Showing 165001 words to 168000 words out of 176868 words

Chapter 56 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

azabar k'arfi kanta ta fara jujjuyawa tare da zamewa ta durk'usa gaban Mamansu murya a hargitse tace.
"Bana sonshi, bazan zauna da shiba, wlh mutuwa zanyi in aka had'ani dashi please Mama kiyi wani abu a kai."
Maryam ce ta d'an kalleta a tausashe dan tasan irin abinda Zaleeha keji a ranta tunda itama a dole aka had'ata da Ya Aminu amman gashi yanzu da tayi biyayya tabi umarnin iyayenta tana ganin ribar haka,
duk da zafin zuciya irin na ya Aminu zama yake kamar bawa a gareta,
baya son duk wani abinda zai sata zubda hawaye.
shiyasa a hankali tace.
"Zaleeha kiji tsoron Allah kiyi biyayya ga mahaifinmu zakiga ribar hakan kada ki bari rud'in duniya ya Kaiki ya baroki.
Ku dena yakice Saifuddeen dan nakasarsa dan babu wanda yasan k'arshensa, kuma in baka mutuba to ba'a k'are maka halitta ba,
shimafa bada larurarnan aka haifeshi ba, kaso 95 cikin 100 ba haihuwarsu ake da nakasaba a duniya suke samu. Kaso 5 ne na cikin 100 ake haifarsu da nakasa,
because muma bamu da yak'inin a haka zamu k'are rayuwarmu."
Cikin tsawa da masifa Mama tace.
"Rufe min baki hegiya mara zuciya,
mai mugun fata mu nan in sha Allah lfy lau zamu k'are rayuwarmu.
Kuma wlh wlh muddin ina raye Zaleeha bazata zauna da wannan gurgunba.
Dan ke kinada macecciyar zuciya sun tankwaraki kin zauna a dole to banda Zaleeha."
Cikin sanyi Maryam tace.
"Kiyi hak'uri Mama ki gafarceni in furucina ya sosa miki zuciya."
ita kuwa Zaleeha mik'ewa tayi ganin sunk'i su sarara bare su saurareta,
ficewa tayi daga gidan a guje.

A Cikin gidan kuwa, Anty Aisha ce ta kalli yayun nata cikin kafiya da fad'in gsky tacewa Mama.
"Da hankalinki da tunaninki kike biyewa zugar wacce kin san batayi imani da Allah da manzonsa ba, bare ta yarda da k'addara mai kyau ko sab'aninta."
A zafafe Ruda tace.
"Ke Rebeka ni kike gayawa haka?."
cikin tsuke fuska da tsawa tace.
"An gaya mikin! K'arya nayi ne, imanin gareki tunda har yanzu baki samu tsarkin zuciyaba, kina kafura,
mara lissafi zata zauna tana bin zugarki,
lallai ke yar uwata ce kuma yayata Amman baki da hurimin kirana da Rebeka call me Aisha in bazaki iya ki bari."
A zafafe tace.
"don't call me Rebeka again."
Sai kuma ta juya ta kalli Maryam tace.
"Maryam tashi mu tafi, ni dai ina bayan Baba Malam daga yau kuma zamu fara shirye-shiryen auren nan."
A hankali Maryam ta maida akwatunan duk wurin zamansu,
sannan ta mik'e tabi bayan Anty Shatu kamar yadda suke kiranta kenan...

Mama kuwa da kafurar Yayarta Ruda,
nan sukaci gaba da tubka da warwara,
suna tubke yadda auren Zaleeha da Abdussalam, kana suna warware auren Saifuddeen.

Ita kuwa Zaleeha tana fita kai tsaye (Jonapwd)  ta nufa tuk'in takeyi tamkar wacce zata bar garin.
tana shiga harabar wurin tayi parking, cikin sauri ta fito gaba d'aya ida nunta dishi-dishi suke mata,
kai tsaye office d'in Ishaq ta kutsa kanta sam bata iya amsawa mutanen nata gaisuwar da suke mata.
shi kuwa Ishaq tun tana babban parlour yajiyo mgnar Sani na mata sannu da zuwa so koda aka turo k'ofar office nashi aka shiga yasan itane.
Tana ganinshi kawai sai rauni ya rufe masifarta dan iya tsawon zamanta da ishaq a matsayin yayanta Ahmad take kallonshi ishaq yanada mutunci a ida nunta gashi last time ta surfa musu rashin ɗa'a kuma daga nan yake fushi da ita,
a hankali taja kujerar dake fuskantar wacce yake zaune a kai ta zauna.
sunkuyowa tayi ta kifa kanta bisa glass table dake tsakiyarsu kawai sai ta saki wani irin mawuyacin kuka mai cike da rauni da tarin k'uncin rayuwa.
cikin tsananin mmki Ishaq ya zubawa saitin inda yakejin kukan idanu tamkar yana ganinta.
sai kuma yayi shiru kamar baya wurin yana jin sautin kukanta na ratsa kunnuwanshi.
Kusan tsawon 10 minutes tana kuka,
bai kulata ba, ita kuma bata bariba,
har 20 minutes har ta zarta rabin awa tana kukan bil hak'k'i da gsky.
daga jin kukan kasan daga cikin zuciyarta yake fitowa kukane mai tattare da k'una da tsoro,
sosai Ishaq ya fara jin tausayinta na kamashi ai ko ba komai ita macece kuma mai rauni.
cikin sanyin sauti yace.
"Ya isa, ya isa haka Zaleeha kada ki cutar da kanki."
jin haka sai kukanta ya k'aru cikin kukan murya a raunace tace.
"Malam Ishaq bana sonshi, wlh bana sonshi, na tsaneshi, inada wanda nakeso wanda ya bada ranshi da lfyarshi domin kare mutun cina pleaseeee Ya Ishaq kace mishi ya janye batun aure a tsaka ninmu, wlh muddin akayi auren nan cikin mu biyu dole d'aya zai rasu."
Sosai ya nitsu yana jin kala manta sai ya kuma ji alamun tazo tana durk'ushe a gabanshi a hankali tace.
"Dan Allah Ya Ishaq ka zame min Garkuwa na mana a karo d'aya dai a rayuwa ta,
dana rok'eka abu dan Allah dan annabi kaji tausayi na mana ka rabani dashi kar in rasa raina please ya Ishaq kada ka bari ayi min auren dole."
Sai ta kuma kife kanta bisa d'aya kujerar taci gaba da kuka.
Sosai raunin ishaq ya halarto kan zuciyarshi,
me zai hana ya taimaketa, to amman bari yaji meyasa bata son Saifuddeen, a hankali yace.
"To waye kike son?." murya a raunane tace.
"Ban sanshi ba?."
fuska cike da mmki yace.
"Ina yake to me sunanshi?."
A hankali tace.
"Duk ban saniba sau d'aya muka tab'a had'uwa shiyasa a gidanmu ake cewa wai ba mutun bane al'janine."
Da sauri yace.
"Yes al'janine mana nima haka zance, tunda shi gaibune."
kuka ta kuma sakewa, sai kuwa ta d'ago kanta jin yana cewa.
"To meyasa baki son Saifuddeen?. "
Rashin sani yafi dare duhu shiyasa Zaleeha tacewa Ishaq.
"Nakasasshe nefa shi gurgune kurma ne ta yaya zan aureshi da lfyata gurgunefa ananfa kuke cemin irinsu basa aure."
da sauri ta mik'e tsaye jiki na rawa ta koma gefe dan jin yadda ishaq ya buga table dake gabanshi tare da buga mata tsawa.
"To sai me!? Shi nakasasshe ba mutun bane!? Ko shi nakasasshe baida ikon auran lafiyayyiyar mace!? To wlh Zaleeha kinyi ganganci wannan furucin naki, ni babu taimakonki da zanyi in sha Allah sai Saifuddeen ya aureki ko zaki mutu ne.
Get out of my office!."
Ya k'areshe mgnar da k'arfi tare da mik'ewa tsaye.
wanda saida mutanen cikin babban parlour nan suka jiyosu.
Ita kuwa Zaleeha cikin tafasan zuciya ta juya ta fita dan yanayinshi ya bata tsoro.

Daga nan gidansu Rashida ta nufa,
nan ta tasa Rashida a gaba tana kuka.
Murmushi Rashida tayi tare da cewa.
"Hmmmm Zaleeha kenan to ni mai zance miki,
kin dai san bazan baki goyon bayan ki bijirewa iyayeki ba, in dai k'awancenmu na gsky ne,
sannan da kiketa mai-maita shi nakasasshe ne ke kinada tabbacin a haka zaki k'arene.
Zaleeha kifa farga ki dawo nitsuwarki kin gani ko wlh wlh dani Saifuddeen yace yana so na rantse miki da zatin Allah da hannu bibbiyu zan amshi soyayyarsa,
Zaleeha inafa gaya miki kada kiyiwa kanki sakiyar da babu ruwa, kibi umarnin iyayemu ki samu rabauta duniya da k'iyama in zaki farga ki farga Ki daina wanna yarintar."
Cikin tsananin takaici ta ture Rashida da tasa hannunta tana share mata hawayenta a hatsale tace.
"Sai yau na gane asalinki Rashida, ke farin cikima kikeyi da wannan abun har dariya kikeyi ko?."
Da sauri Rashida tace.
"Tabbas farin ciki nakeyi abinda baki saniba,
ko jiya muna tare da abokan ango, d'azuma na dawo daga can anguwar tasu federal law cos, layin Sabana hospital, wurin shagon Bash wani tela ne.
Can suka kai kayayyakin d'inkinmu na biki naki da namu na k'awaye kuma komai yayi kyau,
anjima kuma zasu zo batun shagulgulan da za'ayi."
Cikin mmki da tarin takaici Zaleeha tace.
"Shegiya yar iska a ina kika sansu?."
Dariya Rashida tayi tare da cewa.
"A wayar wani ɗan kawuna Jabeer naga hoton Saifuddeen sai yake cemin abokinshi,
harma an kai lefe.
to nan nake ce mishi ai mune k'awayen amarya,
kinga daga nan komai yazo da sauk'i mu yanzu shirin bikin mukeyi babu kama hannun yaro.
nice nan na kaiwa telan kayanki yadda zai d'inka komai dai-dai dake."
bazata fa juri jin tatsuniyar Rashida da ɗan kawunta Jabeer da sauran abokan Saifuddeen ba don haka ta zari car key d'inta ta bar gidan.

Ita ko Rashida murmushi tayi tare da cewa.
"Ayyah Zaleeha zuk'ar zuciya da rud'in shaid'an na d'awainiya da ke sun hanaki ganin nagartan Saifuddeen.
Fatana Allah ya sanya al'khairi a aurenku."

Ishaq kuwa Zaleeha na fita ya biyo bayanta ranshi a matuk'ar b'ace,
parking lot ya nufa ganin haka Ado drivarnshi ya biyu bayanshi bud'e mishi marfin motar yayi.
Bayan ya shiga ya maida marfin ya rufe,
sannan ya shiga yaja motar suka fita,
suna hawa kan titin da kyau Ado ya juyo ya kalli uban gidan nashi cikin girmamawa yace.
"Ina zamu je?."
A takaice yace.
"Gidan Saufuddeen."

A parlour'n Ummi ya samu Saifuddeen shi kad'ai,
kamar babu kowa a gidan.
bayan sun gaisa ne da salon yadda suke mgna,
Ishaq ya rubutawa Saifuddeen duk yadda sukayi da Zaleeha yanzu,
yana gama karanta text d'in ya gyara zamanshi kana ya fuskanci abokin nashi cikin lumshe ido yayi wani tattausan murmushi tare da rubuta mishi.
"Cool down my friend.
kada ka damu da duk abinda zatayi."
cikin jin haushi Ishaq fuskaci abokin nashi da kyau kana yace.
"Saifuddeen ka hak'ura da Zaleeha mana tunda ba ita kad'ai bace d'iya mace,
ita mafa macece kamar kowa ya za'ayi wasu na binka kai kana binta tana ci maka zarafi, na gaji Ka rabu da yarinyar nan,
yarinyar da ikirari zata mutu in ka aureta kayi zuciya ka barta mana."
A hankali Ummi ta zame ta zauna a kujerar da Saifuddeen ya baiwa baya, ishaq kuma ba ganinta zaiba.
Gaba d'aya jikinta rawa yakeyi.
Tsoronto d'aya kada k'iyayya tasa Zaleeha ta cutar mata da d'anta, ya zatayi in wani abu ya kuma samun Saifuddeen d'inta d'a mafi soyuwa a zuciyarta d'an da yake k'arar da lokutanshi wurin sama mata farin ciki da kare martabarsu. tuni hawaye na zirya a kumatunta dan tana tausayawa zuciyar d'an nata da Allah ya jarbaceshi da son matar da bata sonshi.

Shi kuwa Saifuddeen kanshi ya jujjuya kana ya fara rubutawa ishaq mgna kamar haka.
"Uhmmm Ishaq ai duk cikekken masoyi zai jure karan tsana.
Zai jure kai kawo da zirga-zirga ako ina.
Kuma bazai nufi masoyinshi da hatsala ba.
Kuma ai ba'a son fushi a so sai dai hak'uri da juriya
domin yin fushi a so alamun rashin nasara ne, in sha Allah
dole ne fa sai Zaleeha ta shigo gidane dolen-dolenta sai taga aikin ginennen tab'on nan da tace sai na shayar da ita ruwan mmki, barni da ita zata gane kurenta!."
cikin mmki Ummi ta zuba musu ido ganin sun tafa kuma ishaq ya saki wani irin shak'iyin dariya.
"Saifuddeen kenan ya iya sarrafa harshe gashi daga fushi yasa ishaq dariya ko meye ya rubuta mishi sai Allah."
Ummi Ke fad'i a ranta lokacin data mik'e ta nufi bedroom nata dan bata son Saifuddeen ya gane taji zancensu.

Ita kuwa Zaleeha daga gidansu Rashida  gidan Hajja inna nufa,
tana shiga kawai ta tasa hajja inna a gaba ta bud'e wani sabon shafin kuka.
Zakariyya ne dake gugun kayanshi dana Ziyada ya ajiye dutsen gugan tare da cewa.
"To yau kuma me aka miki?."
cikin kuka take cewa hajja inna.
"Wallahi bana sonshi dan Allah ki cewa Baba malam yayi hak'uri kada ya min auren dole."
shiru tayi jin hajja Inna ta ja wani dogon tsaki,
kana ta b'alli tsallin goro ta afa a bakinta tare da taunashi,
kai ta karkace tare da cewa.
"To me ruwana a ciki, aure ne dai dole fa sai an aurar dake,
na gaji da zamanki a gidan d'ana."
Dariya sosai Zakariyya da Ziyada keyi sabida abin na hajja Inna ba mutunci.
suna cikin dariyar suka jiyo muryar Hayatuddeen da sauri Zakariyya ya tarbeshi cikin murna suka ruggume juna irin yar ruggumarnan ta gefe.
kana suka zauna bisa 2 sitter.
Bayan sun gaisa da Hajja Inna ne Ziyada ta gaida Hayatuddeen cikin mmki Hayatuddeen yake tambayar meyasa Zaleeha kuka,
Zakariyya ne yayi dariya tare da cewa.
"Wai kuka take dan za'a mata aure."
Dariyar shak'iyanci sukayi mata cikin dariyar Hayatuddeen yace.
"Ato yarinya da kin san kina tsoron auren mai yasa zakisa gaye ya turo iyayenshi."
Ziyada ce ta d'an kalleshi cikin yanayin d'an sabonta dashi tace.
"Ya Hayatuddeen ai bata son mijin ne shiyasa take kuka auren dole za'ayi mata."
da sauri ya matso kusa da Zaleeha wacce keta kuka hajja Inna kuwa nata aikin auna mata harara, cikin sanyi yace.
"Allah sarki Adda Zalee gsky ba'ayi miki adalciba a dai wannan zamanin mace kekyawa big girl kamarki ace an miki auren dole,
gsky dole kiyi kuka."
jin haka yasa Zaleeha fuskantarshi cikin kukan tace.
"Kuma ina da wanda nakeso sannan su had'ani da wani can banza ginennen tab'o."
kai ya jinjina mata tare da cewa.
"To meyasa bazakuyi mgna ta fahimtar junaba keda shi,
ki gaya mishi kinada wanda kikeso, kice mishi koda ya aureki bazai ji dad'in zama da keba,
in ya amince ya hak'ura shine nan kin huta in ya kafe ya nace kuma kiyi hak'uri kibi umarnin iyayenki."
Cikin kuka tace.
"Na tsaneshi bana sonshi ta yaya zan auri nakasasshe alhalin da lfyta."
shiru tayi ganin yadda a take fuskar Hayatuddeen ta canza launi da yanayi cikin had'e girar sama da k'asa mik'ewa yayi ya matsa gefenta tare da cewa.
"Zancen banza kenan, ashema baki da hujja, shi nakasasshe ba halittar Allah bane, ko a zatonki Nakasa kasawa ce,
aikin banza d'an adam da bai san k'arshenshiba yace yana kyaran larurar wani."
Gaba d'aya ran Hayatuddeen ya b'aci sosai sai yake tuno wata k'ilfa wata ran ayiwa Hamma Saifuddeen d'inshi irin wannan cin zarafin, haka kawai kalamanta sukayi masifar tayar mishi da hankali,
Hajja Inna ce tayi dariya tare da cewa.
"Ato ai duk mai bin bayan Zaleeha zai shak'i takaici, yo wani nakasasshen ma ai yafi mai cikar halitta haiba."
Ita kuwa Zaleeha cikin kuka tace.
"Bazaku gane bane. Gurgu nefa akan wheelchair yake rayuwa, kuma kurmane bayaji baya mgna."
Dam-dam zuciyar Hayatuddeen ya bada wasu tagwayen tarnaki mai cike da fargaba cikin zargin kai anya kuwa wannan bada Hammanshi take ba, cikin tsananin fargaba baki na rawa yace.
"Uhmmm me sunan shi ne!?."
cikin tarin tsanar tsuna taja wani dogon tsaki tare da mik'ewa kana tace.
"Wai Saifuddeen n!!!."
da sauri Zakariyya ya mik'e tsaye tare da cewa.
"Hamma Saifuddeen.
Shi kuwa Hayatuddeen cikin k'arfi ya fizgo hannunta tare da zaro idanunshi da sukayi jazir tuni hawaye na shatata a kumatunshi har kan gemunshi cikin rawan murya yace.
"K'arya ne wallahi Hamma na ba nakasasshe bane, domin nakasarsa bata zame mishi kasawa ba,
Ke da kike zagin nakasarsa kinada tabbacin naki lafiyar ne, da har kike inkarin ke da lafiyarki, to wlh yanzu kika fara kuka ko zaki mutu sai kin zama matar kurma kuma gurgun nan,
D'an uwane shine jigon rayuwar ahlinmu."
Sai kuma ya sake mata hannu ya koma ya zauna, Zakariyya ma tuni hawaye yake zubdawa, dan sai yanzu ya gane ashe Hamma Saifuddeen ne wanda yayarshi Zaleeha keta ƙi.
hakama Ziyada hawaye take zubdawa,
Hajja Inna kuwa cikin mmki tace.
"Hayatu, ashe ma Saifuddeen kyakkyawa ne ta samu har take rigima.
Wlh ni ban saniba."
Cikin zubda kwalla shima Hayatuddeen yace.
"Wlh Hajja Inna nima sai yanzu na gane data kira sunanshi da yanayin nakasarsa kuma,
na tuna ance min sunan matar da aka bashi Zaleeha ne."
ita kam Zaleeha juyawa tayi ta fita jin ƙaninta Zakariyya na cewa.
"Wlh nima ban san akan Hamma Saifuddeen bane take wannan haukan da ko inda take bazanma kallaba."

Hajja Inna ce ta katsesu da cewa.
"Ai kuwa ko mutuwa zatayi sai ta aureshi."
Sai ta kuma kalli Hayatuddeen cikin rarrashi tace.
"Kayi haƙuri kaji ko Hayatu, dan Allah kada ka gayawa Umminku da yayunka wannan batun in sha Allah Zaleeha zata tanƙwaru."
Kai ya gyaɗa mata alamar to,
sai ya kuma Kalli Zakariyya tare da cewa.
"Dama nazo nefa muje gidansu Imran muyi batun dinner ɗin da za'ayi a bikin ne, ina son mu tsara fita ta musamman a wurin," cikin bada ƙarfin guiwa Zakariyya yace.
"To muje, danko abu namune maganin a kwaɓemu."

Daga nan suka tafi gidansu Imran ƙanin ishaq.

Ita kuwa Zaleeha abu ya cakuɗe mata komai ya birkice mata,
Yanzu ba mai bin ta kanta ta lura Aunty Lubna da Zakariyya basu damu da dmuwar tata ba

Haka yasa dole ta ƙudurci son haɗuwa dashi ido da ido ayita ta ƙare.

A lissafi dai yau saura kwana biyar ne auren.
ganin har danginsu na Dukku sun fara zuwane ya ƙara tayar mata da hankalin.
Gashi haka nan take jin kamar ana ingzata da zugata kan tayi wani mummunan abu.
Shiyasa yau tunda safe taketa tura mishi text akan yazo gidansu zasuyi mgna mai mahimmanci ganin har yamma ba amsa ne yasa ta kira Ishaq bayan ta tuttura mishi saƙo dan Allah ya amsa kiranta,
Yana d'agawa cikin rawan murya alamun zata fara kuka tace.
"Dan Allah Malam Ishaq na rok'eka da manzon rahma kace yazo gidanmu inada mgna dashi."
cikin danne dariyarshi da sai yanzu kalamanta na wai sun ce mata irin larrarshi basa iya aure dariyar ya ɗan danne kana yace.
"Yaushe kike son yazo?."
Da sauri tace .
"Dan Allah yazo yau. Ban san in da zan sameshi ba da naje na sameshi."
wani munafukin murmushi ishaq yayi sannan yace.
"Ki duba hanyarshi zuwa bayan sallan isha."
Da sauri tace to kana ta katse kiran,
a take ta kira Bilkisu dan tasan itace zata tayata ci musu zarafi ta yadda sai sun tsani kawunansu ma, aiko Bilkisu najin shirin Zaleeha tace gata nan zuwa.

Bayan sallan isha, Saifuddeen ne zaune bisa wheelchair ɗin shi kalar ruwan toka mai azabar kyau da sheƙi, a zahiri yadda yake caccanza sutura da ɗaukan wanka to hakama mota da wheelchair ɗinshi suma masu kyau da tsada ajin forko yake hawa hakama huluna da takalma,
Sanye yake cikin wani d'anyen yadin voyel mai kalar shud'in sararin samaniya, sai kuma ratsin fari fari tamkar gajumare,
an ƙyanƙyasawa rigar aiki da surfani mai ruwan garai-garai,
hannun rigar guntu ne masu zagayen zaren garai-garai d'in daga bakinsu, hannun yayi cib damatsan hannunsa da suke farare k'al-k'al masu yalwar gargasa mai tsawo da shek'in bak'i mai d'aukar hankalin duk wanda ya gansu sun zauna cib,
hular damanga ya kafa a kanshi irin kafin nan da ake cewa baruwanka da duniya bi ma'ana ya d'an tura hular tayi baya,
hular farace sai ratsin shud'in zare,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login