Showing 114001 words to 117000 words out of 176868 words

Chapter 39 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

da Mudassir da bello ke zaune a babban falon Ummi yayinda Ahmad ya tasa na'urar system a ganshi suna kallon Saifuddeen kana shima yana kallonsu.
Tattaunawa sukeyi kan kasuwancinsu da Allah ya sanya mishi al'barka.
Duk shiru sukayi suna sauraron bappa Ali da yake ware musu kud'in hakk'in aikinsu na cikon shekara.
Sannan ya hada lissafin da suka kawo baki d'aya,
kana ya shiga cikin hatimin zakka,
Kai ya d'ago ya kallesu tare da cewa.
"Zakkarmu ta bana ta kama million hud'u da dubu dari biyu da hamsin da uku zamu fidda."
cikin gamsuwa sukace.
"Na'am."
cikin nitsuwa bappa Ali ya kalli fuskar Saifuddeen ta na'urar tare da cewa.
"Su waye kakeda niyar bawa zakkarka?."
gyara konciyarshi yayi tare da jawo system d'in nashi ya gyara zamanshi kan ruwan cikinsa kana ya fara rubutu musu mgnarshi.
"Akwai bappa idi bappan Ummi dake garin Hashidu, a ware dubu dari biyar a bawa Ahmad da Ummi su kai mishi.
sai Goggo Abu Goggon Ummin a bata dubu dari biyu da hasin d'in.
Million d'ayan kuma Mudassir da Warisu su d'auka,
Bello kuma a bashi rabin million,
Sannan million biyu daya range d'in a rabawa makotanmu na dukku."
cikin gamsuwa bappa Ali yace.
"Hakan yayi Allah ya sanya al'khairi."
Amin Amin sukace baki d'aya,
sai kuma Ahmad ya kalleshi tare da cewa.
"Sai zakkar kasuwarka ta omo da kayan sanyi.
shi dubu dari takwas da hamsinne zakkar."
ya za'ayi dasu?."
Murmushi yayi wanda saida fararan hak'oransa suka baiyana cikin ratsin jajayen lips inshi.
amsa ya rubuta mishi da cewa.
"Wannan na goggo nane a bawa goggo Dada zakkan d'anta gaba d'aya."
Cikin shak'uwa Ahmad yace.
"A a kai malam wai ni bazaka bani zakkar bane?."
Kai ya gyad'a mishi tare da mishi alamun kaima mai badawa ne.
Dariya sukayi baki d'aya,
kana Warisu yace.
"Anfa gyara shagon da kasaya dinnan, sauran zuba kaya kawai."
Kai ya jinjina tare da rubuta.
"next week Ahmad zai tafi Dubai shida Raliya da Anty Kubra zasuje suyi mana sarin, kayan yara da na yan mata da kamarsu dogayen riguna gyalluka zanuuwan gadaje kananun kaya da sarak'una."
Kai ya jinjina cikin gamsuwa shi kuwa Ahmad shafa kai yayi tare da cewa.
"Jiya da Safe Jabeer d'in ya kirani yace ya gama yi mana shirin komai."
da yake da Jabeer d'in zasuje.
kai Saifuddeen ya rausayar tare da rubuta mishi.
"Eh yama turomin hotunan sabbin kayyakin da ake hari, kai dai ka zama cikin shiri."
bappa Ali ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
"To batun sarinmu na kayyakin abinci duk dama kasuwannin sun tanadarmin dan na basu adaddin da nike buk'ata.
Sannan kasuwar magi shi tuni Ahmad ya sara, saura ya tura musu kud'in."
Cikin gamsuwa ya rubuta musu.
"Bana kuma kamfanin k'ananan baturan radio sun tallata min hajarsu. Shiyasa na rage sarin magin zamu sari baturan koda kad'an ne."
Eh hakan yayi cewar Bella da Muddasir.
Daga nan suka tattauna yadda komai zai wakana sannan suka tashi taron.

Abuja birnin taraiya. Amina ce zaune gaban Mommo Hajia Salma kekkyawar bafillatanar jada.
cikin kula tace.
"Niko ya lbrin jikin Saifuddeen?."
ido ta d'an rufe cikin jin kunya tace.
Mommo jikinshi da sauk'i yanzuma muka gama mgna da Hayatuddeen.
Yace min yanzu yana iya jujjuyawa da kanshi."
Cikin gamsuwa dan duk familynsu sun san Saifuddeen a sanadinta sabida yanzu dai a rayuwarta tafi son mgnarshi fiye da komai.
Haka yasa iyayenta ke tsananin jin dad'i dan tunda Amir ya saketa bayan aurensu da sati d'aya bata kuma yin mgnar wani d'a namiji ba sai kan Saifuddeen ko dan haka baya rasa nasaba da rashin mutuncin da Ya Amir ɗin nata ya mata wanda suke ƴaƴan maza kuma a gidasu ya Amir ɗin a gaban mahaifiyarshi ta girma kasan cewar shi ɗaya suka haifa ita mahaifinta da mahaifiyarta suna Jadan Adamawa.
shekararta d'aya da rabuwa da Amir kafin ta had'u da Saifuddeen,
cikin sanyin murya Mommo tace.
"Kwanan Daddynku zaije India, in yaje zai isa ya dubashi da jiki."
murmushi tayi mai cike da Happy tace.
"Badon aiki da yamin yawaba da munje tare."
itama Mommo murmushi tayi kana tace.
"A a ki bari sai sun dawo Nigeria sai muje mu duboshi da jikin."
cikin gamsuwa tace.
"Allah ya dawo dasu lfyto."
Amin Amin tace kana sukaci gaba da hira.


*************

A hankali fa rayuwa ke tafiya kwanaki na shud'ewa i zuwa makonni makkoni na juyawa i zuwa watanni.
Abu da yawa ya faru cikin watannin nan kamar zuwan Daddyn Amina da zuwan Adda Rahma da Saminu da Raihana.
Da Mudassir da Warisu.

Kasuwancin Saifuddeen yanata habaka ga amintattun ma'aikata da ya samu bisa jagorancin Ahmad da su Mudassir.
Yanzu Ahmad shi iya dukiyar Saifuddeen tashi ta kanshi yake jujjuyawa kuma Alhamdulillahi kasuwancinfa sai gaba-gaba.

Yau watansu Saifuddeen goma sha d'aya cib a k'asar India.

Hayatuddeen ne ke zaune gefen Saifuddeen dake kwance bisa dukkan alamu bacci yakeyi.
shi kuwa Hayatuddeen waya yakeyi da Umminshi shiyasa bai lura da Saifuddeen da yayi mik'aba tare da bud'e idanunshi.
ido ya zubawa k'anin nashi da yake waya yanata zuba sakalci wa Ummin nasu.
wani nannauyan numfashi ya firzar tare motsa k'ugunshi, sai kuma yayi saurin juyawa rigingine.
Wani sabon lamari ne yaji yana dirar mishi cikin k'ashin bayanshi wanda kusan wata d'aya kenan yake jin abun.
ido ya rumtse tare da d'ago kafad'unshi,
kamar al'mara sai gashi ya d'ago kafad'unshi har zuwa k'ugunshi wani irin zafi yaji yana ratsashi sai kuma ya tauna lips inshi duka biyu,
sannan ya yunk'ura da k'arfi sai gashi a zaune da daɓas duwawunshi zama kuma na gam da gam.
Dai-dai lokacin Ummi ke cewa Hayatuddeen
"Har yanzu bacci yakeyi ne?."
a hankali ya juyo kanshi, dai-dai lokacin kuma Saifuddeen ya muskuta tare da gyara zamanshi daram bisa tsakiyar gadon.
Cikin tsananin kad'uwa da tarin farin ciki da al'ajabi Hayatuddeen ya cilla wayarshi gefe tare da kurma wani irin firgitaccen ihun da tsalle tare,
"Ummeeee Hamma Saifuddeen ya tashi ya zauna kanshi."
sai ya kuma sakin wani hargitsestsen ihun da yasa Saifuddeen jin kunnuwanshi sun bada wani sassanyan sautin keuuuuuuuuuhh cikin kunnuwanshi daga nan kuma sai kuma jin shuuh a hankali abin yakeyi a kunnuwan nashi.
ido ya zuwa Hayatuddeen wanda ya kware baki da iya k'arfinshi yake rabkawa Dr Anan kira.
"Dr Anan! Dr Anan!! Doctor Anan!!!...!."

A can gida Nigeria kuwa cikin New G.R.A Zaleeha ce ta fito cikin parlour Baba malam fuskarta cike da hawaye,
kai tsaye parking lot nasu ta nufa tana zuwa wurin Raveel na sako kai cikin gidan nasu.
Da sauri ta shiga cikin motarta da gudu ta fita daga cikin gidan.
Ganin haka shima Raveel yabi bayanta.

Babu inda suka tsaya sai cikin gidan M...!


Ka/ki biya ɗari uku kacal dan jun ƙarshen labarin, in baki da ƙuɗi ba dole bane sai kin karanta na sataba, gwara ki karance tsoffin littataimana baya kinga bakici da gumin daba nakiba.


By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:53 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAKASA BA KASAWA BACE*


*PAGE 23*


NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇





Sai cikin gidan Maryam tana isa shima yana isa.
Kusan a tare suka fito cikin motocin nasu.
Da sauri ya nufi inda take fuska cike da tsantsar kulawa murya a hargitse yace.
"Me hakan? Wannan wanne irin ganganci kikeyi da ranki? So kike ki fasamin zuciyta ne?."
Hannu tasa ta sharte hawayenta, yayinda tuni wasu suka biyo layin wad'anda ta gogen cikin raunin murya tace.
"Meyasa haka? Raveel meyasa zakayi min haka meyasa zaka tura iyayenka wurin Baba malam bayan kasan yadda nake fuskantar takura a gida, meyasa zakayi min haka ni nace ka tura iyayenka gidanmu ne?."
K'ara motsowa yayi gabanta cikin fidda sassanyan numfashi ya lumshe ido tare da bud'esu kana yace.
"Sabida ina sonki, kin kuma sani ina sonki, amman kika nuna kamar baki saniba, kin barni soyayyarki nata d'awainiya dani, na rasa sukuni, bani da zabin daya wuce dole in sanyan iyayenmu cikin zancenmu.
Zaleeha kin sannifa kinsan halina kinsan tarbiyata kinsa komai nawa to meyasa kike gujemin meyasa kike son nasantamu."
Cikin tsananin k'unan rai tace.
"Sabida bana sonka, bazan aureka ba, kai ba abokin rayuwata bane."
Idonshi ya rumtse da k'arfi tare da bud'esu kana yace.
"Ni dai ina sonki kuma dole insa iyayenmu cikin mgnar in dai ba so kike in mutuba."
A hatsale tace.
"Sai me? ka mutu d'in mana, na ce bana sonka na tsaneka bazan aureka ba."
ta k'arishe mgnar hawayenta na ci gaba da zubowa.
Jin wani azabebben fargabane ya sashi jingina da jikin motarta dan jin alamun zai iya fad'uwa a hankali yace.
"To meyasa? Me aibuna?."
Da sauri tace.
"Auren ne bazanyi ba ko akwai dole ne."
tana fadin haka tayi cikin gida,
da sauri yasha gabanta tare da cewa.
"Baki isaba in sha Allah sai na aureki, sai na zama mijinki."
wani irin zafi taji kalamanshi na gasa zuciyarta cikin hatsala ta d'ago hannu ta yarfa mishi mari tare da tureshi gefe ta wuce tayi cikin gida.

Ya Ameenu kuwa yana sama yanaji da ganin duk abinda sukeyi.
Ganin ta zubawa Raveel marine ya sashi fitowa ya nufi parlour k'asa da tsananin sauri har yana take steps d'in bibbiyu uku-uku dan azabar zuciya da zafin raina,
tabbas yanzu ya yarda muddin akabar Zaliha zatayi abinda taga dama.

Tana isowa parlour yana sauk'owa,
Da sauri ta tsaya tare da zaro ido ganin ya nufeta gadan-gadan.
Yana isa inda take ya ware tafin hannunshi cikin zafin rai ya fara yayyarfa mata wasu gigitattun tagwayen marukan da suka sata ganin start's suna yawo kana kunnenta ya bada sautin kauuuu.
kafin ta dawo daga gigicewar data shiga ta kuma jin wasu tsinannun marukan da suka sata cilla wani irin zazzafan k'ara mai gigita duk wanda ya jita.
"Wayyo Maryam Ya Ameenu zai kasheni."
shi kuwa Aminu cikin haki yake ci gaba da yayyarfa mata mari yana mai cewa.
"Ae gwara ki mutu kowa ya huta,
tunda fand'arewa kikeso kiyi,
Yanzu kinfi k'arfin mata sai maza.
Ashe har kin kai matsayin da zaki d'aga hannunki ki mari d'a namiji, dan yace yana sonki."

Raveel kuwa tunda ta kwad'a mishi mari ya sunkuyar da kanshi k'asa,
saida yaji ta saki ihunne yayi sauri ya kutsa kai cikin gidan.
Maryam kuwa tana isowa parlour sai ta koma gefe ta zuba musu ido.
Raveel d'inne yayi k'arfin halin kamo hannun ya Ameenu tare da cewa.
"Dan Allah dan darajar iyayenmu kayi hak'uri ya Ameenu mu bita a hankali please kada ka daketa."

Ita kam Zaliha tuni tayi bedroom d'in Maryam a guje tana shiga tayi fad'uwan 'yam bori bisa gadon kana ta saki wani marayan kuka.

Shi kuwa Ya Aminu bisa kujera ya zauna tare da nunawa Raveel kujera alamun ya zauna.
Bayan sun zaunane ya kalli Raveel cikin sanyi da tafasan zuciya yace.
"Raveel kayi hak'uri da abinda Zaleeha tayi maka,
In sha Allah daga kanka bazata sake gigin marin wani d'a namiji ba."
Cikin sanyin Raveel yace.
"Ba komai ya Aminu, Allah ya tabbatar mana da al'khairi."
Amin Amin yace kana yayiwa Raveel rakiya har bakin gate.

Ita kuwa Maryam ganin mijin nata ya fitane yasa ta juya a hankali tabi bayan k'anwar tata,
tana shiga ta maida k'ofar ta rufe.
Da sauri ta haura kan gadon cikin tausayawa tace.
"Zaleeha, kiyi hak'uri kiyi shiru kukan ya isa haka please kinga ga Ayman ma ya fara kuka,
Gaya min make faruwa?."
A hankali ta mirgino tare da kife kanta bisa cinyar maryam cikin tsananin kuka tace.
"Raveel ne ya tura iyayensa wurin Baba malam wai suna neman izinin zance.
yau tunda safe ya aika ya Habu ya kirani ina shiga ya hauni da fada.
Wai zan maidashi mutumin banza ya za'ayi inyi ta turo mishi dattawan mutane.
A karshe yace dole cikin manema in fidda goni ko shi yamin zabi, yace min wai karfa inga yayi shiru yana sane k'a'idar da ya bani saura wata d'aya".
Numfashi ta sauk'e a hankali tace.
"To ke Zaliha auren ne bakya so?."
cikin shesshek'a da miryar tausayi tace.
"A a ni bance bana son aureba."
Cikin kula tace.
"To bakida masoya ne?."
Still hawaye na zuba tace.
"Ina dasu amman ni bana sonsu."
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"To wa kike so?."
hannunta tasa duka biyu ta matse kanta da k'arfi cikin rauni da tashin hankalin dan a duniya tasan wannan amsar itace tafi komai wahal da ita cikin muryar kuka tace.
"Adda Maryam ya kike min tambaya kamar bakisan komai a kanshi ba?."
cikin sin cire mata wannan tunanu Maryam tace.
"Shi waye ɗin kenan?."
Kai tajujjuya kana tace.
"Shi nakeso! Shine farin cikin rayuwata, in dai ba shine yace baya sonaba to bazan auri kowaba, ya sadaukar da rayuwarshi a kaina, ya kareni a lokacin da nafi tsananin buk'atar neman kariya,
Ya zama garkuwata ya tsare min kimata ya bada ranshi da lfyarshi a kaina, ina sonshi."
Sai kuma ta tashi zaune ta rik'o hannayen yayar tata cikin zubda k'walla murya na rawa tace.
"Ina sonshi, wlh ina sonshi bazan iya son wani d'an namiji ba in ba shiba."
Cikin kad'uwa maryam tace.
"Wai waye ne?."
Da k'arfi tace.
"Ban saniba."
Cikin mmki Maryam ta zaro ido woje kana tace.
"Me sunanshi? Ina gidansu yake? Me sana'arsa?."
Nanma kuka tasa tare da cewa.
"I don't know."
Zuwa yanzu abin ya fara bawa Maryam tsoro cikin tsoro tace.
"To ina yake?."
Da k'arfi tasa hannunta tana dukan kanta tare da cewa.
"Ban sanshi ba, bai sanniba bansan ina yakeba bansan sunanshi ba.
daga sau d'ayan dai dana tab'a ganinshi nanma gabanin magriba ne, to ban sake ganinshi ba."
Nan ta k'ara bawa Maryam labarin had'uwarta da Dalla da yadda Saifuddeen ya taimaketa, dan ganin yadda Maryam ta nuna mata kamar bata gane waye take nufi ba, ta k'arishe mgnar cikin tsananin kuka tace.
"Bansan ina zan sake ganinshi ba, ina sonshi, shine nakeso ya zama mijina wlh in ban aureshi ba bazanyi aureba,
wlh in ban sake ganinshi ba zan haukace."
Tsorone mai tsanani ya rufe Maryam,
cikin zubda hawaye muryarta a sanyaye tace.
"Innalillahi wa Inna'ilaihi rajiun, Zaliha ko dai kinyi gamone, kodai al'janine ba mutun ba?."
da sauri ta durk'usa gaban yayartata cikin kid'ima da jujjuya Kai tace.
"Mutum ne shi kamar ni, wlh ba al'jani bane shima d'an adam ne,
na tabbata da al'janine da ya sake zuwamin koda a mafarki ne.
Ni tsorona bansan wani hali yake cikiba, yana lfy ko sun illatashi."
Wani nannauyan ajiyan zuciya Maryam ta sauk'e sannan tasa hannu ta share hawayenta kana ta sharewa Zaliha nata cikin fuskantarta da kyau a hankali tace.
"Wannan zancen naki ba'ak'i ce dashi gaibuba,
domin tatsuniya ce mai zaman kanta, zancene da hankalin bazai kamaba,
Zaliha ki yarda al'janine ya taimaka miki, in ko mutunne to ya mutu."
Wani irin zabura tayi tare da rushewa da kuka tana jujjuya kai tare da yarfa hannu take cewa.
"Bai mutuba yana raye mutun ne ba aljanba ki gane mana ina jinshi a cikin duk wani bugun da zuciyata keyi."
Ganin yadda ta gigicene yasa Maryam cewa.
"Na game mutum ne kuma yana raye."
Jin haka sai ta koma ta konta rubdaciki tana mai ci gaba da kuka.

Ita kuwa Maryam da sauri ta d'iro daga kan gadon ganin Ya Ameenun yana tsaye a bakin k'ofa bisa dukkan alamu yaji duk batun da sukayi.
tana isa inda yake kawai sai ta fad'a jikinshi tare da sakin sassanyan kuka.
Da sauri ya tallabota dan a duniya Ameenu duk zafinsa baya son abinda zai tab'a mishi salihar matarshi mai tarin hak'uri da biyeyya.
parlour ya fito da ita inda ya ruggumeta da kyau a jikinshi,
jin haka yasa rauninta k'aruwa cikin rawar murya take cewa.
"Shi kenan Ya Ameenu Zaleeha tayi gamo, al'jani ya shiga jikinta.
Zai haukata min k'anwata ya Ameenu kuyi mata Ruqyah kada ya haukatata."
ganin sosai take kukanne ya sashi d'ago kanta bakinsu ya had'e wuri d'aya wani irin zazzafan kiss yake mata wanda dole yasa tayi shiru, har saida yaga ta nitsu kana ya jawota suka zauna kan kujera,
tafin hannunshi yasa yana share mata hawaye tare da cewa.
"Am so sorry my happiness kiyi shiru ba abinda zai sameta sai al'khairi ki daina kuka,
zan mata duk abinda kike so kinji ko Ummu Ayman?."
Kanta ta gyad'a mishi alamun gamsuwa, duk da haka bai bartaba har saida ya sama mata cikekkiyar nitsuwa.

Ita kuwa Zaleeha tuni wani baccin kuka ya kwasheta.


Shi kuwa Raveel koda yaje office ya kasa samun sukuni.
Sai sak'onnin ban hak'uri yaketa tura mata.


Abuja
Amina ce ke zaune bisa sallayarta,
yayinda ta bud'e hannayenta sama Cikin sanyin lafazi take cewa.
"Ya haiyu ya k'aiyum ya ubangijin sammai da k'asai ya rabbil izzati kaine mai rayawa mai kashewa ya Allah ka raya min wannan bawa naka Saifuddeen.
Ya Allah ka bashi lfy, Allah ka jib'anci lamuranshi ka sanya salama da farin ciki a rayuwarshi ya Allah ka cika mishi dukkan buk'atunshi na al'khairi."
A hankali ta shafa addu'ar tare da zamewa ta kwanta a nan bisa sallayar,
tare da jawo wayarta hotonshi dake bisa fuskar wayarta ta zubawa ido. murmushin da yake a hoton sai takega kamar ita yakeyiwa.


Indian Mumbai
A guje nurses da Doctors suka shigo d'akinda Saifuddeen ke ciki sabida ihu da kururuwan da Hayatuddeen keyi.
Ihu yakeyi yana tsalle tamkar yaro kana yana yarfa hannu yana cewa.
"Wayyo Allah na yau farin ciki zai kasheni,
Wayyo ni Hayatuddeen waye zai tayani farin ciki,
Wayyo Ummi na yau ga Hamma Saifuddeen d'ina a zaune da k'ugunshi, ya tashi ya zauna da kanshi ba tare da taimakon kowaba.
Wayyo Adda Rahma Raihana, Raliya d'an uwanmu ya fara zama da kanshi.
Ya Adnan ya Ahmad Bappa Ali ina kuke?."
sai kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login