Showing 105001 words to 108000 words out of 116366 words
bani Labari tas, sai naji Tausayin Sajida har ga Allah na san zafin sakin aure sai naji kamar alokacin ya faru dani.
Kuma na bama Sultana rashin gaskiya, komai lalacewar Sajida ta na da kimar da bazata iya maida mata mgana ba ballatana ta yi dambe da ita.
Ammh Saboda bata da Mutumcin har Anty Surayya ma a halin da sultana ke nunawa zata iya sa'insa da ita, Siyama ta yi ta son taji ya mu ke zaune da Sultana? Bakina kanin kafana nace muna zaune lafiya saboda mene ita fa Sultana ta su ce, ni ce bare na zak'e watarana zata iya barewa dani.
Sajida kuma bata kirani ba, ta kasa kirana Saboda kunya.
Sai ni da kaina na kirata Tunda ina da Lambarta ashe itama ta karb'i lambata.
Ina kira ta dauka muka gaisa ta na rawan baki.
Ta kasa yi min mgana, sai ni ce na yi mata jajen mutuwar auranta.
Cikin Sanyin murya tace"Hasiya ki yafemin, na gama dariyan taki kaddaran ga tawa ta fad'amin.".
Kai Tsaye nace"Bakomai ni ban taba rike ki a raina ba."
Batare da na tambayeta ba ta fara bani Labarin irin rashin mutumcin Da Sultana ta rika yi mata abun ba dadin ji.
Ta karishe da cewa"Sai yanzu na gane a wannan Rayuwar da muke ciki in kaga kaddaran wani kada ka yi dariya Saboda baka san yadda taka zata zo maka ba."
Nace kwarai da gaske,hakane Allah yasa mu fi karfin zukatanmu ya kuma zaunar damu lafiya.
Mun jima muna hira da ita, ta na gayamin Yadda Sultana ta ci mutumcin su ta gudo nan
Sajida tace"Wlh in ta yi miki wani iskanci ki ci ubanta."
Ni dai dariya kawai na yi ban iya gayamata komai ba sai ma na kare sultanan nace muna zaune lafiya.
Umma ma mun sake mgana itama na nuna mata muna zaune lafiya.
Abunda ya ke bani mamaki da sultana Mace ce Fitinanniyar mara son zaman lafiya.
Duk hanyar da zata nemi fitina shi ta ke yinsa domin na tanka tamin Wulakanci, sai kuma ni ba na biye mata Tunda naga ko wanda ya Ijiyeta bata raga masa ba, ballata ni kuma saboda Tsabar rigima suna can suna ta karatu a makaranta ammh ita ba karatun ke gabanta ba.
Neman Fitina dani da rashin son zaman lafiya.
Shima na nuna masa tunda yasan Halinta ya daina biye mata, kuma ya daina mata mganar tafiya gaskiyanta ne itama ta na da iko da abunda ya ke mallakinsa ne.
Kuma Assadiq na jin mganata in dai na bashi shawara ya na dauka kamar yadda nima na ke daukan na shi Shawaran
Sai ga Sultana ta yi sati uku tare damu ta gama neman fitinarta taga bata samu abokin tafiya ba, dagani har shi mun koma mun saka mata na mujiya.
Duk abunda tace shi ta ke so ayi zan Taushi Assadiq nace masa ya yi Hakuri don Allah mu rabu da ita lami lafiya.
Ni fa har wake waken Habaici ta sha yi min na mai Farar kafa da bakar Annoba kala kala sunaye ta ke kirana da su har da bazawara mai kwacen miji.
Ban taba daga kai ba, na sakata a layin marasa hankali da sanin Ciwon kansu wlh.
Sai gashi da kanta tace ma Assadiq zata koma zasu fara Test a makaranta ammh suna gama Jarabawa zata zo nan ta yi Hutu.
Ni kuma a raina nace Gusau zan je na yi hutu na in tagama Hutun ta dawo nima sai na dawo.
Har Allah ka yi nisa da wanda baya kaunar ko ganinka.
Saboda ita ya yi shirin tafiya Gusaubni kuma sai alokacin na gaya masa na yaye su Asim
Ya fara min fad'a meyasa ban gayamsa ba nace zai hana ni, bai yi fad'an sosai ba saboda bai ga suna Rigima ba, ni ko abinci da kunu da tea na ke dora musu.
Kuma suna girma suna kara Rage Rigimansu.
Yace shikenan na Had'a musu kayansu Umma da Mama suna da manyan baki.
Nima yaso na shirya muje nace masa a'a sai nan gaba gwara na zauna a gida na yi abunda na kudura a raina.
A daran da zasu tafi na yi masa maganar kudurin da ke raina akan ina so na Rubuta Labarin Rayuwata da Tsaka mai wuyar da na shiga Saboda matsaloli irin nawa suna kara yawa acikin al'umma.
Na dauko Sreenshoot din abubuwan da na Dauka saboda na nuna masa, na irin Labaran da suka yi kamaceceniya da nawa Labarin.
Assadiq ya kalleni ina zaune a falo a gefensa Sultana ta shiga ciki bayan mun gama cin abinci.
Cikin son karin bayani yace"Tunaninki tunani ne mai kyau My Siya, sai dai yanzu in kika ce zaki yi wannan Rubutun ta ina zaki fara? Ke fa ba marubuciya bace?
Cikin kwarin gwiwan da na saka ma kaina nace"Zan nemi marubuta na yi shawara da su, ai ina tare da su ina karanta wasu daga cikin Littafan su. Ga Surayya Dee da muke mutumci da ita sosai Sanadinta ma nasan marubuta da dama dukkansu nasan in naje musu da mganata zasu saurareni kuma su bani shawara sannan ga Anty Habiba iman ikra tare da Anty Sumayyah Abdulkadir Takori da kuma AuntySis tsoffin Marubutan bugawa ne tun Lokacin duniya na kwance, dukkansu ina da kyakyawan tabbacin in naje musu da kyakyawan niyyata zasu bani shawarwarin ta inda zan fara in sha Allahu."
Cikin gamsuwa yace"Dakyau kuma duk wad'anda kika Lissafo duk marubutan ne?
Cikin sauri nace"Eh Sosai ma, kuma suna yin Rubutu cikin ma'ana da Tsabtar alkalami."
Assadiq yace"Shikenan bazan hanaki niyar alherin ba, tunda zaki Rubuta wannan Labarin ne saboda Mutane su gane ba mai yi sai Allah kuma Ubangiji bai isa ya yi ma bawa abunda Allah bai yi masa ba, In har goyon baya kike nema na baki dukkan Goyan bayana Siya ta."
Cikin jin dadi nace"Nagode Mijin siya, ina kara nenan wata alfarma"
Da sauri yace"Ina jinki fad'eta, in dai bata karfina ba zan yi miki "
Da sauri nace"Ka min jagora ka zame min ido a kan wannan abunda zan yi."
Hannuna ya rike kafin yace"In sha Allahu Matar Assadiq."
Mun Cigaba da Tattaunawa ina bashi Labarai masu ban mamaki irin labaran da na ke samu a kan masu Fuskantar irin tozarcin da na Fuskanta a baya.
Ya tambayani a littafi zan Fara Rubutun? Nace sai na yi mgana da d'aya daga cikin marubutan da na gayamasa shawaran da suka bani da shi zan yi amfani.
Ammh ina so na wallafa wannan Labarin ya fita duniya in sha Allahu
Mun jima muna mgana Sultana ce ta sake fitowa jinsa shuru ganin haka yasa na yi masa sallama na shiga ciki.
Da safe tun asuba na tashi na shirya yara Naja ma na saka ta shirya.
Weekend ne ranar Asabar daman tun jiya na yi miyar Naman rago sai na soya musu dambun kaji na zuba a roba nace a kaima Umma.
Miya kuma na innani ne baiwar Allah, sai da naga zasu tafi naji dama na Bisu ammh kuma ina Bukatar natsuwa a gida.
Sai da na Boye sannan suka samu tafiya da su Asim da ke ta kuka kayansu na had'a musu da yawa nace su sha hutunsu wajen kakaninsu.
Sai azahar Assadiq ya kirani yace sun sauka, ina tambayansu Asim yana dariya yace Mama taja megidanta Umma ma haka.
Innani na tambaya yace da sauki, bazai dawo ba sai an siya mata keken da zata rika zama akai tunda yanzu ta zama sai dai a kwantar kuma a tayar.
Kafin Assadiq ya dawo na kira Surayya Dee mun yi mgana na gayamata kudurina taji dadi kuma ta bani goyan baya.
Tare da wasu sharwarin, na kuma kira Hajiya Habiba iman itama sosai ta karbeni ta kuma ji bayanina ta kuma bani shawara.
Na sake kira Auntysis saboda gogewarta a harkan Rubutu da Rayuwa gabadaya.
Dukkansu sun bani shawaran na yi Rubutuna a waya saboda yanzu abun ya koma Direct Print in na yi sai a bugamin shi.
Kuma bakinsu ya zama d'aya sunce bayan na buga zan iya sakin Labari a softy Copy yadda sakon da na ke so zai je ma al'umma da dama.
Sun bani shawaran na yi Bincike sosai kuma na nemi mganar malamai da magabata.
Ni kuma nasan ta wannan bangaren bani da matsala ina da Babban malamina a gefe wato Assadiq.
Da ya dawo shi ya taikamin har na fara Rubutun a computer tunda ya siyamin wata na bama Habiba Tsohuwar tawa.
Sannan Saboda ban saba ba Typing din ba, ya na bani wahala ammh hakanan Saboda na saka abun a raina yasa na Dage.
Koda yaushe cikin bincike na ke yi, Assadiq na kara nuna min wasu abubuwan a Labarin Rayuwata nace bazan boye komai ba.
Hatta sunanaye da garuruwan da abun ya faru saboda so na ke mutane su san cewa da gaske ne ba Farar Kafa a musulunci su kuma saki mganar mutane su kama Allah su gane Ubangiji ne ke da alhakin Faruwan komai.
Ammh Assadiq yace ya na da kyau na sauya sunan garuruwa da wasu mutanen, ammh zan iya amfani da sunana tare da nashi sunan.
Ya kawo min Hujja akwai wad'anda Labarin ya shafa kuma yanzu sun yi nesa da Rayuwata ambatan sunansu kan iya zama matsala ko anan gaba.
Shiyasa sai na bi shawaransa na zan sauya garuruwa da sunayen wasu daga cikin su.
Da na Fara na turashi zuwa wayata da Taimakon Assadiq na kuma Tutturama Marubutan da na yi shawara da su, su ka dubamin su ka kuma jinjina min sannan tare da nuna min inda ya kamata na gyara.
Na saka abun acikin raina shiyasa bana jin nagaji.
Kuma ga shi su Asim basa nan da na sallami Assadiq zan dukufa sai da ya fara min fad'a ne ma nake Tsayawa naci abinci, da sai yammah yini na ke yi da yunwa.
Sannan da daddare ma nace sai nayi, shi ya ke hanani ya sakani dole na kwanta na Huta.
Auntysis ce ta fara ankarar dani ban sama ma labarin suna ba.
Na yi ta Tunanin, wani suna zan sama masa ni da Assadiq mun fi kwana Biyu muna tunanin sunan da zamu saka ma Labarina.
Sai da muka shafe sati sannan mu ka sama masa suna.
Nace a iya rayuwata na Fuskanci Rayuwar TSAKA MAI WUYA.!
Kuma na saka wasu Rayuwaka da Dama da suka Rab'eni acikin TSAKA MAI WUYA.!
Shiyasa wannan Labarin nawa zan saka masa suna TSAKA MAI WUYA(LABARIN HASIYA).
Assadiq yace tabbas sunan ya yi, suma da na tura musu sukace sunan ya hau da Labarin na cigaba da Rubutuna kawai.
Kwarin gwiwan da na samu Daga duka bangarorin yasa na kara zake Damtse, kuma yan'uwana ba wanda ya sani Amma kad'ai na gayamata Tunda ita uwace.
Ta kuma sakamin albarka acikin Lamarin, ni ba suna na ke so na yi ba, sannan ba sha'awar Rubutu ne a raina ba kawai dai ina son na Rubuta Labarina ne domin masu Tunanin akwai mata masu Farar kafa su daina
Da masu tunanin wani zai iya yi ma wani abunda Allah bai yi masa ba.
Da masu Tunanin zawara ba mata ba ne sannan ba su da yanci da gatan da Sauran mata suke da shi.
Wannan shine suka kara sakamin kaimi da Himma wajen Rubuta Labarina.
Kwatsam ina cikin Rubutun karamin ciki ya Bulla a jikina Laulayi ya sakano gaba da dole na ijiye Rubutu a gabana na koma ina fama da kaina.
Allah ya taimakeni sai da na yaye su Asim duk da ban ji dadin cikin alokacin ba ammh ban yi ma Ubangiji Butulci ba.
Na tatattara Rubutun na ijiye a gefe ammh ba wai na hakura da kudurina ba ne.
A cikin raina na saka ko shekara nawa zai daukeni kafin na gama zan yi kokarin na ga mashi in dai da rai da lafiya.
Mata muntashi tsaye mu yaki infection (sanyi) Wani ciwone Mai nacin gaske Wanda idan kikayi wasa xaihanaki jindadin Aure Sannan maganin shi saikin daure da nacin shanshi Akai Akai toh kufito🤌🏽 KUSAI TSIMIN TABAJE DOMIN MUNA DAFASHINE DA INGANTATTUN SAIWOYI MASU AMFANI AJIKI DAKUMA LAFIYA, CIWON SANYI, SANYIN MARA, BASIR DASAURANSU INSHA ALLAH DUK WANI CIWO INDAE NA SANYINE ZAIZO KARSHE DA YARDAN ALLAH KIDAE KIDAURE KIDUNGA SIYAN TABAJE KIJEFI TSUNSTU GOMA DA DUTSE DAYA💃💃💃
Akwai infection Wanda yake nuna kanshi Akwai Kuma kurman infection Wanda baxaki San kinada shiba Amma yanacan yana Miki illa domin duk kyan Kayan mata baxakiga aikinsu ajikinki ba ko Kuma sumiki aiki bayanda akaso ba
Anason duk bayan wata 1 mace tasha maganin infection sbd samun lafiyar jikinta
Alamomin shi sune
Fitar farin ruwa
Kaikayin gaba/ko kuraje
Jin zafi yayin sex
Daukewar ni'ima
Daukewar sha'awa dadai sauran su
Kafin kifara Shan maganin mata yakamata ki fara Shan maganin infection
Ina Yan mata Budurwa kema Yakamata kidinga Shan maganin infection Dan kariya da lfy ki karsai kinyi Aure infection ya Riga yamiki illa Baki saniba Allah y bamu lfy y karemu Ameen 🙏
*Janafty*
*TMWB3020*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl
PAID ADVERT✅
Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki
* Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah
* Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari
* Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan
Allah sa mu qaru da juna Ameen
Ashe bansan cikin su Asim kamar Bonus ba ne sai da na samu wannan, gabadaya na zama a rikice ba na iya komai laulayi na ke yi mai zafi ga Amai da miyau kamar na wanchan.
Ga shi ba na son warin Tafasan abinci warin magi ma ba na so, ballatana na mai ko wani abu.
Shiyasa na daina girki saboda in dai na shaki warin magi ko kamshin Tafasan girki in na rika Amai ranar kamar zan Amayar da Hanjin cikina.
Mun je asibiti an gwada jinina duka duka cikin wattani biyu ne da wani abu, sau biyu muna zuwa ana sakamin Drip saboda karfin jiki sannan ba na iya cin abinci.
Assadiq duk ya shiga damuwa Umma da taji cewa ta yi ya kawo mata ni Gusau har sai cikin ya yi kwari.
Ni kuma sai naga kamar shawaran bata yi masa ba, sai na yi magana da Adda Fati nace ko Habiba ta turomin ita ta zauna tare dani.
Ashe Habiban bata nan tana wajen Amma tunda suka gama Jarabawa.
Sai Adda Rukayya ce da taji ana Jajen yadda za'ayi ta ce ga Amna ta nan zata iya yin komai ta gama primary bata riga ta shiga makaranta ba.
Ban tab'a tunanin Babanta zai barta tazo wajena ba sai gashi ita Adda Rukayyan ta kirani da kanta ta na fad'amin Amna zata zo wajena ya za'a yi?
Ina kwance Lokacin kamar Ruwa Assadiq ya tafi office, ga shi ma yanzu sun fara tafiye tafiye saboda aiyyukan Titunan da suke yi ana tura wasu daga cikinsu wajajen da suke ayyukan Tsoron Assadiq kada Tafiya ta fad'o har da shi, gashi ni kad'ai kuma bani da lafiya.
Kullum acikin bargo na ke yini Saboda na rika rawan sanyi kenan, kai na kara jinjina ma iyayen mu mata Amma kuma kaunarta da Tausayinta sun kara ninkaya acikin Raina.
Cikin Dakushewar murya nace"Adda Babanta kuma ya barta ta zo wajena? Ko baki gaya masa wajena zata zo ba ne?
Cikin Sauri tace"Haba wlh ya sani na gayamasa, ai yanzu shima ya Fahimci duk canfi ne da mganar Mutane baki da wani matsala a tare da ke tunda yaga shaidar haka kina zaune gidam mijinki lafiya har kin fara gina kyakyawan Zuru'a."
Cikin jinjina kai nace"Allah Sarki! Nagode sosai, yanzu to wazai kawo ta? Kuma kamar ta yi karama ku sakota a mota?
Adda Rukayya tace"Babanta yace bazai yi gangancin Turata ita kadai ba, shiyasa na kira ki naji yadda za'a yi."
Jin haka yasa nace ta bari Assadiq ya dawo in na fad'a masa nasan shi zai san yadda za'a yi.
Haka ko akayi sai da ya dawo na gayamasa, shima sai da zamu kwanta Tunda in ya dawo aiki shi ya kan taimakamin na yi wanka sannan ya matsamin sai naci wani abu.
Ina kwance a saman cinyarsa shi kuma yana aiki Bisa Computer dinsa da ke gefensa ni Tsabar yanayin da na ke ciki na manta da wani Rubutun da na fara jama'a ana ta kai waye zai yi na kaya.
Kiran sunansa na yi ya amsa hankalinsa na kan abunda ya ke yi, ina fad'a masa ya kalleni kafin yace"Bansani ba gaskiya, ammh Tahir yace min za su zo shi da Amaryansa abunda za'ayu zan kirasa na tabbatar shin yaushe zai taho?
In cikin sati nan ne sai nace don Allah ya Biya ta Zariya ya Daukota tunda yace min a ranar da za su taho sai ya shiga kaduna."
Da shawaransa muka Tsaya a daran ma yaso ya kirasa na hanashi.
Cikin daure fuska yace"To uban me ya ke yi yanzu? In amarci ne ai ya gama cinye romon tuntuni."
Ina Mirmishin karfin Hali nace"Kada dai ka kirasa, in har kai da ka ke da ni baka gama shanye Romon ba, shima mai auren jiya jiya ai bai gama Cinye Romon ba"
Yana yar Dariya yace"Ina ta ko shan Romo na mai d'an karen dad'i. Ga shi nan sakamakon Romon ne ya nuna a jikin ki.".
Ya karishe fad'a ya na shafa jikina ni kuma na Ture hannunsa na sauke kaina a saman cinyarsa na maida saman Filo cikin Bushewar baki nace"Assadiq sai da Safe."
Saboda bakina yanzu sai ya rika Bushewa har yana fashewa ni dai wannan cikin naga Jalala kala kala.
Sai washegari da Safe ya kira Tahir ya na tambayansa yaushe zai shigo.?
Shi kuma yace abunda zai kaisa kaduna an daga sai wani sati.
Da Assadiq ya gayamin sai nace zan kira Adda Rukayya na gayamata Amna ta shirya sai ta jira Tahir din Sati mai zuwa ya biya ya Daukota.
Haka muka yi dole tunda ba wanda zai Taho da ita, Assadiq ya gayama tahir yace ba matsala ta zo gidan Adda Fati tunda yasan gidan sai ya Biya ya Daukota.
Yanzu tsakanina da Tahir sai gaisuwan mutumci da girmamawa Sannan zumunci na ke yi da Hauwa'u sosai kamar mun zama yan'uwa.
Allah ya taimake ni a satin Safiya ta kirani tace ta raka Mamansu Abuja bikin diyar kanwarta sun kawo Amarya nan cikin garin Abuja.
Tace ta na so tazo sai naji dad'i daman tasan bani da lafiya nan ta ke na Tura mata Address ba dad'ewa sai gata.
Ta yi jimamin halin da ta ganni, duk na tsumaye na rame kamar ba ni ba sai Farin Fata da ido.
Gabadaya kananun jikina