Showing 63001 words to 66000 words out of 116366 words

Chapter 22 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

320

saka kun zata karbi nata Hukuncin daidai da abunda ta aikata."
Zasu fara magiya yace su tashi su bar masa falo.
Shi daman Sadiq yana gama mganarsa ya fita ransa bace.

Suka tashi suna sharan kwallah suka Fice, suna fita Umma ta kalli Abba tana fadin"Abban Siyama ai ba laifi ba ne domin na saka an kori wannan bakar Annobar, wacce ta so ka kashe mana d'a daya Tilo namiji da muka Haifa"
Ko kallonta Abba bai yi ba taga ya Dauki waya ya na Dannawa ba ta ankara ba sai da taji suna gaisawa da Mallam zakari ta Rude.
Tana rokonsa da ido da Hannu ammh Abba ya yi kamar bai ji ba.
Ya kwashe duk abunda ta aikata ya sanar ma da mallam zakari.
Dagacan bangaren ransa ya baci cikin Fushi ya fara magana Abba na jin haka ya saka mata a amsa kuwwa.
Cikin ba da Umarni Mallam zakari yace"Sulaimanu ka fattake ta daga gidanka Tunda Salamatu ta zama zakka, ni kuma ka sanar da ita Tunda ni Uban banza nake gareta ta bid'i wani gidan Uban ba dai nau gidan ba ka hid'i mata haka Tunda Shawaran ki uwa take mara lissafi."
Abba ya kalleta alamun kinjin dai ko sannan yace ai tana jinsa.
Nan yace a bata waya ya yi ta bacinta Umma tana kuka tana bashi Hakuri ya kashe wayarsa.
Abba kuma ya karbi wayarsa ya mike yana fadin"Bazan kore ki ba, ammh ki sani itace damarki ta karshe, nagaji da d'aga miki kafa salamatu."
Daga haka ya tashi ya bata waje, Sai ga Umma da kuka har shashenta.
Su Sajida da suka zauna ta dawo su kara zugata sai kuma suma suka ga ba Dama.
Sultana dai suka gama zaunarwa suna kara zugata, Umma kam ciki dakinta ta shiga ta maida kofa.
Me ta saka me ta saka oho, ta ga dai bata da mafita su Sajida ma bata san tafiyarsu ba.
Tun safe ta je bangaren Abba bayan Mama ta koma shashenta ta Durkusa ta na bashi Hakuri shi kuma yace bakomai.
Fatansa ta sakama auran magajin gida albarka sannan ta maida masa matarsa tace duka zatayi.
Daga karshe yace bayan suna taje taga Jikokinta ta yi ma matar Sadiq barka taje to.
Ta rokesa ya kira Mallam Zakari yace masa ta bashi hakuri, shi kuma yace sai in yaga da gaske ta ke yi hakurin da ta bashi Sannan zai kirashi ya gayamasa.
Tana komawa bangaranta ta kira Sajida da Sadiya da Sa'adatu tace su shirya suje Zariya suna.
Sannan ta kira Surayya tace ta zo gida tana nemanta.
Daman kuma Surayyan zata Biyo Tunda Abba yace har da Mutanen shinkafi za su tafi Sakeena ta kira ta tace itama zata je.
Ta d'an bata Lokaci tunda ta siya wasu kaya aka kawo mata daga kasuwa, Suba'atu da Saddiqq sun turo kudi a siya ma maijego kaya ita da Twins.
Ta yi mamaki da ta zo Umma na bata Hakurin ta jira sauran yan'uwanta su tafi tare, sai ba ta ja ba tace su yi sauri saboda kada su yi dare kuma sai Gobe za su dawo.
Bata gama mamaki ba sai da Sadiq ya Shigo Umma ta yi masa Barka da kuma saka albarka ya amsa bakinsa har Kunne yaci fararan kaya ya Fito sak angon karni karni.

Kuma nan ta ke Umma ke tambayansa bayan suna Sulatana zata koma dakinta kafin dai ya koma wajen aiki.
Shi yace duk yadda ta yanke daidai ne a wajensa.
Sai dai bai yi kasa a gwiwa ba ya kalli Umma yana fadin"Ita Sultanan na son komawa da gaske?
Umma tace"Eh mana, ni ce daman na hana kuma yanzu na saki Allah ya baku zaman lafiya gabadayan ku."
Sai amswa ya ke da Ameen yana mamakin Umma.
Ita kuma Surayya sai take ganin kamar Umma ta yi sanyi ne na d'an Lokaci.
Saboda jiram su Sajida sai sha Biyu na rana suka tafi tashar Sharon suka yi gabadayan su, Mama bata samu zuwa ba diyar kanwarta ta rasu, Siyama ma bata je ba suna da Jarabawa.
Sakeena ce kad'ai a dakin mama sai Sajida Sadiya, Sa'adatu bata samu zuwa ba wai mijinta ya hanata.
Surayya sai su Goggo Hassu sai Hajiya Innani.

Ba su isa ba sai karfe uku saura na Rana koda suka isa gidan suna ya Tumbatsa da Mutane.
Gida cike fa, nan suka iske Saleema sun zo tun safe daman ta yi ta kiran su sukace suna hanya
Saukar ban girma aka yi musu daman Tunda an sam suna hanya an tanadar musu nasu abincin na musammam.
Shinkafa jallop da alala har da nama sai kunin aya da Zobo.
Ni da kaina nazo har falo muka gaisa na kuma saka Ramatu da Safiya suka kai mu su yaran.
Sun zo sun samu har anyaka Raguna Uku,har an gyara su ma tunda za'a soya da wuri a ba su nasu su tafi da shi.
Sun sameni na yi kunshi sannan na yi kitso, kuma sun iske ni da wata Atamfa da muka yi anko da su Adda Fati har da Ramatu da Safiya.
Na saka less ma da Safe Cikin kudin da Assadiq ya Turomin na siya.
Sannan Maman suhailat ta bani materila na dinka shi shima.
Sai Anty Surayya ta bani leda shake da kaya, akwai dinkakku da wad'anda ba'a dinka ba sai na jarirai da su pamparrs da sabulan wanka tace daga gare su ne.
Turmin Atamfa yafi goma leshi guda Biyu har da mayafai da Hijabai, kayan yaran ma masu kyau da su fin kala goma, kuma damam an kara siya musu wasu, Ramatu da Safiya duk sun gwangwaje ya'yan na su da kayan yara har da takalma da safuna masu kyau.

Su Adda na nuna mawa suna ta Godiya, taro ya yi armashi Sosai duka matan Baba saminu da na Baba Tanko duk sun zo min, su salima da la'asar suka dauki hanyar kaduna.
Ita man jiki ta kawomin na yara Hajiya Murjanatu kuma ta aikomin da Atamfa da kayan yara Fathihatu kuma ta bani kudi.
Kai hatta yan gidanmu ma samaru sun kawo sabulai, Ummi ma tazo ta kawomin kayan yara har Fadila sai gata tazo min suna tare da Ummin suka zo, na kuma san harda gulma ya kawota.
Saboda gidan ya yi kad'an ga baki yasa Adda Fati ta Shiga makotan ta inda suke mutunci gidan maman hanna ta roka aka kai su Anty Surayya can suka kwana da Sassafe kuma aka tashi da aikin suya nama Saboda sun ce da wuri za su kama Hanya.
Sai da Safen ne Sajida da Sadiya suka shiga har dakin da na ke Lokacin mun dawo wanka ni da Inna Talatu.
Ita fita ta yi ta bamu waje, suka nemi gafarata nace musu ya wuce.
Sannan suka bani wayata da Key din dakina tare da Atm din bankina.
Sadiya ce ke sakin Fuska Sajida kuma tunda tace na yi hakuri ta kauda Fuska ni kuma na nuna musu komai ai ya wuce ni dai Tunda suka barni da dan'uwansu ai sun gama min komai.
Misalin sha Biyu na rana suka tafi, Suka bar mim Innani kamar yadda Assadiq yace ta na ko kamkame da ya'yan magajin gida ta bakinta.
Ta dankgwali Hancin wancan tace sulaimanu, sai ta dangwali hancin wancan tace muhammadu, ba ruwanta ita fa Imnani in za'a zauna ta yi ta Hira ba'a gwasaleta shikenan su Adda na shan Labaran su Assadiq da Abba.
kuma ba sakaya komai da komai ta ke fad'a ni dai ina Ta tsoron kada ta je ta fad'i abunda ya faru tsakanina da su Sajida sai kuma aka ci sa'a Hirarta bai kaita can ba.
An diba musu nama da yawa sun tafi da shi, Amma na Abba dabam na Assadiq ma dabam, sai kuma na Umma shima Dabam na su ne aka had'a waje d'aya.
Naji dadin zuwan su kuma hakan ya kara tabbatar min da cewa da gaske ne Assadiq na sona kuma ya Tsayamin.
Su Adda kuma suna ta Hiran sun fara Saukowa, suna ta kuma bani shawarwarin yadda zan kara jawo su gareni a sannu ko Saboda yan yaran nan.
Ni dai jin su kawai na ke yi, zan yi dai iya bakin kokarina ammh ba lalle ne na Burge wasu daga cikin su ba.
Ni dai na sakama raina zan zauna da Assadiq cikin Amana na yi masa Biyayya har karshen Rayuwata.
Saboda ya yi min komai a Rayuwata ko nace ya na kan yi mini mana.








*Janafty*
*TMWB3K013*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65

Kamar yadda Umma ta fad'a ashe da gaske take yi, bayan suna da kwana uku ta shirya Sultana ta maidata gidan mijinta duk da sultanan na ta koke koken ita bazata koma ba sai ta gama Jarabawarta gabadaya Umma tace bata isa ba.
Daga Sadiq har Abba suna mai Farincikin ganin Sauyawar Umma, Ko naman suna da yaji da su Anty Surayya suka kawo mata da girmamawa ta Karb'a ta na saka albarka su Sajida ma suna kokarin kawo mata wata mgana a gaban Surayya ta ja musu kunnen bata so, sannan ta na basu Umarnin su shirya da Dan'uwan su bata son ta kara jin wata mgana.
A lokacin Sadiya sai ta kada baki tace"Umma mu kenan zamu bisa muna yi masa mgana! Yaron da ya fara gaba damu?
Umma tace"Eh ku bi shi ku yi masa mgana ku basa hakuri, ai durkusa ma wada ba gajiyawa ba ne."
Da haka ta kashe bakinsu kuma Sai suka yi girman kai ba su ba shi Hakurin ba, shi kuma bai kara bi ta kansu ba tunda dai Siya ta gayamasa sun je sun bata Hakuri kuma sun dawo mata da abunda suka karb'a.
Umma bata nemi Rakiyar kowa ba sanda zata maida Sultana domin ko mutanem shinkafi tun jiya da Safe suka koma gidajensu Mama kuma tana gidan Gaisuwa.
Sai da suka isa gidan ne ta saka Sultana ta zage itama ta tayata suka gyara gidan gabadaya ta kuma sakata ta Dauki waya ta kira Sadiq tace masa ta dawo tana Bukatar Cefane zata yi girki.
A lokacin baki ta tura kafin tace"Umma ni fa baya kirana, ko mgana ma ba ya yi min indan ya ganni."
Sai idanuwanta suka ciko da kwallah Tausayinta ya kama Umma sai dai bata nuna ba cikin ba ta Umarni tace"Maza ki kirasa, Umarni na ke baki ba shawara na zauna ina yi da ke ba."
Dole kanwar naki ta kira Yaya Sadiq da ta manta rabon da su yi mgana ta waya.
Kiran har ya katse bai dauka ba ta kalli Umma a marairaice tana fadin"Kin gani ko Umma bai Dauki Kirana ba, ni fa daman baya sona Hankalinsa na kan bazawarar matarsa da ta haifa masa ya'ya."
Umma ta yi mata banza kamar bata ji ta ba, in da Sultana tasan yadda ta ke ji acikin ranta da bata kara harzuka ta ba.
Duk lakwas din data ga tayi gani tayi Sadiq da Ubansa suna neman su saka Mahaifinta ya yi mata Mugun baki Saboda wata bakar Annoba, shiyasa ta yanke Shawaran gwara ta sauya taku.

Ba abunda yafi bakanta mata rai sai ganin yadda Sadiq ke faman rawan kafa akan yarinyar nan da ya'yan da ta Haifa bashi kadai ba hadda Abban Siyama, sannan uwa uba ga Innani can ta je ta tare a gidan su yarinyar, shiyasa ta yanke shawaran gwara Sultana ta dawo da ita zata yi amfani ta fitar da yarinyar nan har Abada daga Rayuwar Sadiq tunda a baya ta kokarta bata samu nasara ba
Sannan itama Sultanan ta samu ciki ta Haihu shime yanzu babban Burinta.
Tana cikin wannan Tunanin har Sadiq ya Biyo bayan kiran Sultana muryan nasa a cunkushe kamar an yi masa Dole, yace wayar na silent ne bai ga kiranta ba sai daga baya.
Itama cikin Dage baki ta gayamasa wai Umma tace ya siyo Cefane.
Umma kamar ta maketa haka taji da Sauri ta karb'i wayar suka gaisa shi daman Abba ya fad'a masa Umma yau tace masa zata maida Sultana gidanta duk wannan Murnan da ya ke ji a baya na kasancewa da sultana ya kasa jinsa a wannan Lokacin.

Shifa tunda ya Fahimci yarinyar bata da kunya ya gane ta su bazata taba zuwa d'aya ba kawai ta na cin Darajan masu daraja ne shiyasa
Cikin Sauya mgana Umma tace"Kyale Sultana da Sakarci cewa tayi ta na so ta yi maka girki kuma ba Cefane sai nace to ta kiraka ta fad'a maka mana."
Yana kwance ne yasa ya gyara kwanciyarsa yana fad'in"Shikenan Umma dame dame ake bukata sai na je a siyo?
Cikin jin dadi Umma tace"Komai fa babu na Cefane, kuma kai da baka gama Jinya ba?
Mirmishi kawai ya yi kafin yace"Na warke Umma, na ma kusa komawa aikina in sha Allahu."
Jin haka yasa Umma ta fara yi masa addu'an tsarewa tare da Fatan nasara sun rabu tace anjuma yazo tana so ta yi mgana da shi tare da Sultana gabadaya yace mata toh.
Kasala ce ta Rufesa a lokacin domin ba su jima da gama waya da Siya ba itama Gobe zata koma gidanta tare da Inna Talatu da zata Zauna da ita.
Ya na Tunanin ya Tura mata itama kudin da za su yi Cefane duk da tace masa aikwai kayan abinci za su isa har yazo garin.
Hakanan ya mike ya sauya kaya, yasan in bai je da kansa ba sai Umma ta rike sa a ransa.

Saboda kafarsa da bata gama dawowa daidai ba, bai yo siyayyar da yawa ba kayan miya ya siya sai nama da kifi sai kayan lambu da Ruwa tare da lemu, kuma ba shi yaje ya kai ba Mallam tajudeen ya roka shi yaje ya kai ma su Umma sakon ya dawo.
Umma da kanta ta taya Sultana girki mai rai da lafiya.
Farar shinkafa da miyar naman Rago sai cowslow da suka had'a bayan sun gama ta saka Sultana ta tsala wanka da kwalliya ta na tashin kamshi.
Umma ta yi ta kuranta da cewa ta yi kyau ita kuma Fuskar Sultana ba Fara'a.
Dalilin da yasa Umma ta jata suka zauna bakin gado lokaci d'aya tana fadin"ko ke fa? Kin ganki kuwa?
Sultana ta wani kara bata rai, sai Umma ta yi mirmishi kafin ta gyara zama tana fadin"Na lura in ban yi miki bayani ba, zaki iya bani matsala gashi ni kuma a yanzu ke ce Makamina."
Cikin mamaki sultana tace"Bangane ba Umma?
Umma ta gyara zama ta na kara Fuskantar Sultana Lokaci d'aya ta na fadin"Saboda Matar nan ta Sadiq bakar Annoba Mahaifina ke neman yi min baki, sun  kasa Fahimtar abunda na ke so su Fahimta a dole sai na saka ma auransa da wannan Shegiyar yarinya albarka ni kuma na Tsaneta kasancewarta ita da d'ana a waje daya matsala ne, Shiyasa na nuna musu na Hakura komai ya wuce, yanzu haka nace Sadiq ma zamu je Zariyan na yi barka naga yaran saboda su kara aminta dani. Ke kuma daga bangarenki ki yi amfani da kissa da kissina ki na y'a mace ki san yadda zaki yi ki hana ta jin Dadinsa har daga karshe ma ki Raba su, sannan kema ki yi kokarin ki samu Ciki ki haihu sai naga zuciyar wa zata kama saboda Ta haifi yan Biyu."
Sultana ta yi shuru kafin tace"Kamar kin sani Umma, ni kaina yanzu bani da wani buri sai na ganin nima na Haihu kuma nima yan Biyu na ke son na Haifa Umma."
Ta karishe kamar zata yi kuka, Umma tace"Da ikon Allah ke yan uku zaki Haifamana ita din banza, shiyasa na ke so ki kwantar da Hankalinki zamu rika waya ina tsara miki wasu abubuwan, ni yanzu in nace zan kara yin wani abu ido na kaina sai mgana ta kara zuwa kunnen mallam kuma ya yi min gargadi a ka sake kawo masa karana wlh sai ya bace ni fiye da Tunanina, ni kuma na samu Dakyar na kira shi na bashi Hakuri shiyasa ke na ke son ki natsu ki bar mganar zafin kishin nan ki Tsaya ki kwace shi daga wajenta."
Sultana tace" anya Umma zan iyaa? Kina ganin yadda Yaya Sadiq baya ji kuma baya gani a kan matar nan fa."
Idanuwamta suka tara kwallah ta Cigaba da fadin"Ita ya ke so, ni ai matar chuse ce ba ni da Daraja a wajensa."
Umma tace"In ji waye? Yana sonki mana in da baya sonki da bai amince da auranki bayan ya aureta ba."
Sultana ta kalli Umma cikin wani yanayi tace"Umma ni fa ina jin haushin ace itace gaba dani, Mayar kwacen miji kowa ai yasan Yaya Sadiq nawa ne ni kad'ai."
Sai hawaye Umma na faman share mata ta na fadin"Kada wannan ya dameki ni a wajena bayan ke ba wata mata a gidan Sadiq, ki kwantar da Hankali da sannu zata fahimci karatun kurma."
Da wad'anan kalaman Umma ta yi ta lallashin Sultana har ta samu ta yi shuru kuma ta yarda da Shawaran Umma.

Sallar isha'i suka tashi suka yi, Abba ma ya yi mamakin da ya dawo gida ya iske bata dawo ba tana tare da Sultana har alokacin
Da ya kirata cikin Dariya tace Sadiq ta ke jira yazo ta had'a su ta yi musu nasiha sannan sai ta taho.
Shi har acikin ransa ya ke ganin Sauyawar Umma, tunda yasanta ko a baya da Tunani tare da hangen nesa kuma bai taba kamata da laifi irin wannan ba, shiyasa ta yi ta abubuwa shi kuma yana yi mata uzuri.
Umma ta gaji da jiran Sadiq har wajen tara kuma tana so ta koma gida sai ta saka Sultana ta kara kiranshi sai yace yana kan hanya.
Sanda ya shigo falon kallo d'aya ya yi ma Sultana ya kauda kansa ya maida wajen Umma.
Ita kuma Umma ta hau take mata kafa Shiyasa ta mike ta isa gabansa tana yi masa sannu da zuwa.
Ya kalleta sama sama sannan ya amsa yana karisawa kusa da Umma.
Cikin Ladabi ya gaisheta, ta amsa cikin Fara'a ta na kara tambayansa kafarsa yace ta kusa warkewa gabadaya Tunda yanzu ya daina yawo da taimakon Sanda.
Shine ma yake gayamata zai koma asibiti litini mai zuwa yaga likita.
Umma tace yakamata yaje a kara ganinsa.
Suna mganar nan Sultana taje ta kawo masa Ruwa Umma na ta faman mirmishi ta na fadin"ina ruwan Sultana."
Shi dai kanzil bai ce ba ya dai Dauki Ruwan da ta zuba masa ya sha Saboda kada ya kwabe kokarinta a gaban Umma.
Ganin Sultana zata shige Ciki kamar gaske Umma ta kirata ta dawo gabanta ta zauna.

Umma ta gyara zama ta yi musu nasiha sosai, ita Sultana aka ce ta yi ma mijinta Biyayya. Sannan kada taji ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login