Showing 18001 words to 21000 words out of 116366 words

Chapter 7 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

307

damu ki yarda dani."
Sai na kasa musa mata, wayarta ta Dauka ta yi danne danne.
Sannan ta Dago ta na kallona kafin tace"Na kira ki da lambata, ki adanata zan kira ki in sha Allahu."
Sai na bi ta da kallon mamaki ina ta samu lambata?

Kamar ta sani sai ta fara min bayanin ta inda suga hoton da komai.
Surayya ta ce"bamu sha wani wahalan gane gidan ba, tunda baya cikin lungu, sai dai mun shiga wani gida achan baya matar gidan ne tace mu zo nan ta na Tunanin ke ce'"
Sai na kasa mgana ina kara jin Tsoron Rayuwa zaton abunda ba ka yi zato ba.
Ko ni bansan Safiya ta Tura wannan Hoton ba, sannan bani da masaniyar yayarta khairiya na mu'amala da Daya daga cikin yan'uwan Assadiq.
Surayya ce kad'ai ta sha ruwa  har na samu karfin halin cewa zan musu girki tace za su tafi ne ba wanda yasan sun yi wannan tafiyar.
Har ga Allah sai naji Surayya ta Burgeni baki ta ke ta bani ta na lallashina akan na daina kuka ko Damuwa ta na da tabbacin Komai zai zo da sauki na kwantar da Hankalina Sajida ko da mun had'a ido sai ta harareni da kallon Tsana, daman nasan ba kowa ne zai karbi mganata ba, zan Fuskanci tarin kalubale.
Tun ballatana da za su tafi, surayya ta rike hannayena ta na kallon cikin Idanuwana tace"Ki kwantar da Hankalinki Asiya, ba bu abunda zai Faru Sadiq kanina ne kuma Favorite d'ina, ya na ji dani, nima kuma ina ji da shi, kaf gidanmu ba shi da abokiyar shawara kamata, na yi mamakin da bai iya sanar da ni labarin ki ba, na yi masa uzurin Halinsa ne na Taimakon wanda ke neman taimako sai dai bazan taba masa uzurin boye mana wannan gagrumin abun ba, Tunda abu ne da ya shafi aure da Rayuwa gabadaya,so ki kwantar da Hankali komai zai wuce in sha Allahu."
Sai naji hawaye sun cikamin kwarmin Idanuwana, na fara yi mata godiya tace min bakomai.
Sannan ta yi ta jadaddamin na cire damuwa har ta na zolayata akan ina Dauke da Bbyn su, kada na yi musu asara sai ga shi ina Dariya.
Sajida ko ta fita mota, saboda ta kasa zama gani ta ke yi kamar kunnuwan Surayya Hala sun toshene da ta tsaya tana Saurarena kuma har ta na Neman Goyen bayana.
Suna tafiya na koma falo na zauna kan kujera, na saki kuka  ta wani bangaren in na duba Surayya sai naji kamar na samu salama, ta wani Fannin kuma in na Tuna ire iren su Sajida sai naji na Raunana, na Shiga uku ina zan saka kaina in har Assadiq ya rabu da ni? Na tabbata Rayuwata sai ta fi baya kuntata matukar haka ya faru.

Surayya da Sajida a kan hanyarsu ta komawa Gusai, Direba na gidan gaba ya na Tuki su kuma suna gidan Baya, Surayya ko mijinta bata gayama gaskiya ba,  Sai cewa ta yi Umma ce ta aiketa Sajida kuma zata rakata.
Kowannensu ya yi Shuru zuciyarsu na saka musu tunani iri iri.
Surayya tunaninta ya zurfafa sannan ba irin na kowa ba ne, Damuwarta daya ne yadda su Umma za su Karb'i mganar uwa uba kuma Innani tasan akwai babban kalubale, ballatana su san Labarin Hasiya, sannan ta ga alamun za su kyamaceta jin ita bazawara ce, sannan ga Sultana bata san ta ina zasu Karb'i mganar ba.
Ba ta jin Abba shi ya na da Saukin kai, Umma ce abun ji saboda ba lalle ta yarda da abunda zataji ko zata gani ba.
Sadiq ya yi kuskure kuma ya zama Dole a nuna masa rashin kyautawarsa, sai a yanzu abubuwa ke dawowa kanta daki daki ta tuna yadda aka sha fama da shi kan auran Sultana tun a wanchan lokaci ashe ashe ya na dalilinsa, daman ita fa ta yi wannan Hasashen na cewa akwai wani abu a zariyan nan da ya ke Dauke ma Assadiq Hankali, ta kira Tahir ta tambayeshi ya yi mata karya shima, ta na mamakin Wayau Sadiq har ya iya yin aure a boye ya kama ma matar haya suna zaune tare, har tsawon wannan Lokacin ba wanda ya sani abun a jinjina masa ne.

A gefe daya kuma na zuciyarta tausayin Hasiya ya darsun mata, Ba laifinta ba ne ammh sai ga shi ta na Shiga gagarin rayuwa saboda hakan, sannan har itama Sadiq ya yaudareta Don ma zuciyar macece da Rauni Sannan Tsskanin mata da miji sai Allah, ammh ai ko ta barayin hanata Haihuwa yaci Amanarta, ammh ko ma menene Allah ya nuna isharansa shi ya Kulla auran su, kuma shi ya nuna cewa akwai zuru'a a tsakaninsu.
Tunanin ta ya na tafiya ne kan yadda zata iya gayama Umma da Abba wannan Labarin.
Ba Sadiq zata taimaka ba, Hasiya ce wacce taji matukar Tausayinta ta na cikin wani Halin da ta ke Bukatar taimako, Sadiq kuma chan ya karata Shi da ya kira ruwa shi ruwa zai Cinye, zata dai Tsaya tsayin daka ta ga an yi ma Hasiya adalci ko domin cikin Sadiq da ke jikinta.

Ammh tabbas sai ya karb'i Hukuncin abunda ya aikata, sai ya gane ba shi da wayau bazata yarda ta karesa ba, Gwara ya gane kuskurensa nan gaba bazai kara gigin aikata haka ba.
Sajida ko acikin ranta ta gama kissima, irin yadda zata zuga Umma da Innani, in sha Allahu wannan bakar Annobar bazata zauna acikin zuru'arau ba.
Sadiq kuma ta zageshi a ranta bata san iyakata ba, Shege bata san Uban me ya gani a jikin wannan yarinyar ba farinta kamar na ma su cuta, ta gama tsara har Sultana sai taji mganar nan kuma zata zugata tace bazata zauna da Sadiq ba sai ya saki wannan Annobar.
Surayya kamar tasan Tunanin Sajida ta kalleta ta na fadin"Sajida kada naji mganar zuwan mu zariya a bakin kowa, Saddiqa kawai zata ji itama Saboda tasan mganar ne, ammh ban da Labarin Rayuwar Hasiya na baya Sajida ko a gida bazan fad'a ma su Umma canfin karyan nan da mutane ke yi a kanta ba, domin ni kaina ban yarda ba, sai dai ba laifin in sun ji cewa a bazawara ya aureta."

Sajida ta kalleta Sheke sheke kafin tace"Meyasa ba za su san abunda Sadiq ya kawo mana cikin zuru'a ba?
Big sis ki yi hakuri duka sai na karanta ma yan'uwa da su Umma gwara su san abunda ke Faruwa, kina fa ji da bakinta tace duk wanda ta aura ko rasa dukiya ko rasa lafiya, Sadiq kadai ne garemu namiji in wani abu ya same shi ba? kuma mun sani muka Boye wlh Allah bazai barmu ba, ni dai ba Ruwana bazan iya Boye wannan mganar ba ki yi hakuri."
Sai Surayya ta kasa mgana ta na kallon Sajida jin ta kara cewa"Kuma banda Sadiq ya yi asara me zai ci da auran bazawara? Bazawaran ma wacce ta yi aure Har biyu, abun takaicin ma  kuma yasan komai a kanta ammh kuma ya aureta a haka ba da sanin iyayensa  ba Dan Burauba ai ya yi asara wlh, ina sultana zata had'u da wannnan matar? Fatar jikinta kamar na mayu, har ga Allah ban ga abun so a jikinta ba sai wauta irin ta Sadiq."
Ran Surayya ya baci da Sauri tace"Ya isa Sajida, kar ki Rufa asirin kin Dad'e baki Tona ba, ammh ki saani wanda ya Rufa ma wani asiri shima Allah zai Rufa masa asiri ranar gobe kiyama, kuma da ki ke mganar bazawara kina Zagin dan'uwan ki, kin san adadin ladan da ya samu akan haka? Ba zaman bariki ya ke yi da ita ba Matar aurensa ce da shaidu suka shaida auran su, kinga kuwa ko wannan kadai ya isa ki yi salama ki kuma jinjina hikimar Ubangiji"
Sajida ta kyabe baki kafin tace"Daman Tun a dazun na Fuskanci zaki goyama Sadiq da yarinyar nan baya kamar yadda kika saba tsaya masa, ammh ina so ki sani ko Umma bazata taba karb'an wannan yarinyar da abunda ke Cikinta ba."

Surayya tace"Ni ba su zan tsayama ba, Ina bayan gaskiya ne, domin ita ba namu ba ne hakan baya nufin bazamu yi mata adalci ba, itama in zamu kalli abunda ta Fuskar adalci ya yaudareta kamar yadda mu ma ya yaudaremu, maganar Annoba da kike fad'i ki bari Allah ne ya Halliceta tare da kaddaranta ki daina Dariyann rayuwarta ke kuma kina alfahari da naki Rayuwar, mganar bazawara kuma kada ki zama Jahila Sajida, da ilimin ki da komai, ki ke so ki kawo wani karatu na banza wani nafsin ne yace ita bazawara ba Mutum ba ne? Ko kuma akace Saurayi ba zai iya auran bazawara ba? Kin manta da Labarin Annabi ne da Nana khadija? Ashe ko in da shi mu ke ko yi, mu al'ummarsa bamu isa mu kyamaci bazawara ba."
Sai ta yi shuru ta dakata, ta na lura da Sajida da ta koma ba ma yaronta Nono, kanta na gefe kamar maganar na Surayya ta na shiga ne ta na fita.

Ganin haka yasa Surayya ta Had'e rai kafin ta cigaba da fadin"kuma da ki ke mganar Umma bazata amince ba, daman bukatar shi ne a bi kadin auran a tabbatar da auran na gaskiya ne, bayan wannan ruwan kowa ne ya karb'i Asiya ko kada ya karb'eta ammh baku isa ku sauya wannan mganar na cewa itace Matar Sadiq ta farko, sannan har Abada ita din iyalinsa kinga shaida ma, tunda ga ciki kin gani a jikinta,ni bazan kara miki magiyan ki kama bakin ki ba, ammh ina so ki sani, ita Rayuwa ta na da Fad'i, kila watarana Asiya zata iya miki wani amfani ta fanni da baki zata ba, ko da ki ke ganin kin rainata."
Daga haka ta kama bakinta, ta koma ta na kallon tagar gefenta ta na ganin Dajukam da suke wucewa.
Sajida kuma ko a ranta ba ta ji zata iya Rufe wannan mganar ba, kuma har acikin ranta bata hango Sadiq ya cigaba da zama da wannan yarinyar ba.
Ta na jin Surayya na magana da Saddiqa ta na kara bata tabbacin da gaske ne Hasiya matar Sadiq ne ita ya fara aura a boye kafin ya auri Sultana, Dagachan Bangaren Saddiqa ta na ta salati, Sai dai surayya tace ta bari su koma gida za su tattauna yadda za su tari su Abba da mganar, ammh ko ita tace kada sauran su ji tukunna dai.
Wajen la'asar suka isa Gusai, har gida Surayya suka kai Sajida sannan Suka wuce gidanta.
Daren ranar ta kwana Tunanim mafitan yadda zata kai mganar nan gida ta kasa, wazhegari da Safe sai ga kiran Sadiq bayan ta Dauka sun gaisa bata nuna masa komai ba.
Sai yace zai shigo wannan Satin in ta na Free akwai mganar da za su yi.
Sai Surayya ta zargi ko daman shine maganar da ya kasa fad'a mata?
Sai ya ba ta Tausayi, da Sauri tace"Ina nan Sadiq, wannan wani irin mganace tun yaushe ka ke cewa zamu yita, ka kasa kuma fad'amin? Ina fatan dai lafiya ko?
Dagachan Bangaren Sadiq ya yi shuru kafin yace"Sai dai na zo big sis, ina fatan zaki fahimceni kamar yadda kika saba Fahimtata a baya."
Sai kawai Surayya taji kwalla ta cika Idanuwamta, sai tace ta na tsumayinsa.

Shi kuma a satin Zariya ya kamata yaje, ammh ya riga ya yi kudurin Fad'ama surayya komai a kan Hasiya, sai ya kirata yace ta yi masa Hakuri yaje Gusai kan mganarta.
Ni kaina ya na gayamin ina share kwallah, bazan iya gayamasa ya yi jinkiri ba, ballatana na sanar da shi abunda ya ke so yaje ya fad'a sun san da shi kafin shi ya Furta musu.
Alkwarin da na yi ma Surayya na bazan fad'a masa komai ba yasa na kasa gayamasa komai.
Sai dai ina ta addu'an Allah yasa koma me zai Faru ya zo da sauki.
Sadiq yaje gusai, ammh kana ganinsa wani sukusuku, Sultana duk yadda ta Shiryamasa Tarba ya kasa sakin jiki, kuma har ita kanta bai wani yi mata rawan jiki da ya kan yi in ya zo ba.
A daran jumma'an duk yadda ta so su kad'aice bai biye mata ba, sai yace mata baya jin dadi, washegari kuma da Safe yaje gaida su Umma.
Ita kanta Ta Fahimci ya rage walwala ta tambayesa ko lafiya? Sai yace gajiyan aiki ne.
Abba ma sai da yace ko ya yi ciwo ne?Sai yace a'a, Abba kai Tsaye yace yaga ya rame ne, kuma ya rage walwala.
Sai ya kasa mgana, Daga Shashen Innani gidan Surayya yaje, sai dai duk kokarinsa da mganganun da ya gama Tsarawa ya kasa fad'a ma Surayya su  kuma bayan ita ba shi da wani Sauran Hope.
Zaune kawai ya yi tsuru a gabanta, ya kasa magana ya rasa ta ina ma zai fara, duk abunda ya shirya ganinsa gaban Surayya sai yaji komai kamar an shafe masa daga kwakwalwarsa.
Surayya ta kallesa shuru ta na nazarinsa, kafin tace"Sadiq me ke faruwa ne? Tun dazu ka yi shuru ka kasa mgana?
Sadiq ya runtse ido sannan ya Bude ya kasa had'a ido da ita, cikin jin nauyi da kunya yace"Big sis na rasa ta ina zan fara ne"
Da sauri tace"Ka fara ko ta ina Sadiq, zan fahimce ka."
Ta fad'a ta na fatan ya fad'a mata da bakinsa.
Ammh Sadiq ya kasa, ce mata kawai ya ke yi"Big sis na yi muku Laifi, a lokacin wlh zuciyata ba ta ganin komai sai na taimako, ku yafe min."
Surayya ta kallesa kafin tace"Me ya faru? Ka gayamin don Allah"
A gefe daya kuma daga shi har Hasiya suka bata Tausayi domin ta hango Tsaka mai wuyar da za su shiga.
Ammh abun Takaici Sadiq tafiya ya yi, batare da iya gayama Surayya komai ba, ya dai ce kawai yaci amanarsu su yafe masa.
Kasa fad'a mata ya yi, yace zai dawo gobe ya na tafiya sai ga  wayar Saddiqa, Surayya ta karanta mata yadda suka yi da Sadiq.
Saddiq tace"Wayyo Sadiq ya shiga Tsaka mai wuya, ni kaina ina fatan su Umma su Fahimcesa."
Surayya ta so ta kara Turke Sadiq in ya gayamata sai ta gayamasa komai ta kuma nuna masa kuskurensa ta yi masa adalci bisa gayamata da ya yi.
Ammh sai me? Ta yi ta kiran wayarsa bata samu sai ta kira Sultana, ita ke gayamata ya tafi zariya yau da safe dagachan zai wuce Abuja.
Surayya ta sauke numfashi, Sadiq me yasa ya ke haka ne?
Wannan fa gudun nasa ba mafita ba ne.
A ranar ta gama yanke shawaran abunda zata yi, ya kamata zuwa yanzu su Umma su san abunda ke faruwa.
Ba sai na nesa sun zo ba, ko da iya na kusa ne sun wadatar, Saddiq ta kira suka yi mgana, ta tabbatar mata da zuwa Jibi zata zo sai su taru su sanar da ma su Umma komai cikin Rukuni. Ba ta yi ta kan Sajida ba
ta lura so ta ke yi ta b'ata al'amarin to gwara tun kafin ta bata lamarin ita ta warware komai.
Sun rabu da Saddiqa akan Surayya zata Tura ma Hasiya Direba gobe ko jibin ya kawota gidanta ta kwana ranar Laraba da zasu taru sai ta taho da ita hakan zai fi sauki.

Bata kirani a ranar ba sai Ranar Litini da safe, lokacin ina makaranta Assadiq ya saukeni ya wuce Abuja.
A yadda ya zo min na yarda cewa yan'uwansa ba su fasa mganar ba.
Ammh mun rabu bayan ya tabbatar min da cikin Satin nan zai fad'ama Ahalinsa komai game da ni.
Bayan mun gaisa kai Tsaye surayya tace"Sadiq ya tafi ko ya na nan?
Cikin jin nauyi nace"Dazu da safe ya wuce."
Sai tace"Ki shirya zuwa gobe zan aiko Direba zai taho da ke wajena, ki shirya kayanki kamar kala uuku haka"
Cikin wani yanayi nace"Ba matsala ko Anty Surayya?
Da sauri tace"In sha Allahu, zan kira ki in zai taho."
Daga haka muka rabu, a cikin raina sai nake jin wani Tsoro.
Tsoron abunda zan je na tarar, abu biyu ne ko su aminta dani ma zauna cikin Tozarci ko kuma su rab'a ni da Assadiq sun yi min koran wulakanci.
In hakan ko ya faru na lalace domim bansan kuma wani mafita zan kama ba.




*Janafty*
*TMWBK3005*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk

Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haɗin mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan.

Washegarin Talata Saddiqa ta baro Kebbi zuwa Gusau, kuma ita kad'ai tazo ba tare da yara ba tace saboda makaranta sai ta barsu a gida tare da Babansu.
Zuwan bazata tayi, tunda ko Umma sai dai ta ganta kwatsam gashi motar haya ta shigo ta sha wuya, ammh abun mamaki ta na isowa sallolin da suka Subuce mata ta fara rankawa kafin ta ci abinci.
Ta na gama cin abincin sallar mangariba tayi, tace ma Umma zata je gidan Surayyah abun sai ya ba ma Umma mamaki, ganin ko hutawa ba tayi ba, kuma tace zata fita.
Taga kuma ko shashen Mama bata je ba, ta dai Leka shashen innani sun gaisa gashi ma Abba bai dawo ba.

Umma ta kalli Saddiqa na waya da megidanta, tana nazarinta sai taga kamar zuwan nata ya sha bambam da zuwan da ta saba yi, daga gani tafiyar tazo ne babu shiri.
Jin kuma tace zata je wajen Surayya da Daren nan, sai gabanta ya fad'i ta fara Tunanin ko wani matsala ne ya faru da Surayyan ba su sani?
Tunda ta kwana Biyu bata leko su ba, Umman ce ma ta kirata shekaranjiya sai taji muryanta wani iri, da ta yi mata mgana sai tace bata jin dadi ne.
Saddiqa ce ta katse ma Umma Tunani da cewa"Umma bari naje, kada na yi dare na rasa abun hawa."
Umma ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa Surayyan ta na lafiya kuwa?  naga daga zuwan ki, baki huta ba kuma kin ce zaki tafi gidan Surayya"
Da sauri Saddiqa tace"Lafiya kalau fa, kawai ina so naje akwai mganar da zamu yi ne, kuma ba dadewa zan yi ba kila jibi zan koma."
Kamar Umma zata kara mgana sai kuma ta fasa, sai kawai ta ce "Allah ya kiyaye hanya, ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login