Showing 72001 words to 75000 words out of 176868 words

Chapter 25 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

sanyin AC dake zagaye awurin saida Dr Adnan yahad'a zufa sharkaf sabida tashin hankali da fargabar dake tare dashi,
kallo d'aya zaka yimasa kagane tsantsar tashin hankalin da ke shinfide akan fuskarsa cikin mutuwan jiki yayi isa office d'inshi,
Cikin hanzari Ummi dake zaune akan sallaya tana jan jarbi,
tamik'e tsaye tana mai zuba mishi ido tare da fad'in.
"Baban Adnan yafarka kuwa?."
saurin sai-sai ta nutsuwarsa yayi dan son boye tashin hankalin da yake ciki kana yace.
"Ehm Uhmm ba..ba..bakomai fa Ummi in sha Allah zai farka in Allah ya yarda ba wata matsala."
ita kam Ummi cikin rashin gamsuwa da maganarsa tafara magana cikin zubda kwalla tanafadin,
"Ka fad'amin halin da yake ciki in yamutune ma kada ka boye min dole inyi imani da k'addarata."
da sauri su Raliya dasuke zaune agefe suma bayan sun idar da sallah suka taso.
Hayatuddeen dayanzu dawowarsa daga masallacin dake cikin asibitin,shima ya'iso da sauri,
ganin haka yasa Dr Adnan cewa.
"Ummi baifa mutuba zo kuganshi ma."
kana ya juya yayi cikin room d'in dasauri suka rufamasa baya,can suka hangosa kwance ga na'urori sakale ajikinsa
da sauri suka nufi jikin gadon,idanunsa arufe ruf bayako motsi, abinda zainuna maka cewa yanada rai shine numfashin shi da yake ja tacikin na'uwar jan numfashi.
cikin rauni da fargaba jiki na rawa Ummi tariko hannunsa yayinda hawaye ke kwaranya a idanunta murya na rawa
tace.
"Saifuddeen wanene yayimaka wanna illa haka? waya zalincemu zalumci mafi muni arayuwar mu? memuka tare masa?."
a tare tajero tanbayar tareda kife kanta ajikin gadon ta saki sassanyan kuka.
Hayatuddeen,da shima kukan yake ganin dan'uwansa acikin mawuyacin hali,
Raliya Raihana duk kuku suke,
Dr Adnan ma shima kukan yake babu mai rarrashin wani a cikin su zuwa can Dr Adnan yashare hawayen sa cikin hanzari yamaso kusa da Ummi muryarsa narawa ya kwakulo murmushi dole yace.
"Ummi bawata masalafa ku kwantar da hankalin ku in sha Allahu zamuyi duk abinda yadace."
cikin muryar kuka Ummi tace.
"Adnan duba kaga halinda Saifuddeen yake cikifa sannan kace wai babu wata damuwa,
ka duba ka gani nice yau a gaban Saifuddeen amma yagaza d'aga ido yadubeni bare harya shiga farin ciki kamar kullum saboda ganina akusa dashi,
lallai Saifuddeen d'ina yana cikin mawuyacin hali."
sai ta kuma rik'e hannunsa tamatse acikin nata tanamai cigaba da kukan,
da sauri Dr Arabi yaturo k'ofar da sauri dan duk abinda suke yanajinsu daga cikin offece insa,ya'isa ciki tareda d'aura wata na'urar dake rike a hannunsa asaman kirjin Saifuddeen dan da alamun bugun zuciyarshi ta tsananta da sauri
yace.
"Ummi ku d'an je waje zamuyi aiki yanzu."
dakyar Ummi tasaki hannun Saifuddeen ta fita tana cigaba da sharar kwalla,
su Raliya ne sukabi bayanta.
Hayatuddeen ko wayar Saifuddeed ya d'auka wanda yagani agefensa sanna yafita, sunafita Dr Arabi yahad'a na'urar daya d'aura kan kirjin Saifuddeen,
kana ya juyo yana fuskantar Dr Adnan tare da cewa.
"Haba Dr Adnan a matsayin ka na Dr bai kamata karika kashewa majin yatanka guiwaba,
kamata yayi karika karfafa musu goiwa surika sawa aransu majinyacinsu zaisami lfy,
amma kaima kazauna agabansu kana zubda hawaye ai sai ka saka musu kokwanto azukatansu,
tabbas nasan shakuwar dake tsakanin ka da Saifuddeen,
so hakuri zakayi kabasu kwarin goiwa akan samun saukinsa sai kaga komai yatafi dai-dai."
a hankali Dr Adnan yashare hawaye kana yace.
"Hakane amman kaima kasan dai akwai babbar masala,
bazan tab'a iya mik'ewa ya tsaya da kansa ba,bazai iya morar kansa ba,
saboda illar da suka yimasa agadon bayansa zuwa kugunsa,bansan tayanda zansanarwa Ummi wanna mummunar labarin ba"
a hankali Dr Arabi yace. "Nasani,to amma ya zamuyi da ikon Allah, shi ya halicci Saifuddeen kuma ya fimu sonshi kuma insha Allah shi zai zama gatanshi,
yanzu dai ya kamata musan menene mafita."
shiru Dr Adnan yayi saboda tunanin hanyar data fi dacewa don dole a wuce da Saifuddeen Abuja.

Koda Hayatudden yafita Gefe yakoma yazaro wayarsa a'al'juhu dan tun jiya yake akashe yakunna sanna yasaka wayar Saifuddeen acikin aljuhun,
bayan yakunna wayarsa saiya lalub'o number Ishaq wato babban abokin Saifuddeen,
yana d'agawa yace.
"Hello Hatuddeen yau kuma gaisuwar sassafene za'ayiwa Hamma Ishaq."
cikin raunin murya yace.
"Ina kwana Hamma Ishaq."
da sauri yace.
"Lafiya lau, Hayatuddeen."
bayan sungaisanne Hayatuddeen yake ce masa. "Hamma ishaq muna asibiti Hamma Saifuddeen bashida lfy."
ba k'aramin tashin hankali Is'haq yashiga ba dajin cewa abokin sa na'asibiti wanda jiya da yamma suka rabu lafiya-lafiya sannan kuma yanada tabbacin cewa bakaramin ciwo bane zaisa Saifuddeen yakwanta a asibiti.
shiko Hayatuddeen katse wayar yayi yakoma inda su Ummi suke,
jugum-jugum sukayi kowa da abinda yake sakawa azuciyarsa.
sunan zaune har gari yayi haske.

Karan ababen hawane yacika cikin harabar asibitin motoci da mashunan guragu irin masu tsada da kyau wanda zasu iya kaiwa 23 kana sai wasu motoci kusan guda 6 wanda sukeda tambarin (Jonapwd) Gombe state chapter all the best! bi ma'ana tambarin k'ungiyar nakassasu ta jihar wato Joint national association of persons with disabilities.
kuma kowani mashin guda mutane biyu ne ke kansa,haka sukarika faka mashin d'in suna sauka akansa,abin mamaki mutanen duk nakasassune,
sai dai bazaka tab'a banbance makafin cikiba domin babu sanduna a hanunsu bare yan jagora kana suna cikin tsabtacecciyar shiga ta alfarma mafi akasarinsu sunfi kama da ma'aikata, kuramen ciki kuwa bazama ka tab'a zaton sunada wata nakasa a jikinsu ba, guragu kuwa sai dai ka gane da sawun wasunsu da suke a shanye wasu kuma da sanduna suke dan tokarawa gaba d'aya sun cika harabar asibitin kuma ba hayaniya bare sowa suna komansu cikin tsari da wayewa fiyema da masu ji da gani yayinda wasu ke ambaton.
"Ya Allah! kabaiwa d'an uwanmu Garkuwarmu lfy,
idan kacire manashi a cikinmu bamu san ya zamu k'are da rayuwaba dan munsan cewa zamu tagayyara mudawo abin kyama abin gudu acikin al'umma sunai mana kallon wasu hallitu na daban." makafin cikinsu nata fad'in. "ku kaimu inda yake?."

Mutane sukarika fitowa daga cikin asibitin, wad'anda suke gefe da asibitin wato mazauna gefen asibitin suma suka shisshigo,danganin taron mutanen dasuka shigo cikin asibitin.
Dan ganin abinda kefaruwa,jama'ar dasuka fito dan kallon mutanen sunsha mamakin jin kallama da ya kefita abakin wadanna nakasassun,sai ambaton Saifuddeen suke,
jama'a duk suka cika da alhinin jin sunan wanna bawan Allahn dasuke ammaba,to waye shi dahar wadanna mutanen zasu nuna damuwarsu da tashin hankalinsu akansa,lallai wanna mutumin komai akayi adaline,sosai a garesu domin wasuma sunyi zaton ko zanga-zangar lumana nakasassun keyi,
gurin ya kacame da hayaniyar mutane dake tambayar meke faruwa.
Hayatuddeen ne yamik'e tsaye da sauri yace.
"Ummi mutanen Hamma Saifuddeen ne sukazo dan naji sunata kiran sunansa bari naje wurinsu."
kai kawai Ummi ta'iya gyad'a masa alamar toh.

Hayatuddeen yafito farbajiyar asubitin suna ganinsa suka nufi inda yake suka zagayeshi,suna fadin.
"Ina Saifuddeenin d'inmu yake kanunama inda yake."
hannu sa yad'aga sama yana juyashi, tare da yin sauri ya isa gaban Ishaq cikin girmamawa yace.
"Ya ishaq barka da zuwa."
da sauri ishaq ya mik'o hannu ganin haka shima Hayatuddeen ya mik'o mishi hannu tare da cewa.
"Gani nan Ya ishaq."
da sauri ishaq yace.
"Yauwa Hayatuddeen ta ina Saifuddeen yake muje mu ganshi."
cikin d'an murmushi Hayatuddeen yace.
"Hmmm kai ishaq kullum lamarinka akwai k'arfin hali da iya ruggumar k'addara wai muje mu ganshi sai kace kana gani."
shima Ishaq murmushi k'arfin hali yayi tare da cewa.
"ai ba idone gani ba, ku masu idone kuke d'auka da ido kawai ake gani, mu kunnuwanmu ma tamkar idone kana da zuciyarmu da k'ok'wolwarmu, yayinda kuramenmu kuma idanunsu ne kunnuwansu, ba gashi yanzu koda bana ganinka nasan kana zubda hawaye daga sautin muryarka."
cikin sanyi Hayatuddeen yace.
"Ku kwantar hankalinku,
ku dakata dan Allah kuyi hakuri yanzu bazaku sami ganin saba dan yasamu yin bacci saidai zuwa anjima."
cikin gamsuwa sukace.
"To yajikin nasa?."
saida ya maida hawayensa dake kukarin zubo masa dagudun kada hankulansu yatashi,danyasan cewa basu kadai ahalinsa kebukatar Hamma Saifuddeen ba, hardasu wadanna nakasassun,dama wasunsu baki d'aya,.
"Da sauki". yace dasu atakaice,
dakyar shugabannin nasu suka samu suka lallab'asu sukatafi,sanna shikuma Hayatuddeen yayiwa su ishaq d'in iso zuwa ciki inda su Ummi suke.

Suna shiga Dr Adnan nafitowa,
kana Dr Arabi nabiye dashi su Ummi naganinsu sukamike tsaye suka k'araso inda suke,Ummi kallonsu take fuska kunshe da tanbayoyi
Dr Arabi yakalli Dr Adnan wanda keta noke-noke yayi masa alama da ido,
jiki asanyaye Dr Adnan ya mik'awa Ummi wata doguwa takarda fara yace.
"Ummi wanna takardar ta transfer ce zuwa Abuja,
naturaku asibitin kimiya dake birnin tarayya Abuja National hospital Abuja
,idan kun isa saikiba su wanna takardar
da sauri Ummi tace.
"Abuja! Kuma?."
kai ya gyad'a mata alamar eh,
a hankali tace.
"Lallai ciwon Saifuddeen babbane tunda har katuramu Abuja."
Kai Adnan ya girgiza dasauri,dan bazai iya fad'a mata akwai masala ba, yafiso sai sunje can d'in asanar musu.
tana karbar takardar yayi saurin juyawa dasauri dan gudun kada Ummi takuma jefo masa wat tanbayar,
yanafita yayi duk wani cuku-cukun dayadace natafiyarsu ba tareda bata lokaciba yakammala komai bank'arensu.
Ishaq kuwa takardar ya amsa kana suka juya tare da Raihana, kai tsaye Federal low cos suka nufa,
E passport d'in Ummi da Saifuddeen dana Hayatuddden yasa Raihana ta kawo mishi,
daga nan direban k'ungiyar tasu yaja suka wuce Airport, nan ya gama musu dukkan shirin tafiya hardashi d'in suka kuma yi sa'a akwai jirgin da zai tashi zuwa Abuja k'arfe biyun rana zai tashi.

1:53 pm duk sun gama shirin komai,
takofar baya Dr Adnan yashiga yaturo gadon yafita takofar bayan,
Dr Arabi natsaye ajikin motar da zai kaisu airport da taimakon sa suka tura gadon cikin motar suka dai-dai zaman gadon sosai acikin motar,
Kana Dr Adnan yakoma indasu Ummi suke yace.
"To Ummi an gama shirya komai shirya komai ku akejira yanzu,
sanna kuma tafiyar zai kasance dole damutun biyune sanna kuma... da sauri Raihana tace.
"Ummi ku kutafi keda Hayatuddeen, mu zamu koma gida nida Raliya fatanmu samun saukin Hamma Saifuddeen zan kira Abban Farida yayi k'ok'arin dawowa,."
cikin gamsuwa Ummi tace. "to".
"kuyi maza kutafi nima zuwa gobe da yamma zan shigo Abujan."
Dr Adnan ya fad'i tare da juyawa yayi gaba,
da sauri suka bishi abaya.
koda suka'isa jikin motar, Ummi da Hayatuddeen suka shiga,driver yatada motar Raliya da Raihana nad'aga musu hannu dayimusu fatan samun nasara,yiyinda dukansu suke ta sharar kwalla,driver yaja sukabar harabar asibitin,
"Sukadau hanyar Airport, in da tuni ishaq na can su kawai yake jira.
suna isa bada jimawa ba jirginsu ya tashi.
3:00pm yamusu a cikin birnin taraiya Abuja direct National hospital suka nufa.
Kasancewar duk abinda yadace Dr Adnan yarigada ya'aiwatar dashi ta online , so ansan da zuwansu,basusha wani wahalaba,suna isa nurses suka taho jikin motar data d'aukosu daga airport nan suka fito dashi.
Kana Ummi
tamikawa d'aya dagacin nurse d'in takardar da Dr Adnan yabata,sanna suka turoshi sukashiga cikin asibitin, direct Emergence room aka shige dashi.
Nan Doctors suka dukufa akanshi basu yi wata-wata ba suka fara bincike akan laluransa kamar yanda yazo musu arubuce,
cikin k'ank'anin lokaci S.....!







By
*GARKUWAR MARUBUTA*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: [3/30, 10:50 AM]
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAKASA BA KASAWA BACE*

*PAGE 15*

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


~Free page~


Suka gano matsalar shi, kana suka dugufa kanshi dan samo numfashin sa ya dai-dai ta, domin babu wani aiki da zasuyi mishi har sai ya dawo haiyacinshi.
Hakan yasa suka meda hankali ganin komai ya dai-dai ta, cikin ikon Allah a daren ranar ya farfad'o yana kuma cikin haiyacin sa, kasan cewar dare yayi nisa, yasa aka bar batun dubashi zuwa safiya.

Bappa Ali da Warisu da Mudassir kuwa tunda Hayatuddeen ya sanar musu gaba d'aya hankalin su ya tashi sai dai sun meda hankali wurin yi mishi addu'ar samun lfy a cikin ka'aba.

Ishaq kuwa, tunda aka shaida musu bazasu dubash yau ba sai gobei, sai ya kira babban yayanshi dake nan Abuja da iyalanshi ya shaida mishi, ba jimawa kuwa Ya Rabi'u yazo tare da direbanshi, domin dukkan sashin zuriya biyun sun san abotar Ishaq da Saifeddeen domin abotace tun na yarinta, hakan yasa har iyaye su suke mutunci da zumunci mai k'arfi.
Kasan cewar babban doctor uban gidane ga Dr Adnan hakan yasa tun kafin suzo an shirya komai, hatta da masu kula dashi, ya tanadar cikin ma aikatan nasu,
ya kuwa kontarwa Ummi hankali ta tare da bata k'arfin guiwa.
Haka yasa Ya Rabi'u ya tafi da su gidanshi, cikin sa'a ma kuwa asibitin ba tazara sosai da diganshi.


Ummi kuwa da Hayatuddeen dugufa sukayi da Addu'a jigon nasu.
Deren ranar sam basu rumtsaba, shima Ishaqa bayi bacciba.


A can gida Gombe kuwa, bayan su Raihana sun koma gida, kai tsaye falon Ummi suka wuce,
cikin sanyin jiki Raihana ta zauna bisa kujera,
idonta ta rumtse da k'arfi, a jere wasu zafafan hawaye suka zubo mata,
ita kuwa Raliya wayarta ta d'auka, ta fara 'yan dube-dube bayan yan wasu dak'ik'u ta kara wayar a kunne,
a hankali ta bud'e labbanta tare da cewa.
"Wa'alaikassalam, Abban Farida, yaushe zaka dawo?."
a can d'aya sashin Abban Farida yace.
"Lafiya dai ko?."
murya a sanyaya tace.
"Alhamdulillahi ala kulli halin."
jin haka yasan to tabbas akwai matsala sai dai iya sarrafa harshe na matar kwarai wacce tasan yadda zata isar da sak'o wa mijinta ba tare data firgitashi ba,
cikin dakiya yace.
"Meke faruwa?."
tallabe hab'arta tayi tare da cewa.
"Abban Farida ka dawo gobe, please inda hali in zaka samu jirgin yau dan Allah ka taho gida."
cikin kad'uwa yace.
"Raliya meke faruwa ki gaya min mana, zuciyata ta cika da zulumi."
"Hamma Saufudddeeen! Saifuddeeen!! Saifuddeen..!!!."
tai ta maimaita mishi murya na rawa.
mik'ewa yayi tsaye cikin fargaba yace.
"Innalillahi wa Inna'illaihi rajiun. Meya sameshi? ina Hayatuddeen? Ina Ummi?."
Cikin kuka tace.
"Suna Abuja an tafi dashi asibiti."
daga nan ta sanar dashi dukkan abinda yake faruwa,
ta k'ara da cewa.
"Ya Adnan ya turasu Abuja. Abban Farida ka dawo wlh Hamma Saifuddeen ko motsi baya yi sanda suka tafi dashi."
ta karishe maganar tana zubda hawaye.
Shi kuwa Abban Farida datse kiran yayi kana ya fara harhad'a yan abin buk'atunshi, kai tsaye Airport ya nufa cikin sa'a ya samu jirgin Abuja, dama shi bai niyar zuwa Gombe ba.

Kafin su isa abuja dare ya d'an fara nisa kuma yayi ta kiran number Hayatuddeen da Ummi duk basu d'agawa, haka yasa ya nemi masauk'i inda ya kwana da nufin da safe zai nemesu.


Dr Adnan kuwa, saida yaga tashin su Ummi sai da ya koma asibitin kafin ya koma gida.
Shiru parlour nasu ba kowa haka yasa ya zauna bisa 1 str zuciyarshi da jikinshi na cike da fargaba da tsoron halinda martashi Rahma zata shiga in taji abinda ya samu d'an uwanta,
ya rasa tudun dafawa, a fili yace.
"Ya ilahi ya mujubbat da'awati ko taya zan sanarwa Rahma."
sai kuma yayi sauri zaro woyarshi Ishaq ya kira,
bayan sun gaisa yace.
"Kun isa lfy,?."
"Lafiya lau Alhamdulillahi."
gyara zamanshi yayi tare da kallon k'ofar corridor d'in part d'in Raihana sannan yace.
"Kun samu Dr Aliyu ko?."
"Eh to gsky mun samu tarba daga wurin Doctors har uku to gsky ban sanan wanne ne Dr Aliyun ba a cikinsu."
cikin sanyi yace.
"Zakaga Dr Aliyu shima nakasasshene ai domin shima yanada matsalar spanal cord kuma shine big doctor a k'asarnan in dai a wannan fannin ne, uban gida nane kuma wa nane d'an kawuna."
cikin jin dad'i Ishaqa yace.
"Alhamdulillahi, hakan yayi kyau domin dama shi nakasa ai ba kasawa bace, kuma ya yi mana k'arin bayani kan mu kontar da hankalin mu, Alhamdulillahi kuwa tuni ya farfad'o kuma yana cikin haiyacin sa, so zuwa gobe da safe zasu fara bincikan adadin zurfin ciwon."
lumshe ido Dr Adnan yayi kana yace.
"To Allah ya kaimu, in sha Allah nima gobe zan taho please kuke kontarwa Ummi hankalinta."
"In sha Allah ba matsala." cewar Ishaq.
Kana daga nan sukayi sallama,
shi kuwa Dr Adnan Dr Aliyu ya kira bayan sun gaisa yake mishi godiya tare da tambayar ya mai jikin, so shima Adnan ya samu d'an nitsuwa duk da cewa Dr Aliyu ya tabbatar mishi cewa Saifuddeen ya samu nakasar lakkar bayanshi.
bayan sun gama woyar ne yana d'ago kanshi ya hangi Rahma tsaye bakin k'ofar kitchen ta kafeshi da ido gaba d'aya jikinta tsuma yakeyi tuni hawaye sun jik'a fuskarta,
mutuwar zaune yayi domin tabbas yasan taji duk wayar da yayi dasu, dan sam hankalinshi bai bashi ko tana kitchen ba.
Ita kuwa matsowa ta farayi a hankali take taku still jikinta na rawa,
gabanshi ta tsaya tare da tirtsetsen cikinta,
da sauri yasa hannu ya jawota jikinshi kan cinyarshi ya ajiyeta, suna fuskantar juna, murya na rawa tace.
"Me kuma zaka boye min Ya Adnan me zaka boye min? gaya min me zaka boye min. wani abune kuma ke tinkarar rayuwarmu? meya samu d'an uwana? ina yake, waye zai nak'asa Saifuddeen ne ko Hayatuddeen gaya min wani hali Ummi ke ciki?."
gaba d'aya ta birkice ta gigitashi da tambayoyinta yama rasa wanne d'aya zai amsa mata kuma tana k'ara tuno mishi fargabar da Ummi ke ciki.
Kawai sai ya had'eta da k'irjinshi ya ruggumeta da k'arfi kana ya fara magna cikin dakiya yace.
"Madadin kiyi mishi addu'a sai kiyi mishi kuka? kin san halin da yake shiga duk sanda yaga hawaye a kwaranya a idanunki, meyasa rauninki yake yawaita, da can baya da juri na sanki to meyasa bazaki ruggumi k'addaraba, ki godewa Allah a cikin dukkan lamarinki."
tunda yace mata kin san baya son kukanki ta gane Saifuddeen ne, to wani zafin ya wuce inda hawaye yake fargabarta da nitsuwarta duk sun had'u sun hargitse sun danne hawayenta,
sai tayi wani azabebben murmushi da yafi kuka zafi cikin sanyi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login