Showing 99001 words to 102000 words out of 116366 words

Chapter 34 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

340

kina mgana kamar da ni ki ke, nima a baya ina daukan duk macen da ta zama bazawara wata mara gata ko wacce da gangan ta bari hakan ya faru, sai na ke ganinsu kamar ba su kaimu zama mata ba, sai da abun ya faru da ni na kara gane rayuwa na kuma san cewa Mace ba ta siyan ma kanta zawarci sai idan Allah ya kaddaro mata."
Irin kukam da Sadija take yi sai da ta bama Umma da Mama tausayi.
Umma a ranta itama sai taji kamar da ita ake yi, itama ai ta kyamaci bazawar sanda Sadiq ya kawo Hasiya.
Gani ta ke yi kamar gazawa ce ke saka auran mace mutuwa.
Ashe ba haka ba ne, Komai na Duniya nan Allah ne ya ke tsarashi kuma ya faru a yadda ya ke so.
Matar nan har suka fita Sajida na kuka Umma da mama suka bi bayansu zuwa bangaren Innani.
Suna fita Sajida ta mike sai ji ka ke tas! Tas !
Sajida ta wanke Sultana da maruka har Biyu cikin bacin rai ta nuna ta da yatsa ta na fad'in"In kika kara kokarin tozartani acikin mutane sai na yi miki Bugun tsiya sultana, tunda sakara kike mara kunya."
Sultana Dafe da kunci ta na kallon Sajida kafin tace"Kika mareni Anty Sajida? Me na yi miki?
Sajida tace"Uban ki kika yi min? Nace ubanki kika yi min"
Sultana ta mike jikinta na rawa ta nuna kanta ta na fad'in"Ubana kike zagi?
Sajida tace"Shi na zaga wannan tsoho mai gemu da ke zaune a kauye shi na zaga maras mutumci."
Sultana ta saki shewa kafin tace"Wlh ba ubana ba, sai naki Uban, tunda uba bai fi Uba ba, kuma kada ki kara marina akan gaskiyata ba karya na fad'a ba da gaske ne ke din bazawara ce second Hand....!
Ai bata gama Rufe baki ba Sajida ta Buge mata baki ta na fad'in"Ke ce zaki sama second hand da ikon Allah Sultana ba ni ba, ban da an cusa ma Sadiq ke mai zai yi da ke? Banza kucaka kazama wacce bata san ciwon kanta ba.!"
Sultana na duba bakinta ta ga jini sai ta fashe da kuka tana fad'in"Kika fitar min jini? Wlh sai na rama kuma eh din ance bazawara second hand ce ni ai kuma ko da cusani aka yi da aurena mijina bai sakeni saboda bani  da hali mai kyau ba kuma kowa yasan halina ba na had'a husuma kuma ba na yad'a sharri."
Sajida ta nuna kanta ta na fadi'ib"Ni ki ke fad'a ma wannan mganganun ina yayar mijinki?
Sultana tace"An fad'a miki, ai ke ba uwata bace da zan ji kunyar gaya miki mgana."
Sajida tace in ba zane Sultana ba ita ba yar halas ba ce..kawai ta Rufe Sultana da duka itama ta na kokarin ramawa.

Umma Mama na shashen Innani Naja taje ta kirasu Allah yasa bakin sun tafi a haraban gidan suka ci karo da Siyama ta dawo rakasu.
Suka dumguma bangaren Umma suka iske Sajida ta haye ruwan cikin Sultana ta na jibga.
Ga Ummi na kwace kan kujera kamar ta sani ta na tsala ihu.
Dakyar su Umma suka rabasu.
Sultana fuska ta kumbura baki da Hanci ya fashe ita kuma Sajida duk sultana ta cijeta ta yakushe mata jiki ta kuma yagamata riga.
Sannan ta riga jan gashin kanta har tana Cire mata tsinke kitson ta gashinta guda d'aya.
Umma cikin bacin rai ta kallesu kafin tace"Me zan gani haka? Sajida abun kunya da kanwarki kike dambe?
Sajida na haki tace"Na rantse sai naci Uban yarinyar nan".
Sultana na hawaye tace"Ba dai Ubana ba."
Siyama na gefe tace"Sultana baki da gaskiya miye haka?
Mama na gefe tace"To kana karami ma ina kai ina rashin kunya?..
Inaga tun mganar dazu ne ke sultana baki kyauta ba kamar tozartata kika yi."
Umma dai takaici ya hanata mgana ta koma daki ta zauna ta yi Tagumi.
Sultana kuma ta saka kuka tace an had'e mata kai saboda an ga ba gidan Ubanta ba ne.
Ta tattara kayanta da yarta ta tara Naja suka tafi.
Ita kuma Sajida na yi ta mata Fad'an ba girmanta ba ne ta tsaya ta na biye ma Sultana har ta kai su ga Dambe.
Siyama ma tace abun ba tsari.
Kuma daman Sultana ta zama mara kunya yanzu.
Sajida na kuka ta na gayama Mama da Siama irin tozarcin da Sultana ta dad'e ta na yi mata.
Su kansu sai da suka ga bakin Sultana suna mamakinta Aure ne ko iskancinta ne ba su san abunda ya sauya ta ba.
Umma ta kasa ko yi ma Sajida mgana saboda Haushi.
Sai da Sajidar ta sameta ta bata hakuri sannan ta gayamata duk abunda ya faru.
Umma tace"Uhm sultana sai shirin Allah, bai kamata ki zagi babanta ba tunda uba bai fi uba ba, bacin rai da kika Biye mata kina gaba da mijinta bama ita ba, ba girman ki ba ne ki zauna kina fad'a da ita."
Sajida tace in sha Allahu bazata kara ba.
Mama dai kusanta da rariyan baki ita takwashe labari ta gayama ya'yanta.
Surayya kuma Sajida ta je har gidanta ta na kuka tana gayamata abunda ya Faru.
Surayya ta yi ta ma Sajida fad'an wani irin raina kanta ta yi da Sultana zata yi dambe da ita?
Surayya tace"Ba ga shi nan ba, ina gaya muku gaskiya ke da Sadiya kuna gamin ina kare ma Sadiq ba, ai gashi nan ta nuna muku halinta, daman ina amfamin Babba ya rika shigema yaro da sunan ba shi shawara?
Wlh daman nasan haka zai faru."
Sajida na kuka tana fadin"Wlh naga abunda kike fad'amin a baya, don Allah ki kara bama Sadiq hakuri, Hasiya ma ki bani lambarta zan kirata na bata hakuri."
Da Farko Surayya taso ta Fattaketa ne sai daga karshe taji Tausayinta sosai..
Tace ta zauna gidanta ta kwana Biyu ta huta.
Sadiya ma da taji sai jikinta ya yi sanyi tace Lalle Sultana ta zama yar iska mara Mutumci.
Ta kirata a waya tanaa mata fad'an abunda ta yi bata kyauta ba sultana ta kashe mata waya.
Wato ba ta da Lokacinta Sadiya da zuciya ta shirya ta bita har gida ta mata Tas tace taji kunya.
Taje ta nemi wasu dangin tunda kuma ta raina gidan ubansu kada ta kara ganin kafarta a gidansu.
Sultana ta rika kuka tace sun ci mata Mutumci kawai sai ta shirya kayanta Bata so taje shinkafi Tunda ba mai yarda da ita acan.
Kai Tsaye batare da sanin kowa ba Washegarin Alhamis ta je tasha ta hau mota ita da Naja da Ummi sai garin Abuja.
Suna sauka ta daga waya ta Kira Sadiq tace gata a Abuja yazo ya Dauketa.
Yana Office ne zaune ammh sai da ya mike cikin mamaki yace"Abuja kuma?to ke da waye?
Kai Tsaye tace"Ni da Ummi da Naja."
Saboda tsabar mamaki sai da yavce"lafiya kuwa? Kin manta na fad'a miki gobe ina hanya tafe?
Cikin gatsali tace"Ina sane, wulakanci aka yi min acan shiyasa na taho wajenka in kuma kaima zaka wulakantani ne shikenan sai na san inda zani."
Bai Tsaya wani Tunani ba yace su tsaya a inda suka sauka gashi nan zuwa yanzu.
Har ya dauki mota ya fita yana tafe yana mamaki da Tunanin me Sultana ta zo yi a Abuja?
Yana hanya ya kira Umma yana gayamata ga sultana tazo Abuja ita kad'ai me ya faru?
Umma kai tsaye tace"To ina zan sani ni tunda ba ta daukeni uwarta ta gayamin gata zuwa ba? Sai ka je ka sameta in ka tambayeta sai ta gayamaka abunda ya kawota."
Daga haka ta kashe waya daganan yasan ba lafiya.
Shi tunaninsa  yana zaman lafiyansa da iyalansa zuwan Sultana zai iya lalata masa yar natsuwarsa.



*Janafty*
*TMWB3K019*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65

A Jabi suka sauka na cikin Abuja shiyasa ya d'an dauki Lokaci kafin ya karisa, Sultana kuwa sai kiransa ta ke yi yana ce mata gashi nan bisa hanya.
Ya yi mamakin ganin Sultana yarkace yarkace kamar wata yar gudun Hijira daga ita har yar Rakiyan nata daga gani sun sha wuya.
Ummi ma sai rigima ta ke yi, Sultana uwar banza ce son jiki ya yi mata yawa wai Naja ta mika ma Jaririya ita ta na tsaye kamar wata sakara.
Shine ma ya yi saurin karb'an Ummin a hannun Naja ya kuma karb'i kayansu ya saka a bayan mota.
Da Mamakin Akwatin da yaga Sultana ta kwaso ya bude mata gidan gaba ta shiga ta zauna Naja kuma ta zauna a gidan baya.
Sun fara tafiya ya mika mata Ummi yace ta bata nono ta na kuka, ta karb'eta ta na tura baki. sai alokacin ya lura da kumburin fuskarta na Fad'an da suka yi da Sajida.
Cikin mamaki ya kalleta kafin yace"Me ya same ki a fuska kuma?
Kallonsa ta yi kafin tace"Bakomai.."
Ta fad'a lokaci d'aya ta na kauda kai can garin kalle kallenta Nono ya shake Ummi ta fara tari.
Sadiq ya fara yi mata fad'an meyasa ita ba ta kula ne?
Cikin gatsali tace"to ba ita ta shake da kanta ba."
Cikin Hararanta yace"Da ta shake ke kuma uwa mara kula ko?
Haka ake ba yara Nono? Kin sakar mata shi yaushe ta saba ballatana ta iya rike kanta, duka duka yaushe aka haifeta? Ya kamata ki rika lura Sultana kin girma tunda ki ka zama uwa yanzu."
Tura baki kawai ta yi bata yi mgana ba, sai shi nw ya nuna mata yadda zata saka Ummi a saman kafad'anta ta jijjiga ta na Buga bayanta tare da Hura mata kanta zuwa wuyanta.
Tana yi kuma ta na tura baki a Fili ya Furta"Allah ya sauwake miki, da kike son ki haifi yan biyu in da Allah ya baki na tabbata wlh bazaki iya renon su ba  tunda ga shi guda d'aya ce ammh ta gagareki."
Da Sauri Sultana tace"Ai ko zan iya."
Kallonta ya yi ta kasan ido a rene kafin ya maida hankalinsa kan Tukinsa.
Batare da ya kara kallonta ba yace"Me ya faru ne a can gusau kika taho ba wanda ya sani.?
Kallonsa ta yi kafin tace"Umma ta sani mana."
Kai tsaye yace"Bazaki daina min karya ba ko Sultana?
To na yi magana da Umma kafin na zo nan kuma ta tabbatar min bata san kin zo ba."
Sai ta kifta ido kamar wata barauniya sannan ta wani tura baki kafin tace"Gidan mijina ne sai na nemi izini zan taho.?
Kai tsaye yace"Gidan ki na can gusau nan gidan Siya ne, kinsani kuma."
Hararansa ta so ta yi sai taga yana kallonta sai kuma ta fasa ta koma ta na sunne kanta kasa kamar wata munafuka.

Suna tafe a mota ya tuna bai kira Siya ba, kuma bai kyautu sai dai taga baki kawai ba sanarwa ba.
Nan take ya rage gudun motarsa ya Dauki wayarsa ya kirani.
Lokacin ni kuma ina zaune a falo Tibi na aikinta da Mbc3 Cartoon saboda su Asim.
Waya ce a hannuna tunda yanzu saboda zaman kad'aici yasa na waye da sanin Kafafen sada zumunta.
Ina yin Faceebook har da Instagram, ina cikin Groups sosai na karuwa na ganin abunda ke faruwa a duniya.
Ina cikin Sirrin y'a mace a Facebook, sannan Ina cikin Arewa open diary, sannan a Intagram ina cikin Northenhabiscuss.
Ina ganin abubuwa sosai kuma ina karuwa na sha kuma cin karo da ma su irin abunda ya danganci Rayuwata.
Daganan na Fahimci yanzu mutane sun maida Canfi dabi'an su.
Sun kuma sakashi cikin Addini mun saki Allah mun kama mganganun jahilai da malaman tsubbu marasa tsoron Allah.
Ina Tsaka da dube duben Labarai na ban aljabi da Tausayi da mamaki da yanzu na kware wajen bibiya kiran Assadiq ya shigo.
Asim da Asif suna daga can gaba a kasan Cafet suna kallo rabi da rabi kuma suna wasa da Motarsu na roba irin na yara mai tafiya d'in nan.
Da zumud'i na Daga kiran nasa ina mai Fad'in"Mijin Siya."
Shima cikin Farinciki ya amsa min da cewa"Matar Assadiq."
Wanda fad'in haka da ya yi sai da Sultana ta kallesa wani kishi mai zafi ya Turniketa.
Wato matar Assadiq ita da kai Tsaye ya ke kiran sunanta ba Tausasawa a cikin kiran nasa  ammh kalli yadda ya ke mgana da Matarsa cikin girmamawa kamar ta na gabansa
Ya sha harara shi ko bai ko kalleta ba Rabin hankalinsa na wajen Siya rabi kuma na wajen Tuki.
Cikin yanayin maganarsa yace"Ya gida?
Da sauri yace''Gida lafiya lau, sai dai kewarka da mutanen gidan suka yi."
Cikin yar Dariya yace"Nima na yi kewarku, ina su Asim?
Na kallesu kafin nace"Ga su can suna kallo rabi kuma suna wasa kasan su.'
Jinjina kai ya yi kafin yace"ke kuma fa?
Ina dariya nace"Kasan ai abunda na ke yi ko?
Shima dariyan ya maidamin kafin yace"Nasani kina nan kan waya kina Shige shigen da yanzu kika saba da shi."
Mirmishi na yi ina kara fad'in"Kamar ka sani, ina can ina karanta wani Labari kamar irin nawa labarin, Mijin Siya na fara wani tunani fa"
Da sauri yace"Tunanin mene?
Ni kuma kamar nasan sultana na gefensa sai nace"sai dai ka dawo sai mu Tattauna mganar na Bukatar natsuwa gaskiya."
Gyaran muryan Sultana yaji da yasa ya tuna da ta na kusa da shi.

Shifa in ya na mgana da Siya ko yana kusa da ita ya kan manta da kowa da komai ne baya ganin kowa sai ita.
Shiyasa ya yi saurin cewa"Ga ni nan zuwa gidan ma yanzu da baki, ki gyara dakin nan da ke kusa da namu don Allah."
Cikin mamaki nace"Daga Gusau ne?
Kai tsaye yace"Eh! Kin dafa abinci?
Cikin zumud'i a zato ko cikin yan'uwansa ne yasa nace"yar sauran miyan jiya da ta rage dazu na Dafa Farar shinkafa naci, su Asim ma goldenmorn na had'a musu suka sha, bakin da yawa ne?
Cikin sauri yace"A'a mutun biyu haka."
Cikin Girmamawa nace"zai ishe su anjuma sai a kara dafa musu wani abun ko?
Shima sai yace min eh, Kamar yana ganina haka na mike ina fad'in"Dakin ma bashi da wani gyara sai dai saboda kura bari naje na share na goge.'
Ya amsa da"Allah ya yi miki albarka Siya, sai mun iso."
Daga haka muka yanke kiran, Ta bangarena ban taba kawo ma raina Sultana ce ta zo ba.
Tunda yace min suna hanya na Ijiye wayata na shiga dakin na fara gyarawa Gado ne kawai sai Wardrope sai cafet akwai Tiolet acikin dakinn.
Ba mu tab'a kwana aciki ba sai dai muna saukar da baki in suka zo mana.
Jiki na rawa na gama sharewa na saka Moper na goge ko'ina har Tiolet sai da na wanke na saka turaran Wuta a Burner mai kamshi.

Sannan na fito na iske su Asim sun min barin madara a falo tunda nan saman Tv sand na dora shi.
Sai na Musu fad'a na ce su hau kujera su natsu ina cikin goge cafet din ne naji Dirin motar Assadiq.
Su Asim sun yi wayau sanin Karan Motar Babansu da gudu suka fita na bisu da kallo shiyasa nace a karshen wannan watan zan kai ma Umms su, tunda na yayesu a Boye batare da Assadiq ya sani ba
Suna da wattanin sha tara kenan shekara Biyu, Assadiq ne ya hana in yaye su tun suna da wattani sha bakwai
Na gama gogewa kenan ina fesa Turaren ruwa na Cafet naji Sallamar Assadiq.
Na juya cikin Fara'a ina amsa sallamar nasa, sai dai bakina ya yi nauyi sanda na ga Sultana a bayansa sai wani mele baki ta ke yi Su Asim kuma Assadiq ya had'asu ya Dauke su, Yarinyar da ke bayanta ne dauke da Jaririyar nata.
Nan da nan na shanye mamakina, na Saki Fara'a ina yi musu maraba.
Na maida abun hannuna bayan Tv da ke falon na isa garesu ina yi musu maraba da zuwa.
Na wuce sultana na karisa gaban Naja na karb'i Ummi daga Hannunta.
Kuma na kalli Sultana ina yi mata maraba cikin Fara'ata nace"Sultana sannu da zuwa, maraba ku zauna mana."
Assadiq daman shi ya samu wajen zama yana bidiri da ya'yansa, Sultana tak bata ce min ba kallo ma ban isheta ba, kamar bata so haka taje ta zauna a kujeren da mijinta ya zauna lokaci d'aya ta na kare ma falon nawa kallo.
Tana wani tabe taben fuska kamar Taga kashi.
Ni na karbi akwatin da Naja ta jawo ina rike da Ummi na shigar musu da shi Cikin dakin da Assadiq yace na gyara.
Ina fitowa na isa gaban Sultana na mika mata Ummi da ta fara rigima ina Fad"in"Ki bata nono, Asim ba ku ga kanwarku bace?
Na fad'a ina nuna musu ita, Assadiq yace"Ku je ku ga kanwar ku mazajen Abbu"
Ya fad'a ya na nuna musu Ummi da ke hannun uwarta da ta had'e rai kamar taga wani abun ki.
Ni kuma kitchen na shiga Dauko musu Ruwa na had'o musu Lemun Maltina da Fanta sai Ruwan Faro mai sanyi na sako a wani babban Faranti na kawo musu nan Tsakiyar falon.
Naja center Table na tura gabansu a kai na sauke musu.

Kuma na durkusa ina zuba musu tunda na had'a da kofunan glass.
Naja na fara mikamawa sannan na mikama Assadiq ya karba yana min mirmishi ita kuma Sultana ganin ta ba ma yarta Nono sai na kyaleta da Niyar in ta gama sai ta zuba ta sha.
Na koma gefe na zauna ina kallonta ta na Ture hannun Asim da ke wasa da Hannun Ummi.
Asif kuma uban karambanin ya na neman haye jikin Sultana ya danne Ummi.
Ina shirin mgana naga ta Tureshi cikin Tsawa tace"Kai baka da Hankali ne?
Ban tashi ba ganin Assadiq ya kalleta cikin mamaki Asif jin an daka mai tsawa yasa ya tsorata shima Asim haka.
Kafin kace me sun fashe da kuka ba su nufi wajen Assadiq ba sai suka nufo ni suna kuka.
Na kama su na rike ina llallashin su ina fadin"baku san kanwarku ba ko? Ku yi mata wasa a hankali kun ji ko?
Suna ta kallo na tunda suna jin mgana, suma ai suna mgana sai dai bata nuna ba ne, ammh sun iya kira sunan Abbu da Mami su san Umma da Abba da Goggo Surayya.
Assadiq ne ke yi ma Sultana fad'a da cewa"Ina yaro kamar Asif yaga hankali sai ki yi masa a hankali Tunda yaro ne"
Baki ta tura bata yi mgana ba, ni kuma ganin su Asim sun yi shuru sai na kwaso musu kayan wasan su nace suje su yi wasa.
Lokaci d'aya ina kallon Assadiq kafin nace"Ko za su yi wanka ne kafin su ci abinci.?
Kai tsaye yace"Gata nan tana jin ki."
Ya fad'a lokaci daya yana mikewa agogon fatan da ke hanunsa ya kallah kafin yace"Zan koma Office akwai wani abun da kuke Bukata ne?
Girgizamasa kai na yi alamun babu.
Ita ya kallah yana jiran tace wani abu sai kawai ta kauda kai kafin tace"Ban ga dakin da zan sauka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login