Showing 102001 words to 105000 words out of 116366 words

Chapter 35 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

319

ba."
Kafin ya yi mgana na rigasa da sauri nace"Laa ga daki nan, har na kai kayan ku ciki ma."
Na fad'a ina nuna mata dakin da Hannuna ko kallona bata yi ba ta mike Dauke da ummi Lokaci d'aya ta na fadin"ta shi mu je Naja."
Muna tsaye ta wuce cikin dakin Naja na bin bayanta.
Shi dai kai kawai ya girgiza kafin ya wuce yana fad'in"Sai na dawo."
Na rakasa har kofar falo sannan na dawo cikin falo.
Na zauna na yi tagumi ina Tunanin yadda zaman mu zai kaya da sultana daga gani kuma ta zo ta jima ne, kuma Yadda ta ke nunawa har yanzu ba ta son zaman lafiya.

Tunda Assadiq ya fita ina falo nan, saboda kula da su Asif, kada na tafi daki su yi min barna.
Ammh su Dultana ba su fito ba ni dai ina ta jiransu saboda na basu abinci.
Sai da naga har La'asar ta yi na tashi na koma daki na yi salla.
Bayan na idar salla ne na kara Fitowa falo na iske su Asif na ta guje guje da Motocinsu har kuma Lokacin ban ji motsin Sultana ba.
Sai na koma kitchen daman Shinkafar na cikin kula da miyar farantai na had'a da Cokula a faranti na had'a na dauka sai dakin da na sauki Sultana.
Kofar ta na Rufe ne sai da na kwankwasa sannan Naja tazo ta Budemin ban shiga na mika mata Farantin hannuna ina fad'in"Ki zo ki daukar muku ruwa."
Tace toh ta shiga ta ijiye ta fito Falo ta Dauki Farantin Ruwa da lemun da na zuba musu tun dazu.
Kitchen na koma ina Tunanin abunda zamu ci da Daddare, Sai na yi tunanin na yi mana Tuwon shinkafa Miyar agushi da Nama.
Nan da nan na zage na fara aiki Daman Saboda wayar zamanin nan na Koyi girke girke da snkas masu dama a kafafen sada zumunta da suka kara taimakamin sosai.

Sai zuwa can Naji buruntu a falo da na leka sai naga Naja ce goye da Ummi ta duka ta na ta taya su Asif wasa da Motoci ganinta yasa sai naji dadi nasan zata kula da su.
Ina cikin yin girkin ne wayata a falo ta dauki kara ana ta kira ban ji ba.
Sai da Naja ta kawomin tace ana ta kirana, ina Dubawa sai naga Umma ce ta kirani har sau hudu.
Da sauri na wanke hannuna na bi bayan kiranta.
Bayan ta dauka mun gaisa ta tambayi su Asim kai tsaye nace"Umma su nan zuwa a karshen wata nan, yaye zan yi musu sun kusa shekara biyu."
Umma tace"Ma sha Allah, sai sun zo muna nan muna jiransu, ammh ki gayamusu kada su zo hannu Rabba na."
Ina ta dariya Umma na tayani sai can ta kira sunana na amsa cikin Sanyin murya tace"Ashe kuma yau kun yi bakuwa ko?
Kai Tsaye nace"Eh Umma suna nan tun dazu."
Umma ta yi shuru kafin tace"To ki yi hakuri Hasiya, nasan halin sultana da Rigimar tsiya da sakarci duk abunda zata yi kada ki Biye mata, ni ban ma san tafiyarta ba yar hatsaniya suka yi da Sajida yasa ta yi fushi da kowa ta taho nan Wajen ku."
Cikin mamaki nace"Subhanallah! Allah ya kyauta kada ki damu Umma lafiya lau zamu zauna har tagama kwanakinta ta dawo in sha Allahu."
Umma ta yi ta sakamin albarka kafin mu yi sallama..
Na cigaba da aikina ammh a gefen raina ina mamakin wai sultana da Anty Sajida suka yi yar hatsiniya? Lalle abun da ya baka mamaki watarana shi zai baka tsoro.
Ina da ganyen Allayahu da ganyen Ogun saboda Assadiq na san Abinci da ganye yana yawan siyomin ni kuma sai na saka masa ruwa na saka a leda na Masa masauki acikin Firiza.
Ni kad'ai na yi aikina kamar yadda na Saba Sultana ko ganinta ban sake yi ba.
Ammh naji muryanta a falo kamar ta na yi ma Naja mgana ne, sanda kuma na Fito ban ganta ba sai Najan tare da su Asif.
Ba goyon Ummin kila uwarta ta karbe'ta ne, Sai da na yi sallar mangariba na zo na kulla Tuwon a ledan Naja kuma nace su bar wasan su yi sallah sai na kunna musu Cartoon nace su kallah na kwashe kayan wasan na kai su dayan dakin da ke kusa da inda Sultana ta sauka.
Assadiq ya dawo ina wanka naji shigowarsa Bedroom dina sanda na Fito baya d'akin.

Lokacin da Tada sallar Isha'i ne ya sake shigowa shima ya Shiga wanka.
Na idar kenan sai gashi ya fito ina zaune saman darduma na yi masa sannu da zuwa ya amsa ya na kallo na kafin yace"Ya aikin? Ya baki kuma?
Kai tsaye nace"Alhamdulillah.'
Gayamin ya ke yi yaga su Asim sun samu abokiyar wasa naja, nace masa sai da na kwashe kayan wasan ai.
Shima yau a gida ya yi sallar isha'i ni kuma na fita falo na had'a mana Abinci saman Cafet Tunda Assadiq ya fi son cin Tuwo a kasa fiye da a zaman kujerun zamani.
Naja nace ta je ta kira sultana, yau ko su Asif ban samu yi ma wankan yammah ba kila sai munzo kwanciya, ni kuma na koma daki na taya Assadiq shiryawa cikin Saukakkun kaya na shan iska.
Muka fito tare na iske Hakima Sultana ta shab'a uban ado, Ta zauna saman kujera kafa d'aya kan d'aya.
Har ta zuba tuwonta ta cika Uban miya da Nama ta fara ci.
Naja da su Asim na gefe suna kallon Cartoon.
Mamakinta ya kamani sai dai ban yi mgana ba, Assadiq ne da ya zauna ya kalleta yana fad'in"Sultana shine baki jira mun zo an ci gabadaya ba."
Ba ta ko kallesa ba tace"Ni da gidan mijina ba sai na jira wata sannan zan ci abinci ba."
Ya kalleta cikin mamaki zai yi mgana na kateshi da kiran Naja da su Asim
Su daman nasan ba su cika damuwa da abinci ba Tea suke sha ko kuma su sha Goldenmorn.
Ammh na tattarosu na saka musu a filet d'aya har da Naja nace ta luramin da su kads su bata jikinsu da wajen.
Sai tace min zata rika basu ma a baki.
Abunda ya Hana Assadiq mgana kenan ya yi shuru kawai ya koma ya na kallon sultana Lokaci daya da mamakinta.
Shi na fara zubamawa sannan na zuba ma kaina, tare muka fara cin abinci shine kamar ya tuna da wani abu ya kalli Sultana ya na fadin"Ina kika baro Ummi?
Kai tsaye tace"Tana ciki ta yi barci."
Cikin sauri yace"Ita kadai kika bari a daki?
Ta tabe baki kafin tace"To me zai cinyeta?
Saboda sanin halinta na rashin kunya yasa bai yi mata mgana ba.
Muka cigaba da cin abinci, muna cikin ci ne aka kirasa a waya bansan waye ba naga ya bar cin abincin ya mike ya koma daki sai da ya jima sannan ya fito.
Sai ya iskeni sai ni kaad'ai sai yara a falo Sultana ta gama ci ta tashi ta barmin filet da komai ta koma daki.
Ina durkushe ina ta tattara kwanukan Naja na tayani Asif har ya yi barci Asim na kasa a kwance shima barcin zai yi.
Kai tsaye yace"Ina sultana?
Sai na nuna masa dakin da ido kafin nace"Ta koma ciki."
A zafafe naga ya shiga dakin ya Rufe kofa, ban matsa ma kaina sai naji abunda ke faruwa ba.

Tun kafin Assadiq ya gayamin Naja kanwar sultana ne na gane suna diban kama, sai dai ba Halinsu d'aya ba ita ba ruwanta ga hankali da taga zan yi abu zatace in kawo ta tayani.
Tare da ita muka kwashe komai zuwa Kitchen na barta ta na gyaran inda su Asim suka ba'ata ni kuma na kwashe su Asim zuwa daki zan yi musu wanka.
Har sun fara barci na shiga da su Tiolet daya bayan daya na yi musu wanka duk sun bata jikinsu da maiko da miya.
Na gama saka ma Asim wasu kayan ina kokarin sakama Asif sai ga Assadiq ya shigo ransa bace.
Bai yi min mgana ba ya shiga Tiolet sai ga shi ya fito sai kuma naga ya Bude dirowa ya dauko kayan barci ya koma Tiolet ya sauya.
Ya sake fitowa ya gyarama Asim kwanciya a tsakiya ya gyara Filo zai kwanta.
Sai da na gama saka ma Asif kaya na mika masa shi, shima ya kwantar da shi gefen dan'uwansa a tsakiya.
Kallonsa na yi naga ya juya ya Rungume ya'yansa.
Cikin mamaki nace"Assadiq ba anan zaka kwana ba fa?
Da sauri ya kalleni kafin yace"Sai a ina? Kai tsauye nace"A dakin Sultana mana, ai kana wajenta har ta koma Bisa adalci ita ke da kai, ni daman ai muna tare dakai kafin ta zo."
Shiru ya yi na wani Lokaci kafin yace"Yarinyar da ta zo da ita fa?
Kai Tsaye nace"Ta zo dakina mu kwana tare, kaga ai bazata kwana a falo ita kad'ai ba"
Sai ya jinjima min kai duk da yanayinsa ba dad'i haka ya mike ya Dauki wayarsa har ya kusa fita ya kara Dawowa ya Dauki karaman Computer dinsa ya fice bayan yace min sai da safe.

Nima na rakasa da sai da Safe.
Ina ga shi yace ma Naja ta shigo mu kwanta sai gata ta shigo nace taje ta yi fitsari tazo mu kwanta.
Ni kan na dad'e ban yi barci ba akwai wani Tunani da ke yawo a raina Shi na ke ta nazari ba na so na fara yin wani abu batare da sanin Assadiq ba.
Mun yi chart da Surayya ta ke tambayata ya bakuwa na ce lafiya.
Bata gayamin komai ba sai dai ta kara tambayata ko Sajida ta kirani?
Nace mata bata kirani ba.
Daganan sai na kara Fahintar wani abu ya faru, wanda yasa sultana tazo kuma daman Umma tace an yi yar hatsaniya.
Da asuba Assadiq ya tasheni sallar asuba shi kuma ya tafi masallaci.
Saboda yana fita aiki in na yi sallah ba na komawa na ke fad'awa kitchen na sama masa abunda zai ci.
8am ya ke fita kafin lokacin kuma ya karya ya shirya, har kuma ya bar gidan Sultana bata fito ba abun karyawanta ma Naja na ce ta bita da shi Tunda ta zama Hakima.
Ni bazan yi mata abunda tayi min ba, Ummi ma na goye bayan Naja tun safe, ko wanka ba'a yi mata ba ni na karbeta na yi mata tare da Asim.
Ai ko da naja ta kaita a saka mata kaya ina falo ina jin Ta na yi mata fad'an Uban wa yace ta ba ni yarta?
Salon aje a goga mata wani bala'in ko kashin tsiya.
Da karfi ta rika yi saboda naji, ni kuma sai na yi kamar ban ji ba ta kuma tayi ma Naja kashedin kada ta  kara bani yarta in ta kara sai ta yi mata Duka tsiyan
A raina nace abun bai kai nan ba, rike yarki ai nima na Haifa.
Assadiq ya kirani yaji ko ba ma Bukatar wani abu? Nace ba ma abukatar komai.
Ni kadai na ke Budirina acikin gidana sai Naja da yau ta hanata ma zaman Falo tare da su Asim.
Komai na Dafa daki nake aikama Sultana taci kuma ta bar shi aciki sai zan yi wanke wanke na ke saka Naja ta shiga ta Daukomin.
Haka na ke tafiyar da ita, tun kuma ina saka ran yau zai ce min zata tafi har naga ta kwarari sati ta na Hutu ina yi mata Bauta.
Sannan ni da tazo gidana ne nice in ta fito na ke gaisheta ta amsa kamar ba ta so wani Lokacin sai in a gabansa ne ta ke amsani.
Ranar da ta cika sati muna cin abinci da Daddare kai Tsaye ya kalleta yace"Yau dakin Siya zan kwana, ki tafi da Naja dakin ki."
Dagowa na yi ina kallonsa sai naga ya had'e rai, kuma daman na lura tunda sultana tazo ba wani jutuwa tsakaninta da Assadiq.
Shekaranjiya ina jin tashin muryansa kamar ya na mata fad'a ne.
Kafin na yi mgana ita ta rigani da cewa'"Banga ne ba?
Kai tsaye yace"Da hausa na yi mgaana ko baki jin Hausa ne?
Baki ta tura kafin tace"Tabdijam wlh ba'a isa ba, ni da na zo kwanan nan ita ai anan take koda yaushe tare dakai in adalci zakayi min a dakina zaka zauna har sai na gama zama na tafi."
Shima kai Tsayen yace"Shine na yi miki na fitan hakkin bakunta, sai ku raba kwana Bibbiyu, tunda naga kin wuce bakuwa yanzu kin zama yar gida."
Ta kallesa ranta na suya ta gane take takensa so ya ke ta koma gusau kuma wlh ita taga waje bazata koma ba.
Kuma ta fad'a masa kada ma ya Dauka wasa ne.
Shi kuma ransa ne ke bace yarinyar nan ta mugun rainasa ya na mgana tana maida masa martani.
Ya ji kunya da yaji wai Dambe ta yi da Sajida Surayya ta gayamssa Tun ranar da Sultanan ta zo.
Kuma ya Tsareta ya tambayeta ta na kuka tace Sajida ce ta fara zagin Ubanta.
Ya yi ma sultana fad'an baya son reni kada ta kara gigin fad'a da yan'uwansa in bata ci darajan suna yayyensa ai su ci Daraja suna yayyenta ita.
Kuma ya yi hakame saboda kada ta kara kwatatanwa a gaba ammh a ransa yaji dadin haka.
Yanzu sai Sajida ta kara gane bata da wayau, Tunda abokiyar shawaran nata yanzu itace abokiyar Fad'anta.
Yace in ta yi sati ta koma Gusau ta saka masa kuka abunda yasa ya kyaleta ya bari sati na sama in zai tafi ko taki ko taso sai ya tafi da ita baxata zauna a gidansa ta hanashi zaman lafiyan da ya samu ba.
Ni kuma gudun Fitinar Sultana yasa nace na bar mata kwanan nawa gabadaya har ta tafi.
Shi kuma sai yaji Haushi ya fara min Fad'an meyasa na fara abunda ba Halina ba?
Gaddama zan fara yi masa?
Ina jin haka sai na yi shuru na koma ina bashi Hskuri.
A fusace yace"Nan gidana ne, ku kuma dukkan ku mata na ne, kuma hukuncin da na yanke da shi za'a yi amfani na gama mgana."
Sultana ko na jin haka ta mike ta rike Kugu ta girgiza jiki kafin tace"Tab wlh baku isa ba, in a can kun saba Tauyemin hakki anan ko ba wanda ya isa."
Dagani har shi ita muke kallo, sai naga kuma hankalin Naja ya koma kanta sai na yi saurin cewa ta tafi da su Asim dakina su cigaba da wasan su acan ta na goye da Ummi ta rike hannayen su Asm suka tafi dakina Tunda sun gama cin abinci.
Sai da suka shige sannan na kalli Sultana ta na wani cika ta na batsewa kafin nace"Ki yi hakuri, dakin ki zai rika kwana har ki tafi in sha Allahu."
Cikin Fusata Assadiq ya kira sunana"Hasiya.."
Na kallesa da Sauri ina fadin"Assadiq menene aciki? Ai ni muna tare dakai ko da yaushe ita kuma zuwa ta yi zata tafi nan da Lokaci kad'an"
Kamar sultana na jirana sai ta harzukomin ta na fadin"Malama yi min shuru ba na son munafunci, har kina wani cewa zan tafi to ba inda zani nan gidam mijina ne ina da iko da shi kamar yadda kema ki ke da iko da shi."
Ina jin haka sai na yi shuru, shine ya kalleta cikin bacin rai yana fadin"Na gaya miki zan sake fad'a miki kuma nan ba gidan ki ba ne, gidan Siya ne gidan ki na Gusau kin barosa."
Sultana tace"Wlh bazan yarda ba ai gidan ka ne ba nata ba,nima ina da Iko da abunda ka mallaka Ehe."
Cikin gatsali yace"ok tunda hakane kina son kwana da miji sai Siya ta baki girki shikenan'
Siya daga gobe ta fara yin girki, ta bar kara miki walaha kin ji na gaya miki."
Sultana ta Fashe da kukan kissa kafin tace"Wlh ni bazan yi girki ba, dame zan ji da Girki ko da Reno. Ni bazan iya ba"
Kai Tsaye yace"Fine sai ki tattara ki koma gidanki, ki bar mata nata gidan."
Cikin Dara kafa tace"Saboda me ka ke korana? Baka san na zo kusa da kai?
Assadiq yace" saboda ba alheri ya kawo ki ba, in da zaki zauna lafiya da matata kibi Umarnina ko shekara zaki yi bazan damu ba."
Sultana ta shiga mganganun cewa yace mata shed'an ita wani rashin Alheri ta kawo kaza kaza sai yi ta ke yi bai tanka ta ba.
Ni kuma na kwashe abunda muka bata na kai kitchen na koma daki na basu waje suna cashewa yana mgana ta na maida masa martani kamar bata san Darajansa ba.

Ko da na koma daki yara duk sun yi barci sai na gyara musu kwanciyar, nidai har na kwanta ina jin ta shin muryoyinsu a falo suna Rigima kai wannan yarinyar akwai rigiman tsiya.
Da safe kuma ya kara Jaddamin Sultana zata yi girki.
Ai bayan fitansa har 3pm na rana bata Fito ba maga zan yini da yunwa ni da yara na tashi na Dafa muka ci.
Ba kunya da yunwa ta Ciyota sai ga ta fito falo muna zaune muna kallo
Naja ta kallah kafin tace"Ke ina abincina?
Ni yarinyar ta kallah tunda taga yau ban bata ba ta kai mata kamar yadda na saba ba.
Naja ko tace ai ban bata nace ta kai mata ba, sai kawai ta Wuce kitchen ta na fadin"Ba wanda ya isa ya hanani cin abincin da mijina ya siyo ya kawo"
Na so nace mata da ya siyo ai ban yi mata iyaka ba, gwara taje ta dafa da kanta bazan hanata ba.
Ammh sai na Tuna da wani abu sai na yi kamar ban ganta ba.
Kuma har na Daren bata girka ba, ni na girka shi da Assadiq ya dawo yaga bata yi ba zai yi fad'a na ce masa don Allah ya yi hakuri ya kyaleta ba girmansa ba ne ya Biye mata suna sa'insa.
Da kamar bazai hakura ba sai kuma ya kyaleta, kuma na rokesa alfarman ya rika kwana a dakinta har ta tafi.
Cikin Takaici yace"ta ce miki ta na da Niyar tafiya?
Nima cikin mirmishi nace"Bakomai sai na bar maka kai, har sai ka Gundureta."
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Ban taba sanin yarinyar nan Fitinanniya ba ce sai yanzu acan ta gama yi ma kowa rashin kunya har su Umma bata bari ba, nan kuma zata zo ta hanani zaman lafiya"
Ni dai sai na cigaba da bashi baki har yace zai saka mata ido.
Tundaga ranar na dai binta da abinci acikin daki, sai dai ta fito in taji yunwa ta dib'a a cikin Kitchen.
Kuma bata ganin girmana ballatana in samu arzikin ina girka mata taci.
Gaisheni ma batayi sai dai ta shiga daki ta kwana da miji ta fito ta na Chab'a ado ta na isa da gadara ita adole gidan mijinta ne.
Assadiq bai gayamin Abunda ya Faru Tsakanin Sultana da Sajida ba.
Siyama ta kirani ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login