Showing 90001 words to 93000 words out of 176868 words

Chapter 31 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

***
Asalin ahlin Zaleeha.

Malam Bashir Suleiman Dukku asalin haifeffen garin Dukku ne gaba da baya,
Malami ne wanda yakeda cikar haiba da kamala,
Su uku ne a wurin iyayensu babban yayansu Malam Umur sai shi Malam Bashir sai k'anwarsu Goggo Maryam wacce itace akayiwa mai suna da Maryam yayar Zaleeha,
Malam Umar yanada matashin hud'u reras Allah ya azirtashi da tarin yara sama da talatin,
Malam Umar mutum ne mai tsananin zafi da fad'a yanada tsananin kafiya shi kaifi d'aya ne in yace eh tofa eh dince har gaban abadan babu wanda ya isa ya karya mishi doka muddin ya kafa dokarshi,
mutun ne wanda in yayi gyaran murya koda kajin gidanshi suke nitsuwa,
Allah ya shirya mishi yaranshi yayinda Aminu shine babban d'anshi kuma shine ya gado zafin zuciyar Malam Umar da kafiyarsa kab,
sabanin Baba Malam shi kuma yanada tsananin nitsuwa da kauda kai da hak'uri ammanfa in aka k'ureshi yafi Malam Umar zafi da tsanani,
Mahaifinsu ya rasu, shiyasa suka k'auro suka dawo Gombe sun dawo gombe ba juyama Allah yayiwa Malam Umar rasuwa daga nan komai na kula da gidan ya dawo hannun Aminu da baba malam da Ahmad.
Goggo Maryam kuwa tana dukku gidan mijinta.

Hajia Aisha Mamy kenan itace matar Malam Bashir ta forko wacce sukayi auren lalle da lalle,
wacce Allah ya azurtasu da d'ansu Ahmad daga shi kuma bata sake samun haihuwaba.
Ahmad nada shekaru goma a duniya,
lokacin su Malam bashir suna shiga k'auyukan k'abilun gombe da kewaye suna da'awa,
kuma Alhamdulillahi kafurai sunata musulunta suna shiga addinin musulunci sosai,
a cikin hakane sukaje wani yanki kaltingo na k'abilun tangalu nan suka musuluntar da mutane da dama maza da mata a cikinsu akwai wacce ta musulunta da sunata Soro data musulunta ta zab'i a saka mata Halima,
sosai iyayen Halima suka tada hankalin kan musuluntar da tayi daga bisani sukayi mata barazar zasu kasheta,
ganin ta kafe ne kuma bata tsorita ba sai suka koreta,
to daga ranar tayi ta bibiyar malamai mata dasu Malam Bashir Sulaiman Dukku ke zuwa dasu yin da'awa,
dole suka d'auketa suka dawo da ita cikin Gombe suka ajiyeta cikin gidan da aka gina da isilamiya domin irinsu,
nan ta zauna tayi ta karatunta daga bisani akazo batun aure nan ta kafa ta tsare tace ita Malam Bashir takeso.
Allah yayi da rabo a tsakani cikin k'ank'anin lokaci Malam bashir ya sanarwa iyayenshi da matarshi Hajia Aisha duk sai suka bashi k'arfin guiwa dan dama ita Mamy tana buk'atan ya k'ara aure.
Nanfa akayi auren Baba Malam da Halima Mama kenan,
inda ya sai gida a ceceniya ya ajiyeta a nan sabida lokacin suna Dukku ya zama matanshi biyu,
in yazo Gombe ga Halima amarya in ya koma dukku ga Mamy uwar gida mace mai tarin hak'uri da tawakkali.
Zuwan Halima gidan keda wuya Allah ya azurtasu da haihuwa yau da gobe jibi da gata.
saida ta haifi 'yara shida Habu, Maryam, Zaleeha, Zakariyya, Ziyada , kana autarsu Zahira .
Zaleeha na yawan bin Baba Malam suje Dukku dan Mamy na matuk'ar sonta da kula da ita shiyass Zaleeha da Habu da Maryam sun zauna a Dukku sosai sun samu inƙantacciyar tarbiya a wurin Mamy kasan cewar haihuwar kunika Mama takeyi sai hakan ya zame mata kamar hutune da sauk'inta,
Mamy kuwa tasha wuyan yaran nan tamkar itace ta haifesu da cikinta dan ko Ahmad bata sha wuyan rainonshi ba kamarsu Habu Maryam Zaleeha kuma yaran suna masifar sonta hakan itama take matuƙar sonsu,
Zakariyya nada wata biyu ta samu cikin Ziyads,
so randa ta haifi Ziyada a ranar aka yaye Zakariyya daga nan Baba Malam ya d'auki Zakariyya ya kaiwa Innanshi,
lokacin babansu ma na raye daga nan Zakariyya ya zama tamkar d'ansu gata da sakalci dai na goyon kaka yana shanshi,
sai dai duk jikokinsu sunfi son Ahmad da Aminu sai Zakariyyan da Maryam .
Ziyada nada wata sha uku aka aihi Zahira auta
daga nan ita itama haihuwar ta tsaya taci gaba da rainon Zahira da Ziyada wacce takeda nitsuwa irinta Maryam,
daga baya ta kafa nacin a dawo mata da su Maryam shi kuwa baba malam yace takau bazai d'aukosu ba,
amman zai kawo mata Habu tunda ba d'a namiji a gabanta ko d'aya,
to fa shine mafarin fara gane halin Halima dama inkiyarsu ce Halima hali dubu babu na zab'e.

bayan shekaru kad'an babansu Malam Bashir ya rasu daga nan Malam Umar ya k'auro ya dawo cikin gombe a gidanshi daya gina a Fantami yaso ya d'auko inna amman sai tak'i a cewarta bata son tayi nesa da d'iyarta Goggo Dada,
lokacin kuwa tuni Ahmad baya k'asar yana k'asar Italy inda nan yayi karatunshi har ya zama cikekken pilot Aminu kuwa kuwa zama babban soja,
koda Baba malam ya sanarwa innansu cewa zai k'aura shima zai koma cikin gombe fir tak'i da kyar dai da sud'in goshi ya lallab'ata suka k'auro suka dawo gombe nan suka zauna a nan gidanshi na ceceniyan bayan shekaru kamar biyar lokacin tuni Ahmad ya taka k'asa yayi kud'i sosai,
Ahmad yana tsananin son mahaifinshi da k'annenshi baya son duk wani abu da zai tab'a mutuncin mahaifinshi yana tsananin tausayawa da son Mamynshi su Zaleeha kuwa jinsu yakeyi har cikin k'ok'on ranshi kusan shine yake musu komai na karatunsu.
To sanadin hakane Halima ke d'an ragarwa Mamy kisan mummuk'en da takeyi mata,
musamman da taga Ahmad ya sayi k'aton fili a New G. R. Aka tsantsara musu gida na gani na fad'a suka koma can kuma yana yiwa yaranta hidima.
Inna kuwa tace ita dai a barta a ceceniya ita da Zakariyyanta a kuma bata Ziyada acewar yanayin unguwar yana tuna mata k'auyensu badon Mama tasoba sai dan Dole Zoyada ta koma gaban fitinanniyar tsohuwar injita da faɗi.

Ana cikin haka Baba Malam ya had'a auren Aminu da Maryam dan lokacin Malam Umar ya rasu to yana son k'ulla igiyar zumunci tofa anan Halima ta fito da asalin halinta.
Gashi zuwa lokacin iyayenta duk suna ji da ita tunda yanzu tanada wadata sanadin Ahmad kuma tana kasuwanci in zataje garinsu zai bata kud'i ta musu ihsani.

Sosai taso ta zuga Maryam sai kuma tayi rashin sa'a Maryam rainon Mamy ce sai tabi umarnin mahaifinta.

Daga nan kuma ta tsananta bak'in halinta

Yanzu su Zakariyya da Zahira da Ziyada ne suka rege suke karatu Habu da Maryam da Zaleeha duk har aiki sukeyi.
kab cikin yaran kuma Zahira ce munafukar da ta gado bak'in halin uwartasu da k'abilancin ta.
to kuma Zaleeha na shiri da Zahiran fiye da Ziyada dan ita Ziyada irin masu shiru-shiru d'innan ne sosai,
kasan cewar duk yaran da gefen babansu suke kama shiyasa sukayi kyau mai d'aukar hankali.
Shiyasa kuma Halima take jin kanta da yaran take nunawa Mamy rashin d'a'a dan ma yaran basu biye mata.

To yanzu kuwa Zaleeha ce kan ganiyar budurci tana shawaginta son ranta,
tana had'a gwara kan maza a cewarta sai ta duk mai nuna mata barazana da kuɗi ko wani matsayi baya ranta
duk kud'in na miji baya gabanta.
Tace ita soyayyar gsky zatayi duk wanda zata aura take kuma son ya mata tafi son miji jarumi mai tausayi da taumakon na ƙasa dashi kana har ranta tana son kekyawan miji bata son mummunan miji a ranta
Wannan kenan sune ahlin Zaleeha...
***
Ita kam Zaleeha sam bata wani damu da k'a'idar da aka bataba don ganin tsawon lokacin da aka bata takeyi kamar bazai zoba,
so bata wani damuba asalima duk damuwarta da tunaninta a kan son gano ina wanda ya taimaketan yake.

Bayan ta gama shirin baccinta ne,
tazo ta zauna bisa gadonta, ta ajiye system enta da wayarta a gefe,
da niyar had'e muryoyin wadanda tayi hira dasu yau a kaltingo,
kuma sai tayi shiru ta zuba fuskar System en idanu ko k'ibtawa batayi,
ta kai tsawon 5 minutes a haka kana taja dogon numfashi tare da lumshe ido cikin sanyin murya tace.
"Waya sani ma ko sun kasheshi ne?." sai kuma tayi maza ta girgiza kanta tare da cewa.
"Ya Allah ka kare minshi ka sake gaddara haɗuwata dashi."
sai kuma tace.
"To in ma yana raye ta ina zan ganoshi bare in mishi godiyar taimaka min da yayi,
ba abinda na sani a kanshi suna ko anguwa ko aiki ko dangi ko abakanshi bare in mik'a godiyata a gareshi koda a gidan radionmu,
ko menene sunanshi? ta yaya zanyi cekiyarshi ta ya zan ganoshi a faɗin duniyar nan?."
bud'e idanun tayi a hankali kana ta sharte hawayenta dan tabbas ta tuno lokacin da zata fito daga cikin sitadiyon d'in taga sun caka mishi wuk'a a bayanshi, da sauri ta kuma rumtse ido hawaye na zuba kana tace.
"Allah ya isan mishi, Allah zai saka mishi, mugayen banza azzalumai Allah zai saka mana."
sai ta kuma ture system en kana ta zame ta konta,
tana mai zubda hawaye a haka bacci ya saceta.

Dalla kuwa wani babban d'an kalarene wanda ya addabi birnin gombe da kewaye muddin yaga mace ko wacece ita inda ta mishi zaisa yaranshi su kamo mishi ita ya biya buk'atarsa da ita,
Dalla ya addabi garin gombe yayinda duk naci da k'ok'arin hukuma basu tab'a kamashi ba,
yana kuma da d'aurin gindin wani manya da suka medashi d'an bangar siyayasa shiyasa yake cin karensa babu babbaka babu wanda ya isa ya taka mishi birki.
To a yanzu dai babu 'yarinyar da yake cike da cikinta in ya kamata zaiyi mata Dalla-dalla sai Zaleeha,
sai dai shima a sashinsa ana shirin fitar dashi woje dan yana jinyar raunin da Saifuddeen ya ji mishi a gabanshi wanda yake sashi firgita dan gaba d'aya alamu suna nunawa kamar joystick d'inshi zata mace,
shiko fatanshi koda zata mace tayi hak'uri har sai ya rarake Zaleeha a cewarshi...

***
A nan Abuja kuwa

Su Ummi kuwa suna shiga Hayatuddeen yayi saurin nufar gadon da Saifuddeen yake konce,
yayinda shiko Saifuddeen ya mik'owa mishi hannu alamun yazo,
da sauri ya ruggume k'anin nashi kana yasa hannu ya kamo hannun Umminshi dake tsaye tamkar ta d'agoshi,
tuni hankalinta ya k'ara konciya ganinshi konce cikin haiyacin shi,
Ahmad kuwa matsowa yayi gafenshi yana jan yatsun k'afanshi yayinda Ishaq kuwa yake mik'o mishi hannu ganin haka yasashi saurin sakin hannun Ummi ya kamo na Ishaq,
wani sassanyan murmushi sukawa juna,
ita kuwa Ummi kanshi ta fara shafawa tare da cewa.
"Alhamdulillahi Babana jiki da sauk'i ko?."
kai ya jinjina mata tare dasa hannu ya d'an ture Hayatuddeen wanda tuni yaketa zubda hawaye dan tuno bayanin da Dr Aliyu ya yi musu na nakasar da yayan nashi ya samu.
Ita kuma Ummi hawayenta take ta son medawa dan tasan in Saifuddeen yaga tana kuka hankilinshi zai tashi.
Shiko Saifuddeen hannu yasa yana sharewa Hayatuddeen hawaye fuskarshi kana yasa hannu ya zaro woyar shi dake aljihun Hayatuddeen in,
juyota yayi gareshi,
rubutu ya d'anyi kana ya mik'awa Ummi, da sauri ta amsa dan tasan ta wannan hanyarce suke mgna dashi.
Murmushi tayi gani abinda ya rubuta.
"Ummi ki cewa Hayatuddeen ya bar kuka ya zama jarumi, ki tuna mishi yanzufa ya girma ya rage sakalci, ki sanar mishi jikin Hamma Saifunshi da sauk'i, kice mishi in dai yana son in sai mishi mota to ya dena kuka."
cikin samin sauk'in fargabanta ta kalli Hayatuddeen tare da mishi bayanin Hamman nashi, da sauri yasa hannu ya goge hawayenshi tare da cewa.
"Hamma nayi shiru na bar kuka kaji ko zaka saya min motar ko?."
kai ya gyad'a mishi alamar yaji fuska d'auke da murmushin da yasa dimples nashi duka huɗu suke lotsewa, kana ya amshi wayar tashi ya shiga message ya kuma rubutu kana ya turawa ishaq ta inbox nashi,
text d'in na shiga wayar ishaq tayi wani sautin mgna da sauri-sauri hakan yasa ya gane Saifuddeen ne ya turo mishi text alamun yana mishi Magna,
Dr Batulu kam yar kallo ta zama sabida ganin yadda abota take tafiya tsakanin kurma da makaho kuma har suke Magna da juna kuma har kowa ya fahimci d'an uwanshi.
shiko Ishaq lallatsa woyarshi yayi, jim kad'an ya karata a kunne sai ga wannan Magna sauri-sauri ya karanta mishi abinda Saifuddeen ya rubuta mishi kamar haka.
"Ishaq ya su Umma ya Amira da jiki?."
gyara tsayuwa Ishaq yayi tare da fuskantarshi yace.
"Alhamdulillahi suna lfy, sunce in gaidaka da jiki, kana Amira jiki yayi sauk'i har an sallamesu, kai yanzu ya jikin naka?."
rubutu ya kumayi kana ya turawa ishaq.
"Alhamdulillahi jiki da sauk'i, ina amsawa. ya an kai sak'on gidan marayun nan?."
Masha Allah ishaq yace tare da cewa.
"Eh an kai."
daga nan sai kuma Ahmad yace.
"Suifuddeen ya jikin?." murmushi yayi tare da rubuta mishi.
"Alhamdulillahi jiki da sauk'i yaushe ka dawo daga Lagos?."
bayan ya karanta rubutun ne yace.
"Jiya na dawo."
sai ya kuma kalli Dr Batulu sai ya d'an dungula hannunshi ya mata irin gaisuwarsu sabida ya tabbatar ta haifi kaman shi.

Ummi kuwa cikin kula ta shafa kanshi tare da cewa.
"Kai Hayatuddeen bashi wuri ya tashi mana ya samu ya watsa ruwa."
shiru duk sukayi sabida ganin kamar Ummi bata san menene ainihin matsalarshi spinal cord injury ba, ita a zatonta zai iya tashi da kanshi a yanzu haka a taken,
shima Saifuddeen da yanada halin boy'e mata daya boye mata gskyar laturarshi sabida gudun tashin hankalinta.
Itako Ummi sai juyawa tayi ga Ahmad kana tace.
"Ahmad tallefeshi ka kaishi bathroom kasan Saifuddeen da yawan son shiga ruwa."
Dr Batulu ce tayi saurin cewa.
"Ummin Saifuddeen kin mata bazai iya tsayuwa bane, kin mance ya nakasane kike ta cewa a tasheshi yaje yayi wonka, ai an mishi wonka d'azu kafin azo a bashi mgna, a yanzu haka bama zai iya tashi zaune bama sai mu zuba ido mu jira har lokacin da aka mishi aiki ko Allah zaisa a dace, ya tashi ya.....!



Wasa farin girki Ana wata sai ga wata.



By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:53 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAKASA BA KASAWA BACE*


*PAGE 19*


NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


~Wannan shafi nakune Nakasa ba kasawa bace fans 3 kuyi yadda kuke so dashi~

_Turn Katim mtn na ɗari ukku rak ta wannan no 09097853276 ko kuma ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa_


~Hmm Free page dai suna gab da ƙarewa saura ƙaɗan in rufe, hanzarta biyan ɗari uku kacal dan ka/kici da karantashi har ƙarshe~


Yauwa fa ba editing zakusa typing errors


"Ranan tashinsa tsaye sai dai muna tsammanin samun lfyarshi a ko wanne lokacin."
tuni idanun Ummi ke kwaranyar da wasu zafafan hawaye masu tarin k'una zuciyarta tamkar zata faso k'irjinta ta fito woje dan tsananin firgita da tashin hankali uwa uba tsananin tausayi gudan jinin nata.
kukanta ya k'ara tsananta ne jin tafin hannunshi bisa hab'arta yana share mata hawayen tare da jujjuya mata kai kana yana wani irin sihirtaccen murmushi mai cike da zallan tawakkali da yarda da k'addara,
Hayateddeen kuwa kanshi ya kife bisa pillow da kan Hamma Saifunshi ke konce goshinshi ya manna da hab'ar d'an uwan nashi kuka yakeyi mai cin rai da cushe farin ciki murya na rawa yake cewa.
"Dukkan jarrabobinmu sukan riskemu da tsananin zafi da tarin k'una, ko yaushe ciwo ko mutuwa basa zabi duk inda Allah ya aikosu nan suke zuwa, mutuwa ta yashe mana jigonmu, yayinda kowa ya yanke k'auna sai ubangiji ya sauk'ar da k'udurarnsa bisa d'an uwana da duniya ke ganin bama zai amfanin kanshi bama bare ya amfane mu, Hamma Saifuna ya karya zaton mutane da suke ganin nakasa kasawa ce,
ya tashi ya tsaya kaida k'afa ya shiga rana dare zafi sanyi ya ratsa duhu da ruwa da iska na damuna dan tsaida hawayenmu ya zame mana Garkuwa kana bongo abin jingina jigonmu abin al'faharinmu."
sai ya kuma taso ya kalli Hamman nashi da yaketa juya musu kai murya na rawa yace.
"Wallahi! Wallahi!! Wallahi!!! da ana canza ciwo da na canzashi ya dawo kaina, da ciwo bazai kuma rab'ar d'an uwana ba da ina da dama da na tsare maka dukkan wata cutar da zata kai ga tab'aka bare ta nakasa mana kai."
Ummi kam ta kasa cewa komai sai sunkuyar da kanta tayi k'asa tana zubda hawaye tare da ambaton Allah.
Shiko Saifuddeen jawo Hayatuddeen yayi bisa k'irjinshi ya rink'a shafa kanshi cikin alamun lallashi kana ya d'auki woyarshi da d'aya hannun rubutu yayi mai yawa ya mik'a wayar ga Ummi.
ba tare da ta kalleshi ba ta amshi woyar,
sabida hawayen dake kwaranya a idanunta yasa take ganin rubutun bibbiyu d'ad'd'aya rumtse idonta tayi hawayen da suka cika mata idon suka zubo sannan ta fara ganin rubutun a dai-dai kana ta fara karanta abinda ya rubuta mata
"Ni kam Saifuddeeen bani da wani ciwo da zai firgitani koya tayarmin da hankalin a duniya, kamar yadda ganin hawayen Ummi na da k'annena zai sani d'imuwa, zuciyata na k'untatuwa in naga hawayenki,
Ya Nuruddeen ya bar komai a hannu na bisa ya k'inin zan hana idanunku zubda hawaye,
ya Nuruddeen ya shaida min nakasa ba kasawa bace, ya gina min zuciyata da rayuwata ta yadda zan iya zame muku

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login