Showing 69001 words to 72000 words out of 171903 words
tayi ta miqe a yangace dan tagama sawa aranta bazai wuce Mijinta engr mahmmod ba ne"..wat the hell did he want now? Aranta tace nifa baza a takurani akan wasu tsohuwar banza ba,I can't just be rushing myself eating on d table like a baby,kayita gaishe da mace tana maka Kallon yar iska
gaskiya bada ni ba...I can't take it...inma kara zuwa min bakonta tay yau kam bazan amshe ta ba saidai yasan inda zai sakata.
Sanda tagama bambaminta tsaf snn ta mike a zafafe ta dauki wayar da niyyar sauke masa buhun masifa caraf sai taga number mahaifiyarta ne akan screen da Wani irin sauri ta sake wayar takuma daukawa da sauri hannunta na rawa ta karashi a kunnenta cikin sassauto da muryanta a ladabce "Helo Mamee?
Daga dayan bangaren akace Assalamu alaikum shema'u Ina kika shiga haka kika bar wayarki ya nata kara?
Shemau na sosa kai Tace uhmm uhmmm Mameee, dama ina Ina..Ina..kan shiri
Atsawace Matar tace dakata min shemau
Hala ma ko sallahn fajr bakiyi ba sakaliyar banza wato har yanzu baxaki dena wannn mummunar dabiartaki na baccin asarar bako? ...
Xatayi magana matar ta tsareta cikin fada sosai
Ni karki kawomin Wani bayani tunda ba yau aka saba ba Mutum in yace bazaiji tsoron Allah ba saiyayi tayi Nide gani ahanyar zuwa kofar gidan ki zamuxo ne da mutumin nan danake so ki tsayamai a kotu saiki fito ynzun nan dan bazamu jima ba.
Cikin sanyin yanayi shemau ta kalle agogon bangon dakin ganin karfe bakwaine da minti 40 yasa tayi kwafa a hankli tace toh Mameee gani Nan fitowa ...Cillo tayi da wayar akan gado ta wuce bathrum ko minti goma batayi ba ta fito daure da towel Sharp tashasshafa mai tasaka madaidaicin gown din atamfa ,Wani hijabin da tun da can take eye service dashi ta rarumo ta zura ajikinta ta tada sallan asubahi Nan ma sallama kawai tayi ta mike a gaggauce bata damu da yin koda istigfari ba ta fito.
Hijabin dogo ne wanda yaje mata har kasa Dan haka dashi kawai zata fita kodan Gudun surutun mameen sun, kalar sa ash colour sai ya mata kyau sosai dake ma Babu lokcin yin Wani shafe shafe sai fuskanta yayi fayau ya fito da innocent dinta a fili..
turaren dake kan mirron ta Dan shafa sama sama ta zura flat shoe dinta cikin sauri ta haura takan step tana saukowa kitchen direct ta nufa ta samu ruwan shayi dayaji kanunfari mai aikinta hafsa ta saukeshi kenan tana jiran ya huce kadan tayi serving dan already itace take yi ma mijin shemaun komi na abinci kuma take kulawa dashi sosai, infact kusan kominshi agidan hafsace kawai take masa sakamakon shemau iriin matayen nan ne da ko tsinke bata dagawa.
Ita kanta ba taɓuka komi makanta takeyiba bare har ajega tay ma miji dan haka hafsa ce meyin masa komi da komi gyaran gado,wanke toilet hada ruwan wanka, su tashinshi a barci goge mai takalmi,aika, wanki guga, infact evrry little thing hafsa ce keyi.
Kamar guguwa shemau ta faso cikin kitchen din ta bubbude tukunyar a kyamace taga alaman harta yi ma mijinta abinci probably hartagama dashi ya fita, karkada kanta tay cikin yanayin masifa ganin yanzu ne ma take kkrin hada mata nata breakfast din ta dafa mata noodles ta tafasa mata ruwan tea kwan ne ya rage bata soya ba taje dakinta domin daukar wayarta dataji yanata ringing.
Daga kauyensu aka kirata cewa mahaifyarta bata da lafiya sosai tana son ganinta amma tasani da wuyane shemau ta saurareta bare ta barta ta taje gida
Dan tamkar malakal maut haka shemau tazamto mata uwa wata abar tsoro dan tsabar bata ragar mata intaganta awaje bari kawai jikinta yakeyi, ga walaknci ga kuma mugunta gashi bata isa ta huta agidan ba se in shemaun bata nan.
Idanuwanta harna fidda ruwa ta zauna daga bakin gadonta tana jin nakasashen muryan ummanta dake cewa tay kkri tazo ta dubata dan tanaji ajikinta wann ciwon nata bana tashi bane tanason taganta kafin rai yay halinsa
Sosai hanklin hafsa ya tashi ta rasa meke mata dadi tunanin yadda zasu kare da shemau ya hanata sakat ta kasa cewa mahaifyarta eh ko a'a sai kuka kawai takeyi tanamata adduar sauki tana cemata karta mutu tabarta a duniyan nn bata da kowa.
Tin daga bakin kofa shemau take jin dukkan wani abunda suke fada wanda inba wai kanadaa karamcin imani a zuciyarka ba dakyar ne kaji conversartion dinsu jikinka baiyi sanyi ba.
Murya kasa kasa ahankli hafsa tace mama kiyi hakuri anty sheimaun bazata amince ba amma in sha Allahu in mijinta ya dawo zan neme alfarma ta wajenshi naga shi yanada kirki hala ya amince min nazo.
Jin hakan yasaka shema'u gyada kai aranta tanamai cewa ohhhh wato mijina nada hankli nikuma gani mahaukciya ko????..ko uban wayace mata tana ma mijina magana oho..yau nakamata yar iska karuwa kawai.
Fuuuu ta juya a fusace taje kitchen agaggauce ta dauko wuka ganin bazai mata ba ta jefar akasa ,ta dauko muciya shima bai mata ba ta yasar ta dauko wayar wata tuna cewa mum dinta is on her way taga shima bazai mata ba, can ta dawo kan table da niyyar daukar zazzafar indomie taje ta watsa mata ajiki caraf sai idonta ya fada akan tafasashen ruwan shayin
Nan.
Acikin sauri ta zubashi a kofi dan tsabar ya tafasa atake jikin kofin ya dauka da wani irin zafi.
Lkcin Hafsa harta kwantarwa mamanta hankli tana ta kkrin share nata hawayen shemau ta bankado kofar kamar ankarota tana wani huci
Suna hde ido a mugun razane hafsa ta Sake wayar ya fado kasa tayo kanta ta jawota kamar yar tsana Takai mata naushi ke Dan ubanki nine mahaukaciyarki ko?
Aiki ne ya kawoki gidana ko karuwanci so Uban wayace miki kina yi wa mijina magana...
Rudewa hafsat tay jikinta na wani irin rawa tafashe mata da kuka dan batasan ma ta labe taji maganan nasu ba
Hajiya dan girman Allah.
Kiyi min shiru tantiriya yar iska...zaki amsani ne ko saina ci ubanki..nice mahaukaciyarki
Hafsa na kkrin budar baki shemau ta shakureta tare da danne mata bakintan da karfi babu dandanin imani aranta tahau juye mata tafasashen ruwan shayin nan abakinta na dole sauran da basu shigaba nan da nan suka zuzzuba akan wuyarta suka koñata
Fadin irin azaban daya ratsa jikin hafsa bazai misaltu ba, wani irin radadi tare da azabane ya dinga ratsata kukan razana da azabar datakeyin ma bata san kalarsa ba dan har kololuwar kwakwalta taji zafin ruwan yana tsagawa.
Tuni harshenta ya ɗaɗe ya kone tasss ta dawo bata ma iya furta kalma ya fito sarari tsabar konewar da harshenta yay ta dawo kamr wata me koyon magana snn duk da ita baka ce bai hana wuyarta yin ja yabi ya kumbura ba.
Bayan ta mata wann azaban a fusace ta jefar da kofin ajikinta tahaura mata da masifa tana memeta mata abunda taji tana cewa awayarta dazu.
Babu kalar zagin da bata sha ba hartace mata ai uwarkin tasan da haka ta turo ki aiki abinni dan haka kice mata bamu bada hutun mutuwa bare na rashin lafiya.
Wallah wallah kika kuskura kika budi shaddar bakinki kika ma mijina magana akan wata personal issures dinki saina kasheki anan gidan hafsa ki gwadani ki gani....
Fuuuu ta fice ta barta anan hafsa tanata kuka rike da bakinta dayakan mata radadi duk ta dukunkune ta rasa inda zata aje kanta taji sanyi
Ko numfashi bataja ba taji muryan shemaun daga waje tana cewa
Kin fito kin hada min breafst koko kina jirana nazo na karyaki awajen
Da sauri ta miƙe jikinta na rawa sosai tanata kuka a sanyaye, rike da bakinta ta isa kitchen din ta soma harhada mata komi akan tray kamar yadda ta saba
falon kasa shemau ta sauko inda ta samu har ummanta ta iso sunyi cirko cirko atsaye cikin shigarta na brown colour hijab dogo har kasa sabida normally dama mahaifiyar sun haka take dressing dinta a nitse kasancewarta kamilar mace me addini sosai.
Kallo daya mahaifyrtata ta mata sann ta dauke kai tabi ta hade ranta
Shemau Tana karasowa cikin falon ta rusuna har kasa kamar mutuniyar kirki ta hau gaida mahaifyartan wanda take amsata ciki ciki Dan jiranta datasa sukayi ya matukar bata haushi Wai ace mace kamar shemau bazata farka tun asubahin fari ta fuskance hidiman dake gabarta ba? Yo metakeyi agidan mijin? ..Wani uban tsakin takaici taja sanin cewa tun asali laifinta ne da bata musu tarbiyan haka tun Suna yara kanana ba dan lokacin da ubansu yakeda matsayi yanada babban mukamin gwamnati girman gata kawai aka basu,toh yau gashi Babu uban Babu muqamin kuma yara sun riga sun fandare gaskiyar bahaushe dayace icce tun yana dan karami ake tankwarasa basai ya girma ya bushe ba.
Bayan sun gaggaisa shemau tafara yima mutumin da suka zo dashi din wasu tambayoyi tana recoding awayarta dan dama case din rape ne akan uba da ƴarsa amma ana zaton kawai sharri yarsan ta masa bisa umarnin wanda ya mata aika aikan
Bada jimawa hafsa ta leko ganin sunyi baki yasakata koma kitchen din da sauri ta hado musu shayi suma ta taho musu dashi.
Bakaramin ja idanunta sukayi ba ta sauko tana tafiya ahankli kamar batada laka ajiki
Sussunkuyar da kanta kasa take sabida kar aga konewar da wuyarta yay da ruwan zafi ga bakinta dayay wani irin jaaa yadan haura har labbanta yana nunawa.
Kafafunta dake bari mahaifyar shemau ta dinga kalla tana mamkin tsoron me kuma yarinyar takeji hartake ɓari haka wanda da alamu batamasan jikin nata na rawa ba.
Sallama tay muryanta wani iri dan kalmomi basu fitowa abakinta da kyau bisa konewar da harshenta yay tace "atata lekum...nnna ikwana?
Ta rusuna tana gaishe su mamaki ya cika masu jin magananta wani iri kmr na yara.
Shemau sai watsa mata muguwar kallo da gefen idonta takeyi akanda tay sauri tabar wajen kar mum dinta ta fahimce wani abu..
Acikin sauri hafsa ta zuba musu shayin ta juya zata haura sama kenan mahaifyar shemaun tace "ke zonan?..
Da sauri hafsa tajuyo kanta na kallon kasa
Kirjin shemau yahu dukan tara tara
Kare mata kallo matar tay sosai Batace mata uffan ba ta dubi shemau tace "ya naji muryanta haka ko dama haka take magana ne???
Dariyar yake shemau tay tace "ohhh ai bebiya ce mameee haka maganan ta yake baiya wani fita.
Matar Tace ohhh toh jeki
Cikin sauri hafsa ta bar wajen shema'u ta sauke
Boyayyen ajiyar zuciya.
bayan yan wasu lokuta na tattaunawa kadan shemau ta kammala deban rohoton mutumin tare da tabbatar masa da cewa zatayi iya bakin kkrinta wajen ganin an kwato masa gaskiyarsa.
Daga nan sukayi sallama
Ayayinda take rakasu mahaifyarta take kara mata nasiha akan zaman aure dan duk gabaki daya yanayin data kalle hafsan a wahale kuma a firgice aranta sam hakan baiyi mata wani dadi..
Da can harta turje mata tace sam sede akira hafsan ita zata tambayeta taji matsalarta amma haka shemau ta yi kutunktun tahana hakan yuwa
Anan ma ta sauya fuska kalar mutuniyar arziki ta hau tabbatar ma mameentan cewa yanayine kawai na yaranta amma hafsa bata da wata matsala agidan face missing din kauyensu datakeyi acewar shema'un wai aure kawai hafsan ta saka aranta shiyasa batason ta zage tayi aiki, gashi kuma mahaifiyarta tana fama da jinya akauye danda kudin aikintan dashi suke siyan abinci da magani..
Seda ta karkatar da maganan a wann sigar kafin nan mahaifyartan ta kyale zancen tare da ce mata ta dinga kkri wajen nitsar da hafsan sosai.
Wajajen karfe 9 saura suka wuce gida tana dawowa cikin gidan ko karyawa batay ba tay wanka ta zuba uban kwalliya tare da sako wata tsadaddiyar turkishi abayanta mai kyau baka
Tabishi wedge shoes na kamfanin zarah da jakarsa. Wasu iri dokoki ta zubawa hafsan as usual kafin nan ta bar gidan tana Allah Allah ta isa anguwar lekki domin ta ji damuwar hadiza dan ganin miscalls dinta datay dazun tasan bana lafiya ba.
Fannin meenal kuwa gabaki daya bawani jin dadin rayuwarta tayi ayau din a office ba duba da babu fadila awajen aikin yasaka abubuwa suka dan soma cirke mata dake fadilan itace yawanci take daukar aiki
Mafi yawan tanayi a memakonta koda kuwa tananan.
Gashi dama fadilarce kawai tay mugun kwarewa wajen iya aikin tare da iya bida jama'ar dake shige da fice yau da batanan sai abubuwan gaba daya suka rikice ta rasa gane kan komi
Tsabar takaici batama jira lokcin tashinta ba ta tattara kafafuwarta ta wuce gidan halisa nanma tun daga bakin gate malam liman ya sanar da ita cewa sun fita da jasmine a mota baisan inda suka nufa ba
Da dumbin takaici tabar wajen, nan ma tazo ta tarar da wani takacin daga wajen mijinta dr khaleel dan wani sabuwar sarar da ya samona shareta musammn intazo masa da wani complain dinta da babu kai babu gindi.
Yauma ko kula zancenta akan fadilar datakeyi bai yi ba ya fice agidan cikin sauri sauri yanamai duba agogon dake makale a hannunsa da alaman ana nemansa urgently awani waje.
Bude motarsa yay ya shiga yana zaunawa ko kunnata baiyi saiga sakon text message ya shigo atake ya bude yagani an rubuta masa
Location: _NISA Premier Hospital in Lagos located at 2/4, Afolabi Awosanya Street, Off Road 12, Lekki Phase 1, Lagos._
Team: Dr Asim khan(ccc)
Assistants Dr khaleel hasheem and Dr surayyat usman Adetunji
Client: Miss Halisa roberts mansa.
Duration:12 months.
Acikin yanayin sauri ya aje wayar harya kunna motarsa zai wainata ya fita kamar an tsakureshi cikin dakatawa yay sauri ya dauki wayar ya sake duban sakon da kyau. Dede wajen dayaga an rubuta"Halisa mansa Ya kure da idanu,tunowa da cewa halisan dayasani ne yasakashi jan wata kakkaurar tsaki tare da cewa shitttt!!!..dan ko kadan basa shiri da aminiyar matarsa wato Halisa roberts mansa.
AYI SHARING PLEASE
SURAYYAHMS 08060712446
[1/24, 9:13 AM] Lady Surayyahms.: _*CHEATERS CLUB...*_
_(Babban goro sai Magogin ƙarfe...)_
#ROMANCE
#FICTION
#ADULTHOOD
#SEXADDICTS
#WOMENPOWER
BY
_SURAYYAHMS_
_08060712446_
⏯️1️⃣6️⃣
Wajajen karfe 4:3/pm bayan anfito daga sallan la'asr Dr khaleel ya karyo kwanan NISA Premier Hospital dake 2/4, Afolabi Awosanya Street, Off Road 12, Lekki Phase 1, Lagos. wani babban private hospital ne da akeji dashi A garin da kewaye sabida tsabar haduwarsa da yelwatan kwararrun likitoci na zamani da ma'aikta jajirtacu dake aiki awajen,anan ne international doctors kamarsu Dr Asim khan din suka fiyeyin Aikin su in angayyatosu, hasalima shiyake rike da komi na fannin psychology and therapy da Abunda ya shafe gyaran hali na wanda suka zama addicted da shaye shaye da disoder na yawan son jima'i da kuma hyper sexuals.
asibitin ya kafu duk dama asibitin mallakin private organisation ne, Dr khaleel yana shigowa ciki yay parking car dinsa acikin yelwataccen harabar asibitin daidai inda aka barmusu wajen parking slot na manyan likitoci ,yana zare keys ajikin motar ya koma yay jinginar dakanshi akan seat yay lumui har nadan wani lokaci, bayajin zai iya saukowa atake sabida yadda yakejin kansa kamar yay loosing interst akan aikin bana wasa ba,har cikin ransa yaji abun ya fice masa aransa, dan ganin sunan Halisa robert akan file din sosai ya dagamai hanklinsa bana wasa ba.
dan duk duniya in akwai wacce ya tsani su xauna na minti daya a inuwa daya toh halisa ce so how can he even treat her for a year mtsswww tsaki mai cike da hatsala ya kufce masa..
Ta windown motar ya karewa asibitin kallon sama da qasa dan gaba d'aya jiyay kmr komi ya dena burgesa wahallalen tsaki ya saki sannn ya dau wayoyinsa cikin sakalo kafafunsa dats so cute acikin wata arniyar versace black cover shoes,cikin nitsuwa da haduwa yama motarsa lock snn ya soma tafiyarsa mai aji wanda take nan not too slow and not too fast dai dai misali,kayan jikinshi dake kanana ne,dan suit yasaka bazaka masa kallon babba sosai ba sedei hadadden saurayi.
as usual suturarsa na black and white ne ajikinshi,wanda babu ta inda qualityn kayan take gazawa wajen bayyana fasalin sa na hadadden guy mai kyaun aji da cikakken nitsuwa.
Yana danna sliding door hadadaiyar qamshin turaren sa na zebra rasasi ta tursasa dumbin mutanen dake tsattsaye awajen maida hankalinsu kansa..
Shikuwa Direct ya wuce gaban counter inda ya same wata beautiful nurse dake ta famar hadiyar yawu tana kallon sa tun daga farkon shigowar sa har izuwa tahowarsa gabanta,kallo daya yy ma wajen duka ya dauke kansa tamkar ma baisan anayi ba, bold nd confidently yace mata excuse me?"kallonshi ta karayi,yace "may i speak with doctor Asim khan?
wani daburtaccen sosa gefen kunnenta tayi dan tamkar wanda taji dirin sautin muryan aljani haka sautin muryanshi mai bala'in dadinji ya ratsa mata dodon kunne Adan rude tace
Uhmmmm...uhmm yes..yeah. and you are?Kure ta da ido yay sannan yace "Dr khaleel". dago idanuwanta tayi ta wani kalleshi dan bata san sanda ta maimaita sunan san ba cos already tasan da wannan appointment din dazu sectaryn ogansu ya bata wannan sunan akan maishi zaizo,tasaba manyan mutane kadai sukan zo wajen doctor Asim kai tsaye ganin khaleel so young and charmin abun saiya dan mata mamaki.
Ganin bama kulata zaiyi ba tayi saurin daukar recep caller takai shi kunnenta tace hello sir?daga ta dayan bangaren aka amsa ta, within few minutes ta aje wayar,sai gata ta fito daga counter ta na wani irin kirkiro salon rigimamayar murya tace masa,"right after u please,baice uffan ba ta shiga masa jagora har izuwa benen sama na biyar kusanma atare suka bude kofar suka shigo har can ciki,wani kayataccen offis ne na doctors yasha kwalliyar grey and black sofas har ynxu nurse din sai azaban kallonsa takeyi while she is not sure ko yasan ma tanayi.
murmushi tayi tace.."he is here sir..tafada tana kallon doc Asim dayake kkrin dago kansa daga kan file din dayake dubawa tsohone kuma ba indiye wanda yay fice sosai akan field dinsa na mental therapy and psychology.
Babu yabo babu fallasa yace mata "thank you"..u can go .. Tana rife kofar khaleel ya dan sake sakaltaccen tsaki akasar wuyarsa dan bayau ya saba cin karo da ire irenta masu masa kallon maita dana kurilla ba
Daure fuska yay kmr wacce tce masa saceshi zatayi, Dr asim baiyi niyyar murmushi ba amma sanda yayi dan dolensa ganin yadda khaleel din yake bin kofar da kallo kamar da gaske kidnaping dinshin za'ayi..
Sanda ya samu nitsuwa snn yadan kirkiro murmushi ya miƙawa dr Asim din Hannu suka gaisa sosai dan kuwa bakaramin sabawa sukayi ba infact shine ma mentor nashi dayaje yin karantunsa na 2yrs area of specilisation a