar Miyan na yi masa yace na yi hakuri zan bari zuwa wani Lokaci, ammh yanzu na rika cin cingam ko shan minti.
Safiya na ganin na fito ta zo ta rikeni muka samu waje muka zauna.
Ta karbi takardun hannuna ta na fadin"Me likitan yace?
Kai Tsaye nace"Ciki gareni Safiya."
Sai ta washe baki ta na fad'in"Daman Sister Zainab ta fad'a tace ta na Tunanin ciki ne, kai Congratulation kawata na yi miki murna soon to be come a mother."

Ta fad'a ta na dafa kafad'ata cikin murna sai kawai na bi ta da kallo ammh na kasa mgana sai dai na yi mata ya ke, takardan mganin ta Duba ni kuma sai na kalleta ina fad'in"Magunguna ne ya Rubutamin akwai sauran kudi a jakar ko?
Sai tace"Akwai kudi ammh ba su da yawa 5k na gani kuma kinga an siya kati an biya kudin ganin likita sannan an Rubuta ruwa da alluran da aka yi miki."
Ina Rausayar da kai nace"Akwai kudi a cikin bankina, ki yi amfani da Atm dina."
Sai ta amsamin da Toh, kafin tace bari taje ta dawo.
Nan ta barni ina zaune ina Tunanin, makomata, shin makomar Tafiya ko kuma makomar zama ne?
Ina shafa cikina ina hawaye to in na tafi ina zan kai wannan gudan jinin da ke cikina?
Ashe akwai rabo mai karfi a tsakanina da Assadiq, Shiyasa har aka gano wannan Implant din ajikina aka Ciremin shi Saboda wannan Rabon da zai Shiga Tsakanina da Assadiq.
Lalle na kara Shiga cikin Tsaka mai wuya, ni dai bazan zubar da cikin jikina ba sanman bani da tabbacin Uban cikin zai karbesa Tunda tun asali baya so ya had'a zuru'a dani.
Hango su Safiyq na yi da yar'uwanta yasa na yi goge hawayena har suka kariso.

Congrarulation Sister dinta ta fara yi min, na amsa ina ya k'e, Safiya ta nuna min magungunar da ta siyo min ita kuma yar'uwata ta zauna gefena ta na bani shawarwarin yadda zan kula da kaina ina gyad'a mata kai.
Sai shidda Saura muka bar asibitin muka koma gida, Safiya tamin kokari Daman ta jini shuru ne ban je makaranta kuma bata samu na a waya Shiyasa ta zo, ba ta tafi ba sai da tambayeni abunda zan ci nace ta dafamin shinkafa da mai da yaji ita na ke sha'awa.
Sannan ta sakamin Ruwa na yi wanka naji karfin jikina, ta na nan maman Sulaihat ta shigo, ta na ganin ina tofar da Miyau a leda ta fara fad'in Allah ya inganta tun ballatana da taga Safiya na dariya sai ta san abunda ta ke zargi ne, gashi kuma rame na yi wani irin Fari fayau da ni.
Safiya sai da tayi mangariba ta tafi, tace zata rika sakamin Attendence in kuma za'a yi test zatamin kafin naji sauki na dawo makaranta.
A haka muka rabu bayan na yi mata godiya sosai.

In da Allah ya taimakeni Maman Suhailat ke kula dani, zata shigo da Safe da rana sannan da yammah , tace me zan ci? Komai kuma nace ina so zataje dakinta ta dafamin, in ba ita ba yarta ta dafamin, ita kan zo ma tamin Share share ko ta sakamin ruwan wanka, Ummi dai ta shigo ta gaisheni ita da matar da ke dakin Fadila yanzu.
Ina cin abinci ammh ba sosai ba, Sai dai abinci na daga Tuwo sai Fate , sai kuma Shasshaka na ke iya ci sai kuma Kunin tsamiya.
Sai kuma kunzo saboda Miyan da na ke yi, ba domin maman suhailat ba da na zama kazama.
Wayata kuma tundaga ranar ban kara kunnawa ba, ta mutu ma ba chaji Adda Fati ma ta ji ni shuru kuma wayata a kashe yasa ta aiko Habiba ta Dubani sai ta iskeni kwance ina Fama da Farin baki da miyau.
Ta koma ta gayama Adda Fati sai gata tazo, ni da bakina ban fad'a mata ina da ciki ba ita ce ta gane, kuma itace ta gayama Ramatu da Adda Rukayya.
Amma kanta Adda Fati ta kira ta ta na Fad'a mata ina ta fama da Laulayi.
Ta kirani ta gaisheni har da hawayenta na Farinciki nima yau zan zama uwa, Ramatu da Adda Rukayya duk sun zo dubani.
Abakin su naji na koma kamar Zabiya saboda hasken da na kara sannan dagani cikin nan zai sakani rama Sosai.
Suna ta dai zencen su, Saboda ganin ba na iya komai yasa Adda Fati ta ce Habiba ta zauna da ni har sai na ji sauki na kama jikina, nace mata da ta bar shi Maman sulaihat ma na kula dani, sai tace sai a barta da Wahala? Har daki Adda Fati ta shiga ta yi mata godiya tace bakomai kamar y'a ta Daukeni.
Wasa wasa sai da na kwashe kwana goma sha ina kwance sannan naji sauki na mike, sai dai ban daina kwana da zazzabi ba, sannan ga Miyau ni shi yafi damuna ba, haka zaka shiga cikin Jama'a ka na fama da Miyau?
Sannan Tun naga nafi Sati Biyu Assadiq bai biyo bayana ba na kara Tabbatar da ma da kaina zama bai ganni ba.
Duk a tunaninsu Adda Fati Assadiq ya zo ya dubani ya koma ne, ganin bani da matsalan komai yasa ba su kawo ma wani Tunani ba.
Sati daya Habiba tamin nace ta koma gida naji sauki, ranar da na cika Sati biyu Ranar lahadi, daman a ranar na gama kudurin Tafiya wajen Amma Tunda naji sauki.
Zama na ba shi da amfani , bazan taba Damuwa don Assadiq bai karbi Cikin jikina ba, ni dai ina son kaya na kuma zan renesa na haifesa ko da shi d'in baya bukatar haka.
To ta ina zai bukaci haka Tunda ba Sultana bace? Ni fa daman taimako na ya yi, baya so na ban dace da Rayuwarsa ba shiyasa ba zai zo ya had'a wani abu da ni ba.
Safiya ta dawo wajen sau biyu ta Dubani, ta yi ta min fad'an na kunna wayata sai na yi mata karyan inaga ta lalace tunda na yi ta kunnawa taki kawowa.
Misalin karfe sha daya da wani na Safe ne, na yi wanka na shirya cikin Doguwar rigar abaya baka sai na saka Hijabi saboda na rame.
Na adana komai Saboda bansan yadda Tafiyar tawa zata kasance ba, ammh ina ji a jikina ba ta dawowa bace.
Na janyo akwatina babba da karamar sai karamar jakata da na saka Muhimman abubuwana, na yanke shawaran zan ce ma Maman suhailat cewa zan je wajen mafiyata Saboda Mijina sun tafi wani aiki kuma zai Dade bai dawo ba saboda gudun zargi.
Da wannan shawaran na saka Takalmi na janyo akwatina kii sai kofar Daki na saka hannu na bude da makulli sannan na Cire makullin a Hannuna.
Ina Bude kofar, ya na karisowa wajen kamar ko daman ya na wajen ne ni dai ban sani ba.
Na dai gansa kaawai a gabana, ya na kallona nima ina kallonsa cikin mamakin ganinsa.

ASSADIQ ne sanye da kananun kaya Riga da wando fari da baki sai jaket da jakar baya, duka Hannayensa na cikin Aljihun wandonsa.
Yadda na ke kare masa kallo shima haka ya ke karemin kallo.
Cikin mamakin ramar da na yi masa har a ido, ni kuma naga ya yi kiba sannan ya kara haske.
Sai naji Duhu ya mamaye ganina na kishin Tuna amarci fa ya ke yi ai Dole naga ya sauya.
Kawai sai na juya masa baya ina kokuwa da Numfashina.
Mirmishin saman baki ya yi sannan ya taka ya shiga dakin ya na fadin"Tsanar da kika min siya har ta kai ki juya baya daga kallon Fuskata?
Sai kuma ya bi akwatin gefena da kallo.
Kafin ya yi mgana na koma falo Fuu, sai ya bi ni da kallo kafin ya Rufe kofar ya Tura akwatin ya taddani a falo a zaune a kasa na saka kaina a gwiwa.
Da Sauri ya ijiye akwatina tsakar falo ya karisa gareni jikinsa na rawa ya ke fadin"Siya na san ni me laifi ne ammh don girman Allah ki tsaya ki Saurareni."

A fusace na Dago ina kallonsa kafin nace"Na saurareka? Ashe akwai sauran abunda zaka gayamin wanda ban ji ba, ko kuma nace ban gani da idanuwana ba?
Umh! Abubakar kenan"
Na fad'a hawaye na kawo idanuwana, da Sauri ya saka Hannu zai rikeni na Zabura naja baya ina fadin"Kada ka kuskura ka tab'ani Tunda BAKA SO NA ASSADIQ."
Ido ya zaro kafin yace"waye ya fad'a miki ba na son ki SIYA?
Cikin Idanuwansa nace"Kai ne."
Cikin karin mamaki yace"Ni kuma? Look Siya boye miki Asalina ya na da Nasaba da Sonki da na ke yi, ina sonki ba na son na Rabu da ke shiyasa ban taba fad'a miki komai game dani ba."

Kallonsa na ke yi ina tsiyayan hawaye kafin na kira sunansa"Assadiq."
Sai kawai yace da Sauri"Ki tsaya ki Fahimceni Siya, mu zauna mu yi mgana don Allah, ammh kafin nan wannan akaatin nan na miye ne? Ina kike shirin tafiya?
Kai Tsaye nace"Wajen mahaifiyata."
Sai ya koma ya zauna Dabas kafin yace"Why Siya? Sai ki iya tafiya yanzu ki bar ni?
Mirmishin takaici na yi kafin na jawo karamar jakata, na bude na Dauko masa takardan shaidar cikina na mika masa.
Sai ya ki karba'a ya na kallona Sai ya kira sunana "HASIYA.."
Da Sauri nace"Sakon ka ne aciki ka Duba."
Ba musu ya karb'a ya Bude ya Fara Dubawa, ina kure masa ido naga ya Dago a razane ya na kallona.
Cikin mirmishi nace"Ka yi mamakin ko? Ka yi mamakin ya aka yi na samu ciki Ahalin ka kaini an datsemin Hanyar samin cikin ko Assadiq?
Ina ganin Razana da Firgici a idanuwan Assadiq.
Ya na kallona ina Hango kunya nadama da Tsananin tsoro da wani abu a akwayar idanuwansa.
Cikin Sauri na mike ina fad'in"Zaka iya sakina Assadiq ammh sai dai ka sani ko Sama da kasa zata had'e bazan amince na zubar da wannan cikin ba."
Na fad'a ina kokarin Danne kukana ammh sai da ya kwacemin.
Cikim kuka na cigaba da fadin"Na yarda baka sona, ammh ni ina sonka Assadiq don Allah ka barni da cikin nan na yi maka alkwarin zan yi nesa da Duniyarka har abada ba wanda zai san ka na da wani gudun jini bayan Ya'yan da Sultana zata haifa maka."
Ban karishe mganata ba naji ni gabadaya acikin jikinsa.
Ya yi min wani karkarfan Riko cikin wani irin Sauti yace"Tare zamu rene gudan jinin mu siya, zai kuma zo Duniya ya iske gatan Iyayensa Biyu tare da gatan duka Ahalim mu Siya."
Cikin mamaki na Dago fuskata da tayi jage jage da majina ina kallonsa
Cikin mamaki na kira sunanshi.

"Assadiq"

Kai ya gyad'amin kafin yace" Ina sonki HASIYA, ki yarda ko karki Yarda, ina sonki sannan kuma na yarda da kuskurena na kuma karbi laifina zan kuma gyara, ta hanyar gayama Ahalina da Duniya cewa ke MATATA CE.! Kuma cikin da ke jikin na wa ne"
Ya fad'a ya na shafa kasan marata, sai naji kamar zan suma saboda dad'i
Cikin kuka nace"Ko da kuwa hakan zai jefa rayuwarka cikin Tsaka mai wuya?
Da sauri yace"Eh na amince da hakan matukar zan cigaba da kasancewa tare da ke na shirya karban komai Siya."
Bansan lokacin da na kara Rumgumesa ba ina dariya ina kuka nace"Nagode Assadiq. nagode."
Kwata kwata naji jin haushinsa ya fita daga raina daman Fargaba na d'aya shine yace zai sakeni ko zai rabani da Cikin jikina.
Sannan maganar Boyemin Asalinsa da ya yi bai dameni ba, ta wanni Fanni ya yi hakane domin amfanin kaina da na shi gabadaya.
Ni ban damu da ya so ni ba, ni dai ina son shi kuma ina fatan na zauna da shi har karshen rayuwata.






*Janafty*
*TMWBK302*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/I7uxPXgtPKBHnVQjaEbRlE

Mun dad'e tsaye Rumgume da juna kafin ya sake ni, sannan ya bi fuskata tare da bakina da sumbata mai yawa.
Sannan ya ja hannuna muka zauna saman daya daga cikin kujerun falon.
Ya Rumgumoni ta rabin jikinsa na Dama, lokaci daya hannunsa na shafa kasan marata cikin sannu a Hankali kamar ya na shafa kwai.
Ni kuma na lafe a jikinsa ina sauke Numfashi ji na ke yi kamar dukkan wasu matsalolina na nan duniya sun kauce, kamar ni kad'ai ce Sarauniya da ta yi saura a duniya.
Idanuwana suna lumshe naji Assadiq ya fara mgana cikin Taushin murya da fari da kiran sunana ya fara

"HASIYA."

Na amsa cikin Dakushewar murya da alamun sanyi a cikinta, miyau kuma ya fara taruwa a bakina na kira sunansa nima bayan na amsa kiransa.
"Na'am Assadiq din Hasiya"
Mirmishi ya yi domin har sai da kunnuwana suka jiyomin Sautin mirmishin nasa da ya shiga har cikin zuciyata.
Cikin kwantar da kansa saman kaina ya fara fad'in"Zan fada miki ko ni waye, sannan zan amsa duka tambayoyinki game dani, nasan zaki ce me ya rage baki sani ba? To har yanzu akwai muhimman abubuwan da ya kamata ki sani game da Rayuwata Siya, ammh kafin nan sai kin fad'amin meyasa a wanchan Ranar a gusau kika taho zariya cikin Daran nan Siya? Sannan me yasa kika ki Daukan Wayata? Daga karshe sai naji ta a kashe, Siya kinsan iya adadin Tashin hankalin da na shiga bayan tafuyarki kuwa? Kinsan adadin irin Bugun zuciyar da na rika fama da shi in na Tuna a yanayin da kika taho zariya da daddare sannan ga hanyarmu sai a hankali?
Me yasa kika yi haka?

Ajiyar rai na sauke, kafin na Dago kaina miyau ya cika bakina shiyasa na tashi da sauri sai ya rikoni ya na fad'in"Ina kuma zaki muna mgana?
Bakina na nuna masa da ya cika da Miyau sai ya yi saurin sakina ya na fad'in"Sorry."
Kai na gyad'a masa, sannan na wuce zuwa cikin daki na shiga makewayi na zubar da miyan bakina sannan na wanke bakin, ban fito ba sai da na samu wata bakar leda na taho da ita, gudun kada maganar ta Gundiremu da yawan tashi na.
Sanda na dawo gefensa na sake zama kamar dazu sai ya kara rumgumoni,Ya dora kansa saman kaina da ke gefen wuyansa, ni kuma sai na nuna masa ledan hannuna ina Fad'in"Ka yi hakuri, na zama kazama yanzu ban iya hadiyan miyau."
Mirmishi ya yi kafin yace"Mun zama kazamai zaki ce, ni ma in naji miyan sai na Tofa abuna aciki ko?
Ya fad'a ya na leken fuskata sai na kyalkyace da dariya shima ya na tayani.
Sai da muka natsu sannan ya kalleni ya na fad'in"Umh baki bani amsar tambayoyina ba?
Shuru na yi kafin nace"Tsoro na ke ji, ba na so na zauna wata acikin yan'uwanka su Fahimci alakarmu da kai wani abu mara dadi yazo ya faru shiyasa na tafi."
Na kasa fad'a masa karona da abokinsa saboda bansan ya zai Dauki mganar ba.
Kai Tsaye yace"Me yasa kika tafi? Ba wajen Saliha kika zo ba? Ba wanda zai fahimci wani abu tunda ki na da alaqa da Mijin da Salima ta aura."
Cikin mamaki na kallesa shima ni ya ke kallo kafin ya yi mirmishi yace"Kin yi mamakin ya a ka yi duk na san wannan ko? Sai bayan tafiyarki a ranar nasan haka nima."

Nan ya fara bani Labarin abunda ya faru bayan tafiyata, ashe yan'uwansa sun hanashi sakewa su dai sai an yi Hotuna, in kuma ya nuna wani abu za su iya gane akwai wani abu a kasa.
Ya na fad'in sai bayan mangriba suka sake shi daga Daukan Hotunan nan shima din ya Tuburene yace zai je ya yi sallah.
Ya na gayamin hankalinsa tashe ya rika nema na acikin gidan nan bai ganni ba, sannan ga shi ya na kiran wayata ba na dauka, yace har Tahir ya tambaya tunda ya sanni, ammh yace bai ga fita ta ba, ban yi mamaki ba Tunda nasan abokinsa ba ya son alakarmu ba abun mamaki ba ne in bai gayamasa mganganun da ya fad'amin ba.
Yana cikin nema ne, yaji Saliha na cigiyar kawarta da ta zo mata biki daga Zariya, sunanta kuma Hasiya, daganan sai ya sha jinin jikinsa, ya tabbatar ne lokacin da yace in Saliha na da Hotona ta nuna masa sai ko ta nuna masa ya ganni, itace ma ta ke fad'a masa cewa ni yar uwar mijin Salima ce daga zariya.
Ya na gayamin Hankalinsa bai kwanta  ba, sai da yaji Saliha na fad'in na yi mata Sako nace mijina ne yace na Dawo gida, Tun kafin ma nayi masa tambayar da ke cin raina naji ya na amsamin.

Assadiq ya kalleni cikin sanyin murya ya na fad'in"Nasan zaki ce meyasa bayan haka ban biyo bayan ki ba? Siya bani da mafita illah zabin na zauna a gusai tare da Sultana da ta tare a gidan da Abba yaa bani tun a daran, in na yi wani motsi abubuwa za su kwabe ni kuma bazan so haka ba, Shiyasa na zauna har na Tsawon Hutun da na Dauka na Sati daya daga wajen aiki, ammh na rantse da Allah ki sani ko wata dakika ba ta wuceni sai na Tuna ki Siya, wayarki ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login