Showing 57001 words to 60000 words out of 116366 words
sai kuma yar'uwata Sister Zainab da ke aiki a asibitin.
Sadiq ya yi kwallar Tausayin Hasiya ciki har wajen wata sha daya yana jikinta bata haifeshi ba sai yanzu ga nauyin jiki ga na zuciya ga na lulura ga tashin hankali ammh ko alama bata zaunar da wani cikin yan'uwanta ta b'ata shi ko danginsa a wajensu ba, sai yaji matsayin da Siya ke da shi a baya yanzu ta na Hau hau sama da matsayinta na baya acikin zuciyarsa.
Kimanin awa uku sannan aka Samu nasaran fito da Ya'ya biyu duka maza acikin Hasiya yan biyu kosassu masu lafiya wad'anda ke kama sak da mahaifinsu sai dai Farar Fatar Hasiya kad'ai suka dauko.
Ita kuma ba ta farfado ba an kaita dakin Hutu.
Sadiq na gefe yana yi ma Allah kirari da godiya.
Tahir ya amshi yaron bayan su Adda sun gama ganinsu suna hamdala.
Adda Fati ta yi gefe ta kira Amma tana gayamata an yi ma Hasiya aiki an ciro mata yara maza guda biyu.
Amma sai farinciki da hamdala kuma daman ba su gayamata Hasiyar na naguda ba, kada su tada mata hankali.
Kamar Amma na wajen tace"Allah Sarki Ina shi megidan nata ya dawo kuwa?
Adda Fati tace"Ya zo a kan gaba Amma, shima ashe achan in da suke aiki hatsari ya samu."
Amma ta yi ta salati nan tace a bashi wayar shi kuma Lokacun yana gefen Tahir da ke nuna masa yaran shima bakinsa har kunne.
Adda ta mika masa waya tace ga Amma cikin ladabi ya karb'a ya gaisheta lokaci d'aya yana yi mata gaisuwan Adda Tunda Maman suhailat tace yayar mahaifiyarsu yasan Adda ce tunda shi dai ita kad'ai ya sani."
Amma ta amsa masa, itama ta yi masa jaje tare da barka da arziki sannan suka yi sallama ya mikama Adda Fati wayar.
Shi bai yi ta yaran ba sai da ya tambayi likita yanayin jikin matarsa ya tabbatar masa zuwa dare Hasiya zata Farfad'o cikin koshin lafiya.
Sannan ya karbi yaran hannun Tahir sun ci Kayan sanyi na yara masu kyau, Allah yasa Hasiya ta kwashi wasu daga cikin kayan haihuwanta ranar da su Sajida suka koreta suka karbe key din dakin.
Kuma daman wasu kayan akwai biyu biyu wasu kuma daman Both sawar maza daa mata ne.
Tahir na gefe na daukansu Hoto cikin murna yace"Abokina ga jinjina."
Ya fad'a yana sara ma Sadiq shi kuma yana mirmishi tunda bashi da kafa, sai da ya zauna Tahir ya Dora masa yaran a jikinsa.
Kallonsu kawai ya ke yi yana jin wani Farinciki daman haka ake jin in mutun ya zama Uba.
Addu'a ya ke ta tofa musu sannan Tahir ya kama masa dayan ya rike dayan ya yi musu kiran salla duka kunnuwansu kuma ya sanya musu suna batare da ya Furta ma kowa ba.
Aka bar Tahir da fadin"Ashe ashe shiyasa ka dage, ashe akwai rabon yan Biyu zarata kai da yar Zabiyar ka."
Hararansa Sadiq ya yi kafin yace" Sunanta Asiya mallam ba zabiya ba."
Tahir ya kwashe da Dariya yana fadin"To yau kuma sai ta koma Asiya ba Hasiya ba."
Yana jinsa ya yi masa banza, yaran nan sai da Nurses suka zo suka Daukesu suka maida su ciki sannan suka bar hannun Sadiq.
Adda Fati kuma taje gida ta kawo ma Hasiya wasu kaya tare da Ruwan zafi.
Su kuma su Sadiq suka tafi salla domin ba su yi azahar da la'asar ba har Biyar na yammah ya wuce
Sun idar da sallar kenan Abba ya kira wayar Tahir.
Tahir na gani yace"To an fa gane baka gida."
Sadiq ya karb'i wayar yana fad'in"Ba ni zan dauka."
Ba musu ya mika masa shi ya amsa kiran.
Abba daman suna shashen Sadiq ne an turke Auwalu dole ya fadi gaskiya Umma ta kasa zaune tsaye itace daman ta fahimci Sadiq baya gidan tunda har ciki ta shiga bata gansa ba.
Daga karshe da Tambayoyi suka tashi kan Auwalu yace sun fita a mota tare da Tahir shine Abba ya kira Tahir shi daman su suka kirasa suka tadamai Hankali kada Innani da Umma su ji Labari.
Abba na jin an dauka yace"Attahiru kuna ina ne kai da Abubukar?
Sadiq yace"Ba shi ba ne, ni ne Abba."
Abba yace"Magajin gida lafiya? Ina kuka je?
Sadiq yace"Zariya Abba."
Abba ya maimaita"Zariya?
Da yasa gabadaya su Umma suka mike suna kallonsa gaban Umma na fad'i.
Dagacan bangaren Sadiq yace"Eh nazo na iske Hasiya na asibiti zata haihu, sai dai Mungode ma Allah tunda an yi mata C.s an ciro mata mazaje guda Biyu."
Abba ya washe baki cikin Fara'a yana fadin"Alhamdulillah masha Allah, ina ita uwar fata ta na lafiya?
Sadiq yace"Eh bata dai Farfado ba dai har yanzu muna asibitin tare da yan'uwanta."
Abba ya Shiga addu'ar Allah ya bata lafiya ya yara abunda aka samu.
Sannan suka yi sallama.
Abba na sauke wayar a kunnensa mama ta ce"wa ye kuma ya haihu Abban siyama?
Cikin Tsananin Farinciki yace"Matar Magajin gida ce ta sauka, aiki aka yi mata an ciro abokaina har guda Biyu."
Umma sai ta zaro ido, Mama kuma sai tace"Allah sarki.!
Innani kam sai kabbara cikin Dariya tace"Ni"imar Ubangiji da rahmarsa ya sauka a gidan magajin gida Allahu akbar"
Sai kuma ta kasa kuka tana fadin ashe tana raye zata gani. ita innani abunta kamar na yan juju ne nan Umma ta gayamata ta saka an koreta tace gwara da akayi haka ammh yanzu ance an sauka tace Rahma ta sauka a gidan magajin gida.
Umma mamaki ya hanata kara mgana kenan yarinyar nan sai da ta kara kusantar rayuwar Sadiq ita tana Tunanin ta rabasu ashe hakan ta bai cimma ruwa ba..kafin kace kwabo kowa yaji Sadiq ya samu karuwar yan Biyu.
Sultana da siyama da suka Dawo daga Jarabawa suka samu Labari. sai kishi da bakinciki ya turkuketa har da kuka Siyama kuma sai ta kama Murna tana son ganin yaran kuma ma yan Biyu masu ban sha'awa.
Surayya da ta samu Labari ta fi kowa murna daman kuma tasan girman cikin nan na Hasiya yafi guda d'aya.
Bata yi mamakin jin cewa Sadiq yana zariya ba, daman tasan matukar yana iya tafiya sai ya nemo Hasiya zuwa kuma wannan lokacin tasan yasan komai da ya faru.
Da wayar Tahir ta kirashi suka yi mgana da shi ta yi masa barka, bai yi mata wata mgana ba itama bata yi masa ba sun Rabu akan gobe zata zo in sha Allahu..shi kuma yace zasu kwana a Hotel zuwa da Safe tunda Hasiyar ta Farfado dazu bayan mangariba.
Ni dai kawai farkawa na yi na ganin a gadon asibiti acikin daki na musamman.
Nurse din da ke kaina ta shaidamin aiki aka yi min an ciromin yara Biyu duka maza.
Ba farincikina Haihuwanta na rika yi ba sai na ganin Assadiq a kaina yana rike da Hannuna.
Sai gashi ina hawaye ina fadin"Assadiq daman zan kara ganin ka?
Cikin mirmishi yace"Gashi kin gani, ai na taba fad'a miki ni da ke har Abada ne Siya."
Duk da dinkin jikina sai da na Rumgumesa ina kukan Farincikin sake ganinsa a Lokacin da na Fidda rai.
Ban taba ganin Tahir ya yi min Fara'a irin na yau ba, shi ya mikama min yaron d'aya Assadiq ya kwantar da daya a saman jikina.
Su Adda na gefe suna ta min mirmishi da barka da arziki.
Bansan Sadiq na tafiya da Sanda ba sai da ya mike cikin damuwa na kallesa ina fadin"Assadiq me ya samu kafar ? ita bata warke ba?.
Domin duk naga Tabon ciwukan kansa cikin mirmishi yace"Karayace a kafar ita bata karisa warkewa ba."
Sai gani hawayena na diga saman ya'yan dake zube a jikina.
Mirmishi ya yi min kafin ya Furta"Nagode Nagode sosai Siya, na yaba kuma ina Fatan Ubangiji kema ya yaba miki fiye da yadda ni na yaba miki."
Na kalli yan'uwana a zagaye dani abun Farincikina ganin Assadiq a kusa dani, na tuna a baya sanda na shiga cikin kunci saboda rashinsa.
Har nagama zamana a wajen Amma bata san abunda ya faru ba, saboda kada ta Fahimci wani abu yasa nace zan dawo wajen Adda kafin Assadiq ya Dawo.
Itama da na dawo ban gayamata komai ba, har kuma zuwan Maman suhailat ni nace kada ta sanar da su, hatta kawata Ramatu na Boye mata wannan sirrin Saboda ba na so su rika kallon Assadiq da wani Duba na Dabam.
Safiya kawar Amana ce bata tafi gida ba sai da taga farfad'owata na Tuna gajiya ta yi da kiran wayata a kashe taje gidana maman suhailat tace ina gidan yayata daman kuma mun taba zuwa tare sai gata tazo ganina, da ya ke mun koma makaranta a halin nauyin cikin nan da na ke ciki tara kani makaranta naje na karbo T.P LETTER d'ina ban dai samu na kai makarantar da zan yi Teaching pratice din ba Nagudan Tsaye Tsaye ya kamani, daman kowa na mamakin girman cikina sannan kuma ya wuce wattanin haihuwansa.
Kuma da na dawo naje asibiti suka Dubani sukace lolacin haihuwata bai yi ba, duk da cikin ya wuce wattaninsa ba su ga alamun mahaifa zata Bude ba.
Yadda gabadayansu suka zagaye gadon da ni ke kwance ne ya sakani kwalla, naji a raina ni Ubangiji ya gama mini komai tunda ya barni da Soyayyar yan'uwana tare da gwarzon miji irin Assadiq
Daman na sani ko a jima ko a dad'e Assadiq zai zo ya neme ni shiyasa nima na kasa mantawa da shi acikin zuciyata.
*Janafty*
*TMWB3K012*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl
PAID ADVERT✅
Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki
* Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah
* Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari
* Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan
Allah sa mu qaru da juna Ameen
Washegari Surayya da ta shirya tafiya Zariya sai da ta biya ta gida ta sanar da Abba zata je ta duba mejego da yara.
Jin haka yasa Abba yace Mama ta shirya sai su tafi tare da Surayya sannan yace nawa suke bukata wanda zasu iya rike ma maijegon wani abu?
Ita daman Surayya ta zo da kaya cike da leda su pamper din yara ne, sai Kayan sanyi masu kyau da mayukan setin na yara.
Sai sauran tarkace irin na kayan yara dai jariri, Jin Abunda Abba yace ne yasa tace ya bari wannan sai sun je sun dawo tukunnah.
Siyama ma jin da Mama Za'a tafi ganin Twins itama ta dauki damara tace sai taje daman da Tunanin yaran ta kwana a ranta, Innani kuma damam Tun jiya ta had'a kayanta tace ai magajin gida ya yi mata alkwarin ita zata yi ma Hasiya wankan jego saboda haka rana fa bata karya sai dai uwar diya taji kunya.
Shi kuma Abba yace a tafi da ita taga ya'yan magajin gida Umma kuma sai ta zama yar kallo Sajida ma tazo gidan gulma taga ko Surayya ba ta tsaya cewa tazo su tafi ba, ballatana Abba da ga ita har Umma sai ya yi kamar bai ma gansu ba, harda Sultana da ta damu kanta da bakin kishi Saboda Haihuwar Hasiyan.
Direban Abba ya tukasu zuwa Zariya ko da suka isa ba su iske Sadiq ba ance ba jimawa suka dauki hanya shi da Tahir, sai wayar tahir din ta kira ya bashi suka yi mgana.
Ita kanta tasan Sadiq ya riketa a ransa saboda ko alama a muryansa ba wannan Fara'a da sakin jiki in yana magana da ita kuma a jiyan ta fad'a masa yau zata zo ta duba mai jego ammh yaki Tsayawa su iso.
Sunan asibitin ma Tahir ta kira da Farko ya fad'a musu da sunan lambar Dakin kafin su isa sannan suke samun Labarin Sadiq din ya Dauki Hanyar komawa Gusau.
Shi ko daman ya riga ya yi ma kansa wani alkwari acikin ransa, in dai abunda ya shafi Siya ne ya Cire kowa a ciki shine mijinta kuma Shine Dolenta ba wasu yan'uwansa ba, Abba ne kawai da Umma suka zame mata Dole suma sabama Ubangiji ya danne Bin umarninsu.
Shi daman Tunda ya samu had'arin nan da kuma jinyar da ya kwanta ba komai daya danganci katunan bankinsa a hannunsa, shiyasa ba shi da kudi sai ya yi ta aron na Hannun Tahir wanda shima yace ba na shi ba ne na ajiya ne, Kamar Abba ya sani da Safe ya kirashi suka yi magana yace ya Turamai account din bankin tahir ya Tura masa 100k.
Da shi ya samu ya yi ma Siya siyayyan kayan titi, kayan yara na pampers da Sauran su, tunda komai na haihuwan da suka tanada na cikin Dakin nan kuma sun tafi da key d'in.
Sai kawai ya bama Adda Wasu kudi yace taje kasuwa ta siyo abunda babu kafin yasan abunda zai yi akan su Sajida.
Ko zuwan su Surayya Abba ya fad'a masa ammh ya ki tsayawa Saboda bai ga abunda Tsayawar nasa zata haifar ba shiyasa yace su koma kawai.
ya so ma Tahir ya barshi ya hau motar haya shi kuma sai ya wuce Daura ammh yace a'a bai gama warkewa ba yana Tafiya da sanda bazai barshi ya yi Tafiya mai Tsawo a motar haya ba.
******
Nayi matukar Farinciki ganin Anty Surayya, acikin raina nasan ya'yana a kallah suna da masu son su daga dangin mahaifinsu.
Innani kamar ta lashe yaran nan ta yi kuka kafin su tafi bata san iyaka ba sai ta kallesu sai ta koma ta na jan majina tana fad'in"Allahu akbar Ashe ina da Rabon ganin tsatson magajin gida ban mutu?
Mangaganu dai an sha su kamar ba Gobe sun yi ta tsiya da Siyama wacce tace Innani ta hanata ganin ya'ya.
Innani ta balla mata Harara kafin tace"Kaji min rashin kunya, to an hanaki ganin su d'in, in kin ji Haushi sai ki yi aure ki haifi naki."
Siyama sai hawaye Adda Fati ce ke faman bata Hakuri innani ko sai ta fara masifa Surayya na gefe bata ce komai ba ballatana Mama da in ta Tofa tasan nata sai yafi zafi.
Ba su wani dade sosai ba sallar azahar kad'ai suka yi da Adda Fati ta yi tayi suje gidanta su huta su ci abinci Anty Surayya tace za su tafi ne kada su yi dare.
Ita dai Surayya ta yi karan cewa Umma na yi min barka na amsa ba wai domin na yarda ba, Abba dai da tace na aminta tunda kafin Tafiyar Assadiq ya had'ani da shi a waya ya yi min sannu ta wayar Tahir.
Siyama ce ta bani mamaki itama da ko maganar arziki bata tab'a had'amu ba sai ranar.
Kuma ta yi ta daukan yan biyu Hoto a waya sai da tagaji, Surayya ta kawomin kayan da ta taho da shi Inna talatu ne ke ta yi musu godiya Tunda ko a jiyan ita ta kwana dani a madadin Amma.
Wajajen Biyu da wani suka juya sai dai an sha daga da Innani Domin tace ita bazata tafi ba jego tazo yi min.
Dakyar ta yarda suka koma da ita dacewa ta bari in taje ta gama Had'o kayanta gabadaya sai ta dawo.
Anty Surayya ta bani kudi 10k tace na rike a Hannuna kafin ta Dawo yadda bata min maganar abunda ya faru ba nima ban yi mata ba duk da dai nasan tasan abunda ya faru d'in.
Sai bayan tafiyarsu ne su Adda Fati ke hirar Rigimar Innani, ina dariya nace musu haka fa take, Assadiq na bani Labarinta Akwai aikin Tsufa a tare da ita.
Sai kuma suka koma mganar Mama da Anty surayya ce, sukace ta na da kirki duk da ba su san abunda ya faru ba ammh sun san cewa Dangin Assadiq ba su karb'eni ba.
Ni dai nayi shuru ban yi mgana mganar ma tawa ta karfin Hali ce tunda ruwa kawai na fara sha, likita yace sai da safe zan fara cin wani abu mai nauyi haka.
Bani da waya a hannuna shiyasa ban yi waya da Assadiq ba, ammh mun yi mgana da Anty Surayya tunda ta karb'i lambar Adda Fati ita ta kira da Daddare muka yi mgana na yi musu bangajiya.
Assadiq kuma sai washegari can da rana ya kirani da layinsa, ashe ya siya wata wayar ce sai ya saka layinsa, tunda wayarsa tasa da Atms dinsa da I.D card dinsa da aka gani wajen da Had'arin ya faru ya na Hannun Abba sanda ya koma ajiyan a daran tun kafin ya yi mgana Abba ya Dauko masa ya bashi shine da Safe ya siya sabuwar waya ya saka layinsa a ciki.
Haka na cigaba da zama a asibiti karkashin kulawar likotici, tare da yan'uwana Amma dai bata zo ba tace ga Inna talatu nan tare dani.
Sai dai matar Hamma Isuhu da Sauran matan kannensa sun zo sun dubani sun yi min barka suka koma.
Sannan matan Baba Tanko ma sunzo tare da wasu daga cikin ya'yansa.
Na yi mamakin inda suka samu Labari sai gashi suna fadin a bakin Baba Tanko su ka ji, shima yace Alhaji Jibril ya gayamasa na haihu kuma yan biyu ni kuma nasan a cikin gidansa yaji Tunda surukarsa kanwar Assadiq ce.
Su ba su yi wata mgana ba sai da Adda Fati ta kira Goggon kona ta fad'a mata ranar da na ke da kwana Biyar a asibiti sai gata tazo da yammah,.
A bakinta na ke jin yan'uwana Suka san yan'uwan Assadiq ni suka d'orama Alhakin Hatsarin da ya same shi.
Na yi ta jin Tsoro kada ta fad'i wata mgamar da zai saka su Fahimci abunda ya faru sai kuma bata fad'a ba.
Illah Adda Rukayya da ta yi Tsaki kafin tace"wannan ba bakon abu ne goggo. Abu ya sha faruwa a d'orama Hasiya alhakin abunda bata ji ba, kuma bata gani ba."
Goggo ta tabe baki kafin tace"To mutane fa suna amfani da abunda suke gani yana faruwa ne."
In da Allah ya taimakeni ba ta dad'e ba ta tafi da mgana ta fasu, kuma sai har bayan tafiyarta ba wacce a cikin su ta d'aga maganar tunda daman na fad'amusu abunda ya faru zuwana Gusau a karo na Biyu.
Sai washegari ne da Adda Fati tazo kamar daga sama ta jefamin Tambayar a ina Sadiq din ya samu hatsarin da ake kokarin d'oramin laifi?
Kai tsaye nace achan inda yaje aiki ne, bansan karyan da zan yi a gaba ba shiyasa na yi shuru da bakina, Sannan game da key din dakina karya na yi musu