Showing 51001 words to 54000 words out of 116366 words

Chapter 18 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

345

taso bai hanasu zuwa ba, suma sai yamma suka iso Abba me ke ta shiga yana Fita zuwa Lokacin har Alhaji Jibril da Mubarak da salima suna asibitin, salima ta yi kuka kamar ranta zai fita , tunda su ke ba su taba ganin tashin hankali irin shi ba, duk wanda yaga Sadiq a wannan Halin sai ya Zubar masa da kwallah shi Abba ya sakaya abun, ammh Salima da suka yi mgana da Big sis ta na kuka tana gayamusu halin da dan'uwansu ke ciki, tace ma yanzu a daran nan Hoto kansa za'a yi masa tunda ya samu Buguwa a gani ko buguwar bai shafi kansa ba.
Sai gida ya kara rikicewa, da koke koke duka ba wacce ta yi shirin komawa gida nan suka kwana da kuma Shirin gobe da safe za su bi bayansu Abba suma su ga halin da Dan'uwansu ke ciki.

Tahir ma a daran Surayya ta kirasa ta na gayamasa abunda ke faruwa ya Rud'e daman kuma yana katsina ne yace gobe zai biyo motar asuba zuwa kaduna in sha Allahu.
Mallam Zakari da su Baba Saminu har Abba ma a gidan Alhaji Jibril suka kwana tunda su a tsarin asibitin ba'a kwana da majinyaci sai dai gobe da Safe mutum ya dawo, kuma yana cikin Emergency har Lokacin ba'a Fito da shi ba an samu dai an yi masa Hoton kan sakamakon ne sai a washegarin zai fito.
Alhaji Jibril fadi yake yi"Sai da  daman nace, yarinyaar nan auranta ba alheri ba ne, gashi ta saka yaron nan cikin jarabawa."
Su Abba dai suna ta Sadiq ba su ko Biyema Alhaji Jibril da manganunsa ba.

Dagachan Gusai ba su yarda sun gayama su Abba suna tafe ba, Mijin Surayya ya dauketa ita da su Umma da Mama da Innani sauran kuma mijin Sa'ima ya Tuka su, sai kuma Direban mijin Sadiya shima ya ba su mota dai uku duka kuma gidan suka tafi, megadi kawai aka bari mallam Taju ya na binsu da Fatan isa lafiya da kuma Allah ya tashi kafad'un magajin gida.
Da azahar suka isa can suka iske Tahir ya iso shima Tun safe sai dai sun samu hankula sun kwanta Tunda sakamakon Hoton kai ya fito kuma komai Normal buguwar ba ta shafi kwakwalwar kansa ba.
Kuma an fito da shi daga Emergency zuwa daki na musamman Cuwukan ne kad'ai suka samu Dressing ammh karayan ba'a Daura shi ba Abba suna ta shawaran in da za'a bar shi ko anan din ko kuma a kaisa asibitin dala kano a yi masa Daurin asibiti.
Har alokacin Sadiq barci ya ke yi a wahale sai dai ance da safe ya farka yana ta kukan kansa.
Dukkansu matan nan da kuka suke Fitowa daga dakin nan Sultana kam ta kasa shiga ma saboda tashin Hankali a ranar ma sai ga su mallam Shitu da su Goggo Hassu sun zo suma cikin Tashin hankali.

Saboda yanayin Tsamin jikin Sadiq yasa mallam Zakari yace a barsa anan a yi masa Daurin asibiti ammh in fa akace za'a rika Kai can da mara lafiya nan za'a iya samun matsala.
Domin shi Baba Sammani yace gwara a yi Daurin gida zai fi yin kyau..mallam zakari yace halin da yake ciki za'a duba.
Karshenta dai aka tsaya a matsayar anan kaduna zai zauna a yi masa Dorin asibiti a gani, kuma Abba na saka hannu ya bama likoticin dama sukace a daran za su daura shi.
Abba bai bar su Umma ba saboda Innani Tunda suka zo ta ke faman koke koke, daga  asibitin gidan Alhaji jibril suka tafi sallah dagachan kuma yace su kama hanyar Gusau inda ma yaji dad'in ganin mazajen su Surayya sai ya samu salaman cewa zasu kula da iyalansa.
Maallam Zakari ma Abba ya yi ya koma gida yace yana nan sai yaga yadda Jikin Sadiq ya yi.
Tahir ma da ya yi zuru zuru yace yana nan sai zuwa gobe ko Jibi zai koma ganin haka yasa su Baba Sammani suka juya zuwa shinkafi su da su Goggo Husai a ranar.
Ita Surayya ba ta bi su Umma gidan Salima ba, ta  tsaya a asibitin tace anan zata yi sallah abinci kuma bazata ci ba, suna ta waya da subai ne da ta taso daga kano
Saddiqa kuma gobe zata taso daga Kebbi gabadaya hankulansu yaki kwanciya, Shahida ma ta iso daga katsina dazu kowa ka gani Fuska ta jeme sai jan ido kawai.
Shiyasa bata san abunda ya faru ba, ashe suna fita daga asibitin nan Umma ta bama Sadiya da Sajida kudin mota tace suje Zariya su fattaki Hasiya daga Rayuwar Sadiq su tabbatar da bata kara marmarin kusanto Rayuwarsa ba.
Mama ce kara zuga Umma tana fadin ai wannan yarinya ba matar zama ba ce Annoba ce
Tunda Sajida tasan gidan ita tayi musu jagora Umma tace su yi sauri zata san yadda tayi suka b'ata Lokaci kuma Surayya bata fahimci komai ba.
Ko tasha ba su je ba, a bakin hanya suka samu mota duk da Tsadar da aka yi musu suka shiga hakanan sai Zariya.

**********

Zariya.

Tun ranar da Assadiq ya bar ni zuwa Abuja na ke ta kiran wayarsa a kashe, har washegari to ban damu ba sai na yi Tunanin kila babu chaji ne.
Ko aiki ya yi masa yawa zai kirani Daga baya, ban kara shiga damuwa ba sai da naga har dare bai neme ni ba, kuma na kara kiransa har Lokacin wayarsa a kashe.
Ranar barci na rabi da rabi ne, sai kuma da safe na tashi da sanyin jiki da faduwar gaba.
Haka kurun nake jin wani iri acikin jikina.
Ranar na kira wayar Assadiq ban san adadi ba, in nace bari na kira Anty Surayya sai na kasa sai nake ganin kamar zata ce na cika zakewa ne shiyasa na kasa kiranta. sai dai na kasa natsuwa ina ji araina da wani abu ni bai saba min haka ba, abunda bai taba Faruwa ba.
In dai Assadiq ya tafi Abuja yana isa zai kirani ko ya yi min sakon cewa ya isa lafiya ammh yau har an kwana Biyu ban ji daga garesa ba.
Daman na bari ne zuwa dare in ban same sa ba daga baya zan kira Anty surayya naji ko ita sun yi waya da shi.
Allah sarki bansan abunda ke faruwa ba, ita kanta Surayya tashin Hankalin da ta ke ciki ne yasa ta manta da Hasiyar kwata kwata ballatana ta kirani ta fad'amin.

Tun safe ina kwance kamar ruwa ban iya yin komai ba abinci ma Maman suhailat ta aiko min da Doya da miya naci na sha ruwa dakina kaca kaca cikina ya yi nauyin da yanzu ban iya moruwa. sai dai na kwana in an kira sallah na tashi nayi gabadaya hankalina baya jikina.
Wajen biyu da wani abu na rana naji ana bugamin kofar d'aki kamar hauka abunda ya bani tsoro shine jin ana ta mganganu kuma naji muryan Maman Suhailat na kiran sunana.
Sai na Rarumi dankwalina na taka da Cikina a gaba naje na Bude kofar sai dai me? Ko gama Bude kofar ban yi ba aka Bugo min kofar saman cikina sai gani na yi baya na fad'i a kasa Dabas.
Ni dai ina ji Maman suhalat na salati kuma naga sanda yan'uwan Assadiq suka tsallake suka shigo dakin suna fadin"Bakar Annoba zo ki fice daga Rayuwarmu mun gode, ammh bazamu bari ki karisa mana Dan'uwa ba."
Maman suhailat ita ta kamani ma mike ina raba ido, Sajida ce tsaye a gabana ta nuna ni da yatsa tana fadin"Ki kwashe kayanki kaf ki bani key din dakin nan zan Rufe dakin zaman ki da Dan'uwan mu ya kare, tunda burin ki ya cika kin kusa kashe  shi."
Sai Hankalina ya tashi cikim Rawan murya nace"Me ya faru da Assadiq din?
Kusan ni da maman suhailat muka yi tambayan a lokaci d'aya.
Ban tsamnani ba sai da naji Sajida ta kwasheni da mari sai da na fad'a jikin Maman su Suhalait saboda azaba.
Ta kuma nuna ni da yatsa tana fadin"Har ki ke da bakin tambayata? To yana chan a gadon asibiti ya karareaye duk kuma saboda ke bakar Annoba da Jaraba, Saboda haka Umma tace mu zo mu sallame ki, ki kara gaba ki yi nesa da Rayuwar Dan'uwanmu in ba haka ba ke zaki rasa taki rayuwar."
Hankalina ya tashi cikin Firgici na fashe da kuka na kasa mgana.
Maman suhailat ce ke fadin"subhanallah ku tausaya mata baku ga halin da ta ke ciki ba ne?
Sadiya tace"Mu kuma baki ga Halin data sakamu ba ne? Daga wajenta ya ke ya samu hatsari ya na chan baisan inda kansa ya ke ba, kuma kice mu kyaleta wlh sai ta kara gaba malama ki zo ki kwashi kayanki ko mu yi miki watsi da shi.'"
Ni ban damu da kaina ba irin Assadiq da akace yana chan baisan inda kansa ya ke ciki ba.
Duk da halin da nike ciki haka na Duka ina rokon su gayamin inda Assadiq ya ke su kuma barni naje na gansa daga baya sai na tafi ammh sukace ban isa ba.
Ganin zasu faramin watsi da kaya yasa Maman suhailat tace na bar kuka na shiga na had'a kayana su Sajida ba su da Mutumci.
Ina kuka harda majina na had'a kayana akwati biyu Maman suhailat na tayani, su kuma suna Tsaye zagi da cin Mutimci sai wanda suka manta. ni kuma ina ta Rokon su, su barni naje na Duba Halin da Assadiq yake ciki sukace ban isa ba.
Kaya kawai suka bari na Dauka na Dauko wayata suka kwace da jakata suka caje komai suka kwashe kudin ciki har da Atm dina, Hijabi kad'ai suka barni na saka suka Turoni waje suka rufe dakin su kuma saka key din a jaka.
Allah yasa gidan dagani sai maman suhailat, itace ke ta ba su hakuri ba su ma tsaya sauraranta ba suka min kashedin ko da wasa kada na kuskura na kara nuna ma san kaninsu, na jira a duk inda na ke zan samu takardan sakina, mari da dunguri ba wanda ban sha shi ba suka tafi da komai suka barni Durkushe ina ta kuka.
Maman suhailat tajani dakinta ta na ta lallashina da bani baki.
Taso ma na kwana a wajenta kafin da safe asan mafita nace mata ta bani kudi zan tafi, sai dai ban nuna mata in da zuciyata ke rayamin naje ba.
Sai nace mata gidan Adda Fati zan tafi kamar ta sani sai ta bani 5k ta kuma rakani har bakin Titi na samu adaidaita.
Sai da muka d'au hanya sannan nace ya kaini tasha, motar gada zan hau gwara naje wajen Amma. Da naje na sauke ma Adda Fati halin da nike ciki gwara na tafi wajen uwata a wannan Halin da nike ciki lallashinta na ke Bukata.
Ina mota ina kuka kukan tunanin wani Hali Assadiq ke ciki, shi kawai nake Tunani a raina kuwa ina ta masa addu'an Allh ya bashi lafiya Allah Sarki ashe Shiyasa najisa shuru ashe ashe shi ga halin da ya ke ciki ban sani ba.
A cikin raina na yanke shawaran zan rabu da Assadiq ko saboda son da na ke yi masa na barsa ya yi rayuwarsa cikin salama sannan na kara aminta da maaganar mutane a kaina ni din Bakar Annoba ce.

Gwara na je na zauna gaban Amma na haifi abunda ke cikina na Reneshi in Assadiq ya barmin shi ya Rayu dani in kuma bai barmun shi ba shikenan sai na zauna na cigaba da bautar Ubangiji har ta Allah ta kasance.
Ammh na hakura da yin aure na daina jazama mutanen da suka min hallaci wahala a rayuwarsu.
Na isa gada bayan mangariba saboda motar Bus ce, sai dai a halin da na iske Amma aciki bazata iya ma fahimtar nawa Halin ba.
Na iske Adda kwance ba lafiya sosai kuma taki yarda a kaita asibiti, a sanda na isa jikinta ya yi zafi ya'yanta duk suna kanta tare da Amma shiyasa ba wanda ya iya Fahimtar ina cikin wani hali, ni ma ai sai na Boye nawa na koma cikin yan jajantawa.
Amma kuma ba ta cikin natsuwarta a tunaninta na zo ganinta ne ta ma manta cewa Tsohon ciki gareni haihuwa ko yau ko gobe.
Na isa Garin ko awa daya ban yi ba Adda ta amsa kiran Ubangijinta.
Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un
Kullu nafsin za'ikatul maut."
Kowani rai sai ya dan'd'ani dacin mutuwa.
Sai gani ina taya Amma kukan Rashin yar'uwata a raina ina gayama kaina na Dunkule damuwata kada na bari Amma taji, in ba so na ke a yi gawa Biyu ba tun adaran na dauki wayar Amma na kira su Adda Fati na gayamusu.
Suma ta mamakin zuwana su a tunaninsa ko naji tashin jikin Adda ne yasa na tafi ba su san rashin dad'i ne ya kawoni ba.
Har Ramatu sai da na kira da wayar Amma na gayamata tace zata biyo su Adda Gobe da safe.
Haka ko akayi sun iso har da Inna Talatu sun kuma iske har an kai Adda Gidanta na gaskiyaa.
Ya'yanta na ta kuka damu kanmu Sabida mun yi rashi, Amma tafi kowa jin mutuwar nan saboda Adda ce kadai yar'uwan data rage mata Cikim Dangi.
Allah Sarki Rayuwa Allah ai baya barin wani domin wani yaji dad'i.






*Janafty*
*TMWBK3011*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl
PAID ADVERT✅

Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki
* Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah
* Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari
* Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan
Allah sa mu qaru da juna Ameen



Babu wanda ya lura da Halin da ni ke ciki sai ranar da aka yi addu'ar uku na Adda, sannan ne Adda Fati ta Fahimci ko sau d'aya bata ganni da wayata ba shine ta ke tambaya ta.
Ni kuma cikin sauri na sanar da ita cewa ta lalace na barta a gida ne.
Daganan bata kara tambayata wani abu ba, a ranar Ramatu da Inna talatu suka tafi tare da yan dogon gida na samaru maman boy da maman Salihi sun zo Amma gaisuwa a ranar, sai suka koma tare da su Ramatu.
Adda Rukayya ma sai da ta kara tambayata ina wayata nace ta lalace na baro ta gida, ita dai cikin mamaki tace"To da wata waya ku ke mgana da Abubakar din?
Mirmishin yake na yi mata kafin nace"ai baya garin, ma'aikatan su ta tura su aikin titi wani gari in da ba Service shiyasa ma yace nazo nan wajen Amma kafin ya dawo."
Saboda tun washegarin Biyu da Rasuwar Adda na saci wayar Amma ina ta kiran wayar Assadiq ammh yaren guda d'aya ne wayarsa ta na kashe ne.
A dangin Babanmu Baaba ta lagos ce kad'ai ta kira Wayar Amma ta yi mata gaisuwa tace itama Baba Saminu ke gayamata ki rasa ta ina suke samun Labarin mu. Shi ko gaisuwan bai kira ya yi ma Amma ba ammh ya iya yad'a ma wasu.
Tare muka zauna da Amma har aka yi addu'ar bakwai din Adda, ba na yarda na yi kukana gaban yan'uwana Saboda ba na so su fahimci yadda Rayuwata ta kara yin tsudum a cikin tsaka mai wuya.
Kuma ko da sun ga idanuwana sun kumbura ba su cika damuwa ba, a tunanin ina kukan wannan rasuwar da aka kwantsama mana ne.
A daran da Adda ta yi bakwai ya'yanta suka taramu har da Amma suna rokon mu kada mu ce zamu dauke Amma ta koma wajen mu da zama, bayan Adda ba su da wata uwa da ta wuce Amma saboda haka zata cigaba da zama tare da Hamma Isuhu da iyalansa.
Mu ma daman bamu da wannan niyar ballatana Amma bazata taba aminewa da komawa zariya ba, nan take tace ba inda zataje tana tare da su itama har mutuwarta tazo ta isketa nan da nan sai kuka sai mutuwar ta dawo sabuwa.
Allah sarki ashe mutuwa bata  daukan wanda ke ciwo haka na raya a raina, Amma ce lafai lafai Adda kuma macece mai kazar kazar da alamun karfi Allah dai ya jikanta da Rahma.
Washegari kwana takwas su Adda Fati suka fara Shirin tafiya abunda ya basu mamaki ganina kwance bana shirin tafiya.
Habiba ce ta kalleni ina kwance da katon cikina a gabana tana fad'in"Adda Hasiya ke bazaki tafi ba ne?  naga baki shirya ba ne?
Duk kuma sai da ta yi mgana suka maida hankalinsu kaina har da Amma da ke zaune a gefena.
Adda Rukayya tace"Ina zucci zuccin na yi mgana kika rigani, Hasi nan zamu barki ne?
Ina kokarin tashi zaune nace"Eh yace in ya dawo zai zo ya daukeni."
Sai ba su damu ba sukace Allah ya kaimu ai bakomai sai na kara taya Amma zama Tunda har lokacin bata wani saki jikinta ba.
Amma ta kallo inda jerin akwatunan kayana suke cikin mamaki tace"To zai dad'e ne shi megida naki haka? Naga kin kwaso kaya har akwatina Biyu?
Gabana ya fad'i ammh kuma sai na yi saurin Washe bakina zan yi mgana.
Ammh sai Adda Fati ta rigani da fadin" Amma kika sani ko kayan haihuwa ne, tunda Adda bata raye ke zaki zama uwar zoman Hasiya."
Amma mirmishi kawai ta yi kafin tace"Allah ya jikanAdda, ko a satin da zata rasu sai da tace min Hasiya ta shiga watan haihuwanta ko?
Hasiya na ranta ta yi alkwarin zuwa ta zauna dake ta kula da ke tare da abunda kika haifa ashe Allah mai Hikima bazai bata damar ganin wannan Lokacin ba."
Gabad'ayanmu muka had'a baki wajen fadin"Allah ya jikanta da Rahma."
Amma ta amsa da Ameem Ameen ta na sharan kwallah.
A ranar su Adda Fati da Adda Rukayya tare da Habiba suka koma Zariya suka barni tare da Amma ina sake lallashinta sannan ganina yana sawa tana sakin jikinta.
Ya'yan Adda suma kowa ya koma wajen neman abincinsa mai auran ma mace itama ta koma gidan mijinta daman Badd'o na wajenta tun Adda na raye yanzu ma wajenta ta koma.
Sannan har a lokacin makota da abokan arzuka suna ta shigowa kara yi ma su Amma gaisuwa.
Ni kuma koda yaushe tunanina wani Hali Assadiq ya ke ciki?.
Har yau da Adda ke cika kwana goma da Rasuwa na kara gwada layinsa ammh amsar dai iri d'ayace a kashe.
Sai na fara tunanin ko dai wani mummunan abu ya faru da Assadiq ne? Kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login