Showing 54001 words to 57000 words out of 176868 words
Chapter 19 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel
cewa.
"Zaka sake yin sati uku har kusan hud'u baka zoba kuma kana cikin lfy."
Kai ya jujjuya mata yana mai shafa kunenshin,
daga nan sukaci gaba da hira tana mai tayasu aikin nanda nan suka gama girkin suka jera komai a dinning table,
daga nan suka zauna suka karya,
Saifuddeen ne ya fara cire hannu sai kuma Rahma sannan Salisu nandai duk sukaci sukayi nak,
suna gamawa Ahmad ya tattare wurin sannan ya nufi d'akinsu dan yana son watsa ruwa,
Salisu ne yabi bayanshi sai kuma Mudassir.
Ya Adnan kuma gyara zama yayi tare da cewa.
"Ummi ta gaya maka dalilin kiran da nake maka ne?."
kai ya jujjuya mishi alamun a a,
cikin nitsuwa Adnan yaci gaba da cewa.
"To batun Faruq da Adam ne naje jiya dan zan d'aukosu su dawo nan da zama a gabanmu zamufi samun konciyar hankalin da damar basu kulawar da ta dace a matsayinmu na iyayensu, sai Ummi tace min wai ai ka hana,
shiyasa na nemeka inji dalilin da yasa zakace kada a bamu su."
kanshi ya d'an sunkuyar cikin dottaku da sanin ya kamata ya kuma d'ago kanshi tare da mishi mgna cikin body language yace.
"Ba komai kawai dai naga gidan naku a cike yake gasu Ahmad sannan kuma kace zaku k'ara dasu Faruq,
kuma nasan Baba Hamisu bazai amince ba."
murmushi Adnan yayi tare da cewa.
"To jiyan ai saida na fara zuwa wurin baba Hamisun na nemi al'farma kuma ya amince, hakama Bappa Ali sai dai in kai d'inne zaka k'i amincewa ban saniba ko ban dace da a bani su bane."
da sauri ya jujjuya mishi tare da zaro wayarshi ya rubuta mishi.
"Ba haka bane Ya Adnan wlh bana son rabuwa da yaran ne,
hakama Ummi itama suke d'ebe mata kewa,
sannan Hayatuddeen shima sune masu d'ebe mishi kewa tun kafin ayi auren yaketa cemin kar in bari Adda Rahma ta tafi da yaranshi fa."
ita kam Rahma ido ta lumshe lokacin da Adnan ke karanta rubutun,
tasan duk farin cikinta sukeso tasan irin son da Saifuddeen kewa su Faruq,
tasan shi kuma ya Adnan yana son yaran sosai kuma yasan zatafi samun farin ciki in suna kusa da ita ido ta zubawa mijin nata kuma abokin yayanta jin yana cewa.
"Dan Allah da sonka da manzosa ku bamu yaran nan mahaifiyarsu zatafi samun nitsuwa tashi d'aya a rabata da yaranta abin da ciwo a rai."
da sauri Saifuddeen ya zubawa Rahma idanu ganin tana zubda hawaye alamun tabbas tana tare da kewan yaran nata.
Hannunshi yasa ya sharte mata hawayenta sannan ya amshi wayarshi tare da rubuta musu.
"Kiyi hak'uri Adda Rahma kada ki zubda hawayenki kinsa Raihana da Raliya zasuyiwa su Faruq duk abinda uwa ke yiwa d'anta kinsan Ummi kuma zata basu ink'antacciyar tarbiya,
ni kuma zan zame musu uwa uba."
kai ta jujjuya tare da cewa.
"Na sani Saifuddeen na sani ai ni kaina ka zame min uwa uba bare yaran da nasan ka fini sonsu duk da ni na aifesu."
sai kuma hawaye yaci gaba da zubowa ganin hakane yasa Saifuddeen mik'e tare rubuta musu.
"To ba matsala zan kawo muku Adam amman kuyi hak'uri bazan iya baku Faruq ba."
murmushi yayi ganin itama tana murmushi shi kuwa Ya Adnan dariya yayi tare da cewa.
"To Hamma Saifuddeen mun gode a hakanma,
dan naga yanzu ka zama kaine babba a kanmu."
dariya sukayi baki d'aya sannan suka mik'e suka dawo parlour
cikin kula Rahma tace.
"Saifuddeen zo ka duba bedroom mana ka kashe min kud'i kuma baka zo ka duba kayan d'akinba kaga yadda parlour kam yayi kyau ko d'an uwana."
murmushi yayi tare da mata alamun.
"No shi bazai shigaba komai yayi kyau."
sai ya kuma mata alamun in akwai abinda take buk'ata ta gaya mishi, cikin jin dad'i tace.
"Ka gama min komai d'an uwana ba abinda baka yi minba komai sabo ko budurwa bazata nuna min sabbin kayaba."
sai ta kuma kalleshi tare da cewa.
"Yauwa dama ina son in ce maka kasa su Raihana su jerawa Ummi tsoffin kayan d'aki na d'in nata kuma ta bawa Goggo Dada su."
kai ya jinjina mata alamar to,
sannan ya nufi d'akinsu Ahmad nan sukayi ta hirarsu ta abokai,
sai k'arfe tara Saifuddeen ya mik'e ya shiga bathroom wonka yayi yana fitowa yasa kayan Ahmad daga nan suka fito da shirin tafiya dubu uku ya bawa Adda Rahma kana ya bawa Ahmad da Mudassir dubu bibbiyu sannan suka sallamesu suka tafi.
A daren ranar yaje ya gayawa Baba Hamish batun ya Adnan ya nemi da a basu Adam.
Cikin aminci baba Hamisu yace ba matsala a basu.
Washe gari ya rarrashi Ummi ya samu ya kai musu Adam.
*************
Lokaci yaja kwanaki sun tafi makonmi sun gibta sun juye ih zuwa shekaru.
Rayuwa taci gaba da tafi,
Al'barka yanata ratsa dukiyar marayun nan yayinda adalcin Saifuddeen yake tasa dukuyar habaka,
tausayinshi da gskyanshi da taimakonshi da yawan sadakanshi ya zamewa dukiyarshi Garkuwa.
Abubuwa da yawa sun faru a shekarun nan.
Tuni Saminu ya fara aiki a kaduna har an aura mishi Raihana.
Suna can kaduna garin gwamna mai mata had'i da mota.
Ahmad da mudassir da Ishaq ma sun gama karatunsu,
tuni har ishaq ya samu gurbin karantarwa a jimi'ar Gombe state University,
wanda wannan abu yake matuk'ar bawa mutane mamki ganin gashi makaho kuma yayi karatu kuma gashi har yana karantarwa.
Mudassir kuwa da Ahmad basu samu aikin yiba kasan cewar yanayin k'asar ne digiri ya zama ruwan dare ko wanne gida da akwai sai dai samun aiki sai d'an talaka yayi dace,
wannan dalilin yasa Saifuddeen ya jawo Ahmad da Mudassir cikin kasuwancishi cikin ikon Allah kuwa taurarinsu suna haskawa kasuwancinsu yaci gaba,
kasan cewar dama shi Ahmad business administration ya karanta shi ya bawa kasuwansu damar habaka gabas da yammaka kudu da arewa.
Alhamdulillahi shima kanshi Saifuddeen da Salisu sun gama karatunsu,
to amman basubi ta kan neman aikiba,
dan a ganinsu duk sunada sana'a kawai dai sun nemi ilimin ne dan shine gishirin rayuwa,
to ta inama zasu fara tunda sunaga Ahmad da Mudassir ma shekaru biyu kenan har zuwa uku da gamawarsu basu kuma samu aikinba bare su da kwanannan suka gama bautan k'asarsu.
Zuwa Yanzu ko bappa Ali bai san adadin dukiyar da Allah ya azurtasu da shiba shi,
Saifuddeen ne kad'ai yasan k'a'ida da adadin dukiyarsu, kasan cewar shi yana ajiye komai a rubucene yanayin hakane kuma dan ta hakane zasu san adadin zakkar da zasuke cirewa duk shekara.
Ganin harkar k'arfe ya karb'i Salisu to sai ya bare kud'i kimanin 3 million ya bawa Salisu ya fara zuwa sarin motoci a Cotono da mota biyu rak ya fara sari yan million d'aya da rabi-rabi cikin ikon Allah a ko wanne mota ya samu ribar dubu dari uku-uku, koda ya ware kud'in mai da kud'in sauran uzururruka da kud'in da ya biya wanda ya tashi d'auko motor ya samu sauran ribarsa dubu dari uku da hamsin,
nan yaje ya bawa Saifuddeen su,
shi kuwa Saifuddeen yace bazai karb'i ko asiba,
yace yaci gaba da tara ribarsa randa ya samu ya tara koda 5 million ne sai ya maida mishi kud'inshi million ukun shikenan daya bashin,
shi kuma ya d'auki wannan na ribar tashi yaci gaba da sari ya samu jarinshi kenan da haka,
ya k'ara da cewa ya bar mishi su halak malak.
to fa daga nan Salisu ya fara harkar mota babu kama hannun yaro kuma Alhamdulillahi harkar ta amsheshi.
Shagunanshi a kasuwa kuwa yanzu Warisu da Bello da Mudassir suke kula dasu yayinda Ahmad kuma ya zama tamkar manajansu,
shine ma'ajiyinsu yakan fita zuwa su Lagos onitsha da dai sauransu yayi musu sarin kayan masarufi, direct to company.
Bappa Ali kuwa shine mai sarin kayan abinci ciki da wojen gombe Alhamdulillahi yanzu abun ya hab'aka shiyasa yawanci da Warisu yake shiga sauran k'auyuka na sauran jihohi kamarsu.
Bauchi, Jigawa, Jos, da Adamawa musamman kasuwar cigari ta adamawa inda nanne dilar manoman shinkafa na jihar.
Ummi taje makka ta sauk'e farali hakama bappa Ali da goggo Dada,
shima Saifuddeen yaje tare da Adda Rahma Ya Adnan kuwa ya biyawa kanshi da mamansu so duk a shekara d'aya sukaje.
To da yayi niyar Raihana da Raliyya duk zasuje shekarar data gabata,
inda yacewa Hayatuddeen yayi k'ok'arin haddace izu arba'in kafin nan to zai had'a dashi suje,
aiko Hayatuddeen yasa himma,
to yanata shirye-shiryen biya musu hajjin kwasam,
sai Alhaji Kabiru ya kawo mishi tallan wani gida dake kusa da gidanshi a nan federal low cost.
Koda ya samu Ummi da Bappa Ali da zancen sai Ummi tace ya bar batun biya musu hajjin ya bari sai wata shekar in Allah ya kaimu,
a cewarta kadarar babban filin da mahaifinsu ya bar musune suka saida suka kama sana'ar dan haka yayi k'ok'ari ya sai wata kadarar da zata ke tuna mishi da gadon da mahaifinsu ya bar musu.
shi yaso ya biya musu Hajjin to amman fir Ummi tak'i hakama bappa Ali dole ya hak'ura yabi ra'ayinsu.
Sai dai kuma cikin ribar ledanshi da yake tarawa tsawon shekaru da balance d'in machine d'in da Salisu ya rik'e tsawon shekaru da kuma wanda iro yake kawowa har yanzu da kud'in ne yace zai sai gidan sabida baya son tab'a wannan dukiyar gadon nasu yafi son ya sayi gidan da guminshi shi d'aya yadda zai zama halak makal d'inshi,
Ummi da bappa Ali sun amince da haka to amman kud'in nashi basu wuce rabin kud'in gidanba dan haka sai ya ranci sauran rabin kud'in a cikin tarin ribarsu na shekarar da zumar zai biya kud'in da balance d'in machine d'inshi da kuma ribar ledodinshi da omonshi da su pure water da ribarshi na gefen kayan masarufi wanda yanzu k'atun firijine ya saya ya ajiye a bakin shagonsu sannan yana saran omo yana sawa a gefe kuma har yau yakan rarraba leda ya kuma had'a kud'insu ya basu sannan ya cire ribarsa,
to duk wani abu daya sani dukiyarshice ta kanshi wanda ya tara da guminshi to a account number daya kuma bud'ewa na musamman yake sa kud'in a ciki.
so hakan ne yasa suka amince da hakan cikin wata biyar akayi cikinikin gidan aka gama,
sosai cinikin gidan ya zabge asusunsu Saifuddeen ya kuma sashi cin bashi,
sai dai kuma duk wanda yaga gidan yasan lallai tabbas gidan yaci wannan milliyoyin kud'in.
To fa tun randa Hayatuddeen yaga gidan ya kasa ya tsare dolefa su k'aura su bar dukku,
haka zai tasa Ummi da Saifuddeen a gaba harda kukanshi shidai a bar wannan k'auyen dashi.
Ahmad da Mudassir kuwa har yau a gidan Adda Rahma suke,
ita kuwa Adda Rahma har yau Allah bai basu haihuwa da Ya Adnan d'intaba.
Warisu da Salisu kuwa suma yanzu an kusa bikinisu inda sun gina 'yan madaidaitan gida jensu a cikin unguwar Dubai cottars.
Ishaq kuwa shima yanzu ya fara taka k'asa,
tuni yayi gidan kanshi saidai har yanzu bai fara neman aureba,
yafi maida hankalinsu wa kula da k'ungiyarsu ta,
Joint national association of persons with disabilities,
(Jonapwd) gombe
state chapter. All the best!!! yayinda yanzu shi har ya samu muk'amin ciyaman a kungiyar,
Saifuddeen kuwa bai fiye zuwa ofishin nasuba sai dai yana matuk'ar bada taimako da dukiyar da Allah ya bashi ta sanadin nema da guminshi kusan akwai kason daya ware duk wata yakan saka a asusun k'ungiyar,
baya zuwa amman hannunshi na zuwa sai dai in zasuyi Mittin mai girma da mahimmanci to Ishaq na sashi zuwa bisa dolen-dole da zaran an gama mittin kuma zai tafi.
Ahmad kuwa soyayya yake zubawa Raliya sosai.
Yauma kamar kullum Hayatuddeen ya tasa Ummi da Saifudden da Rahma da tazo duba jikin Mamansu Ya Adnan a gaba,
fuska ya kwabe tare da tura baki cikin kalato hawayen dole yace.
"Dan Allah mu bar zancen auren Ya Ahmad da wannan yar cukului d'in shin nan."
bai kula Raliyya dake watsa mishi hararaba yaci gaba da cewa.
"Ni dai dan Allah ku rufa min asiri mu k'aura mu bar wannan gari na dukku wallahi ni dai na gaji da garin nan."
cikin irin son da iyaye ke yiwa 'yan autansu Ummi tace.
"Wai ni kam ku saurari autana d'innan mana yace muku ya gaji da dukku."
fuskarshi ya kuma kwab'ewa tare da cewa
"Ba waninnan Ummi ai duk kece kikak'i ki amince na san in kin cewa Hamma na mu k'aura dai zai yarda."
Rahma ce ta gyara zamanta cikin sanyin muryarta tace.
"Wallahi Allah ko Ummi nima ina son ku k'aura ku dawo cikin gombe kusa dani,
ku ganifa bani da kowa a can dan ma Allah yayi Mamansu Ishaq tanada kirki,
wlh ko Ya Adnan ma cewa yayi ya dai kamata ku dawo gombe ko dan karatun Raliya da Hayatuddeen,
dan cewa yayi ya kamata ace Raliya taci gaba da karatu ta samu koda N,C,E ne tunda sun nacewa juna ita da Ahmad kuma shi yace bai yi aure a gidan hayaba,
gashi kuma ya kasa k'arisa ginin gidanshi."
shi dai Saifuddeen ido ya zuba musu dan shi kanshi ya gaji da wannan zirga-zirgan kuma yana son faranta ran Hayatuddeen da Faruq,
shiru sukayi jin Faruq na cewa.
"Nima dai wlh na gaji da k'auyen nan yaseen ko mu k'aura mu koma gombe, ko kuma inbi Ya Adnan in koma gidansu."
cikin nitsuwa Ummi tace.
"To Saifuddeen ka jisu ko?."
Kai ya gyad'a mata alamun eh yaji,
cikin sanyi tace.
"To nima da kaina ina son mu koma cikin gombe ko dan tak'aitawa Saifuddeen zirga-zirgan da yakeyi kullum yana hanya tsakanin Gombe da dukku,
to sai dai haka kawai in na tuna mu k'auran sai inji zuciyata ta tsinke wani azabebben fargaba yazo ya rufeni shiyasa jikina ke mutuwa."
Da sauri Rahma tace.
"In sha Allah ba komai sai al'khairi kawai dai inaga fargaban rabuwa da inda kika saba ne shiyasa kikejin hakan."
kai Ummi ta jinjina dan kamar ta gamsu da mgnar Rahma,
cikin sanyi tace.
"To na amince Babana in dai kana son mu k'aura to na amince."
da sauri Saifuddeen ya kalli Hayatuddeen da Faruq da suka durk'usa gabanshi suna ta magiyar dan Allah yace shima ya amince."
kai ya gyad'a musu alamar to ya amince.
Ido suka zazzaro gaba d'ayansu dan ganin wani irin...!
By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:51 PM - Ummi Tandama: ๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 11*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐
~Dan Allah kuyi haฦuri masu cewa in rufe group bazan rufeba! Sabida inada dalilin barinshi a buษe~
_Lale marhababikun masoyan littafin Nakasa ba kasawa bace ina maraba daku, turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number! 09097853276. Ko ka/yimin transfee ta bank ac na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, pleess ku fahimceni ษari uku nace kuma ga number da zaki turo tanan ko ac no ษina_
_Dan Allah dan soyayyarmu da annabi kuji tsoron Allah ku dena tambayata tsoffin littatafaina, sai kuzo ku haษani da Allah in ban kulakuba inji ba daษi, dan Allah ๐๐ป ku bari bana so! Pleees fans ษin hukuncin Allah da suka saya wai yanzu basu dashi ku dena tambaya bana so๐กku tambaya a gruops ษin Hukuncin Allah, bana son shegen takura da rashin tausayi ,fisabilillahi a wuni zan samu pc sama da 1000, masu sabon littafi da masu son tsoffi da ฦดan gaisuwa da wasu ga tarin rashin fahimta nayi bayani inda za'a turo kuษin da adadin da za'a turo amman sai kaji ana, Slm Aunty Aishs ta ina zan turo/ koko Garkuwa nawane kuษin littafin koma kece Garkuwa en nace eh sai ace wai ,a a ฦarya kike ba kece Garkuwa ba, ko kuma wai Garkuwa nake nema, koko wai dan Allah turo min littatafai masu daษi jifa kamar ni baiwarsu ce ฦดan gab da kano kawai yaseen ku ba ฦanenne uwata bace da amsa muku zai zame min wajibi_
Zabura da yayi tare zurma ihu mai cike da jin dad'i sai ya kuma zaro woyarshi dake cikin al'jihunshi samfarin infinix Hot 5 wanda a lokacin ita ake yayi, kid'i ya kunna tare da fara zabga rawa baji ba gani,
yayinda Faruq ma ke take mishi baya,
cikin yanayim fad'a Saifuddeen ya watsa mishi harara tare da mishi mgna cikin body language yace dashi.
"Irin godiyar da ya kamata ka yiwa Allah kenan bisa wannan ni'imar da yayi mana? rawa da ihu shine kaga ya dace?."
kai ya jujjuya mishi yana mai ci gaba da jujjuya k'ugunshi ganin haka yasa Saifuddeen yi mishi alamun cewa.
"To na fasa tunda hakane tunda bazaka nitsuba sai randa kayi hankali ka nitsu zamu k'auran."
da sauri ya nitsu tare fuskantar gabas kana ya gyara tsayuwarshi sannan yayi sujjadar godiya ga Allah,
yana d'agowa daga sujjadar ya fuskanci Hamma Saifuddeen d'in nashi cikin sanyi yace.
"Hamma Saifuddeen na nitsu dan Allah kada ka fasa kaji d'an uwana."
k'ara matsoshi yayi ganin bai kulashi ba sai ya kuma raunata fuskarshi sannan murya na rawa yace.
"Na tuba Abba."
cikin tausayin yaron Saifuddeen ya gyad'a kai dan duk sanda zai nuna mishi biyayya irin na d'a da uba to yakan ce dashi Abba.
tsalle yayi ganin Hamman nashi ya huce,
sai ya kuma lallatsa wayarshi sannan ya kara kunne jim kad'an aka d'aga.
Cikin tsananin jin dad'i yace.
"Hello Imran al'bishirinka."
A can d'aya sashin kuma cikin d'aga sauti da yanayin rawan kai da rigima irin na Hayatuddeen Imran k'anin Ishaq yace.
"Goro fari k'al ba dukke bani insha."
dariya Hayatuddeen yayi tare da cewa.
"Da kenan! yaseen yanzu Bagombe nake,
Hamma na da Ummi da Bappa Ali sun amince zamu k'auro."
wani wawan zabura imran yayi tare da zurma tsalle ya saki ihun da saida Ishaq dake gefenshi ya mik'e tsaye Mama kuwa dake bedroom ta fito parlour da gudu tana cewa.
"Innalillahi Imrana lfy kuwa meya sameka."
rawa yayi ya kuma juyawa sannan cikin karad'i yace.
"Su Hamma