Showing 117001 words to 120000 words out of 176868 words

Chapter 40 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

yayi kan Hamman nashi wanda tuni likitoci sun zagayeshi,
yayinda suma duk fuskokinsu ke cike da farin ciki.
Wani Irin sassanyan rugguma yayiwa Saifuddeen sai kuma ya fashe da wani irin kuka wanda daga kaji kasan daga cikin zuciyarshi kukan ke fitowa.
Ganin haka yasa Saifuddeen ruggumeshi da kyau tare da d'an bubbuga bayanshi kana ya d'agoshi ya share mishi hawayenshi tare da mishi alamun.
Shin irin godiyar daya dace yayi Allah kenan?.
gane hakan ya sashi yin sujhadar shukur da sauri,
wanda kafin ya d'ago daga sujjadar tuni an tura gadon da Saifuddeen ke kai an shiga dashi wani d'aki na musamman.

Ummi kuwa duk abinda Hayatuddeen keyi da fad'i tanaji,
Lokaci d'aya hawayen farin ciki ya rufeta,
cikin tsananin happy ta sanarwa Raliyya abinda taji,
ruggume juna sukayi dan tsananin farin ciki,
daga nan Raliya ta fita a guje side d'insu ta nufa,
tana shiga ta samu ya Ahmad d'in baya parlour da gudu ta kutsa kai bedroom nanma baya ciki.
Jin motsin ruwane yasa tayi saurin bud'e k'ofar bathroom d'in,
hangoshi tayi k'asan shower yana tsaye ba komai a jikinshi,
cikin wani irin tsalle ta fad'a jikinshi dan ta mance cewa wai gudunshi tayi.
Da sauri ya ruggumota ganin yadda taketa tsalle kawai sai yaga ta fara mammanna mishi kiss tako ina najikinshi.
Sam ta kasa cewa komai ganin haka sai ya fara zame mata kayan jikinta,
bata bi ta kanshi ba bare ta hanashi sai ma k'ara mak'aleshi tayi cikin fizgo mgna tace.
"Al'bishirinka Ya Ahmad."
cilla rigarta gefe yayi tare da had'e jikinsu wuri d'aya kana yace.
"Goro fari k'al."
kiss ta manna mishi a goshi sannan tace.
"Jikin Hamma Saifuddeen da sauk'i ya shida kanshi ya tashi zaune ba taimakon kowa."
Wata iriyar amintacciyar rugguma Ahmad yayi mata tare da giggicewa gaba d'aya ya abka mata,
bata da zabi dole ta karb'eshi a yadda ya zo mata,
mgna d'aya sukayi ta maimaitawa juna,
"Hamma Saifuddeen ya fara workewa yana zama da kanshi."
shi kuma sai yace.
"Alhamdulillahi ya Allah mun gode maka ka nuna mana ranar da zai kuna tsayuwa da sawunshi."
A haka dai sukayi ta kabta nanayensu.

Ummi kuwa wayarta ta d'auka ta gaya dukkan 'yan uwa da abokan arziki.

Adda Rahma kam kawai sai taje gaban surkarta tana kuka tana sanar da ita, cikin kula tace.
"A a Rahma to ai wannan abin farin cikine bana kukaba Allah zamu godewa."

A gefen Raihana ma haka abin yake,
dan ita cewa ma tayi dole Saminu ya kawota gida gombe.

Su Salisu, Mudassir, Warisu, da Bappa Ali kuwa duk Ahmad ya sanar dasu.

Ummi da kanta ta kira Ishaq ta sanar mishi.


Kai wannan rana wannan safiya tazowa da masoyan Saifuddeen da daddad'an labari da sanyin safiya.

Kafin zuwa shabiyu duk makota da 'yan uwa anata zuwa yiwa Ummi barka.
Bappa Alima yazo da Aunty Nina da Goggo Dada maman Ahmad,

Shi kuwa Hayatuddeen
sanin bazasu barshi ya shiga bane ya sashi komawa ya d'auki wayarshi,
aifa kusan a Jere a jere kiran abokan Hamma Saifuddeen da k'annenshi ke shigowa wayarshi,
Haka ya zauna yana musu cikekken bayani yadda komai ya faru,
sai ya k'ara da ce musu yanzu an shiga dashi wani d'akin.

Haka dai yayi ta zaman jira,
Abu wasa-wasa har azahar ba'a fito da Saifuddeen ba,
Ganin haka ya kira Dr Aliyu ya sanar mishi abibda ke faruwa,
sun gama mgna da Dr Aliyu kenan sai ga Dr Acash prasat ya shigo inda yake cikin tsananin jin dad'i ya ruggume Hayatuddeen kana ya jawoshi suka zauna cikin kula yace.
"Hayatuddeen jinya tayi kyau komai yana tafiya yadda mukeso Alhamdulillahi yanzu alamomin samun sauk'i sunata k'ara baiya a wurin d'an uwanka,
tun d'azu muna tare a kanshi duk wani bincikenmu yana bamu tabbacin kaso saba'in cikin kaso d'ari na cutar ya worke a koda yaushe Saifuddeen zai iya tashi tsaye da sawunshi.
Yanzu kuma Alhamdulillahi zai iya tashi zaune daga konce,
kuma zai iya juyawa hagu da damanshi.
Sannan zai iya durk'usawa kan guiwowinshi,
kai nan gaba kad'an ma zai iya sunkuyawa,
shine zatonmu a binciken da muketa gudanarwa a kanshi.
So yanzu ka kwanrar da hankalin ka koma masauk'inka dan sai gobe zaka kuma ganinshi."
Cikin gamsuwa da jin dad'i Hayatuddeen ya gyad'a mishi kai tare da cewa.
"Thanks Doctor."
sai ya mik'e cikin jin dadi har zai fita sai Dr Acash ya jawo hannunshi gaban wani window ya kaishi tare da cewa ya lek'a.
Hammanshi ya hango cikin wata na'ura mai girma dan k'afafunshi kadaine a woje sai kanshi kad'an.

Cikin bashi k'arfin guiwa Dr Acash yace,
"Wannan shine taimako na k'arshe da akeyi masu irin larurarsa,
Yanzu sai in an fiddashi sai bayan, wata shida za'a sake sashi,
so nanda one month za'a sallameku,
in zaku iya duk bayan 6 months sai yazo a dubashi,
a k'ara canza mishi drugs d'inshi.
So ka kontarwa iyayenku hankalin kada wani yace zai zo."
Tofa wannan abu shine Noor ala noor haske kan haske,
sosai bayanin ya kontarwa Hayatuddeen hankalin.
Shiyasa cikin k'arfin guiwa ya koma masauk'inshi.

A ranar dai kam wannan family sunyi matuk'ar shiga farin ciki.
Musammam Ummi da Hayatuddeen ya mata bayanin likita, kawai sai takeji kamar bata da wani sauran damuwa a duniya.

Hakama Dr Adnan da yaji bayani a bakin Dr Malik Khan sosai ya samu konciyar hankalin.

Ahmad kuwa a ranar ya nemo ma'aikata sukazo suka gyara side d'in Hayatuddeen dan Ummi tace anan Saifuddeen zai zauna,
So an fasa duk wani wuri mai d'an tutu ko steps d'in da zai hana keken weelchair gangarawa da wucewa a sauk'ak'e.
Sosai aka gyara side d'in.

A washe garin ranar Ahmad yasa aka kawo mishi gadon samfarin royal bed kana da kujeru suma royal d'in.
Aka canza mishi AC bedroom aka dawo dashi parlour kana aka sa sabon AC a bedroom d'in.
Hatta labulaye da carpet da blanket da beshid sabbin Ahmad yasa aka saka komai na d'akin lemon green and white ne sosai kalan ya haska d'akin,
Kayayyaki sabbi dal-dal Ahmad ya sayo yazo ya jera mishi kananu na d'inkawa kuma shida kanshi ya fito da kekken d'inkin Hayatuddeen ya fara yayyarΙ—a mishi Ι—inkunan zamani d'inka mishi.

Sosai Ummi take cikin farin ciki.
Adda Rahma kuwa a kwanakin kullum sai tazo.


Yau kwana biyar kenan da fara tashin Saifuddeen,
suna zaune shida Hayatuddeen wanda ya kira Ummi video call sai hira da dariya suke, nan Raliya ta amshi wayar ta nuna mishi yadda aka gyara mishi side d'in da zai zauna.
Murmushi yayi cikin jin dad'i da begen komawa gidan Cikin ahlinsa.
Shiko Hayatuddeen kai ya jinjina kana yace.
"Oho wato abinma son kaine, da yake Hamma ne zai zauna a nan kalli yadda kuka wani gyara d'akin tamkar makwancin shugaban k'asa.
Wato nine jaki in na ga dama in kwan a k'asa ko?."
Cikin kewar sangartarsa tace.
"Ohoho my autanmu kaima ai yanzu side naka tas yake in kana soma sama zaka koma,
inda Hamma Saifuddeen yake da."
Cikin jin dadi yace.
"Wayyo Allah kice na zama alhajin sama."
Dariya sukayi baki d'aya kana suka d'anci gaba da hira daga bisani suka salami juna.

Yau mako biyu kenan cib da fara tashin Saifuddeen zaune,
Kuma Alhamdulillahi tuni an gama mishi duk wani abinda ya dace na sallamarsa da shared'in duk bayan wata shida zaizo a duba jikinshi.

Tuni Hayatuddeen ya gama musu dukkan shirin komawarsu da taimakon Dr Malik Khan.

Nanda kwana biyu jirginsu zai d'aga zuwa Nigeria.

A cikin asibitin.
Saifuddeen na konce shi kuwa Hayatuddeen yana harhad'a duk wani abu nasu domin gobe da asuba jirginsu zai tashi.
a hankali ya zubawa d'an uwan nashi idanu ganin yadda jikinshi ke rawa kar-kar- kar tamkar mazari idanunshi sunyi jazir,
gaba d'aya jijiyoyin kanshi sunyi rud'u-rud'u wani irin zufane ya yanko mishi a take, da sauri ya matso gaban gadon cikin tsananin fargaba da tsoro murya a birkice Hayatuddeen yayi kanshi jiki na rawa.
Sai ya kumayi dib ya tsaya wuri d'aya da yake ganin Hamman nashi na jujjuya mishi kai alamun karya matsoshi.
Idanu ya zuba mishi cikin kad'uwa sai kuma ya rink'a kame jikinshi ganin Hamman nashi so yake ya durkusa,
cikin ikon Allah kuma sai gashi a durkushe bisa tsakiyar gadon.
Kusan a tare suke sauk'e numfashi,
Dai-dai lokacin kuma Dr Anan da Dr Malik Khan suka shigo.
Samunshi a haka yayi matuk'ar sasu farin ciki nan take suka k'ara gwadashi,
kana suka dank'a mishi takardar sallama da sharad'in duk bayan watanni shida zaizo.
Nan Dr Anan ya kara ink'anta mishi durkuson nasa.
Washe gari bayan an idar da sallan Asuba Dr Malik Khan yazo ya d'aukesu, da kanshi ya Kaisu Hilton international Airport Mumbai.
Bai bar airport d'inba saida yaga tashin jirginsu.


Abuja
Amina kuwa yau satinta biyu kenan tana neman Hayatuddeen bata samunshi a waya,
gaba d'aya abin ya dameta,
gashi yanzuma ta kira layin baya tafiya,
kai ta rausayar kana tace.
"Allah yasa dai lfy, sai anjima da yamma zan kuma gwadawa."


Gombawa d'iban fari.

Yau gidan Ummi a cike yake,
Raihana mutanen kd ma tun jiya tazo da Affan d'inta.
Adda Rahma kuwa itama yau sammako tayi.
Hakama goggo Dada da Aunty Mina.

Farop da Adam sai tsalle suke yau Uncles nasu zasu dawo.
Salisu ma ya kawo Salimanshi.
Gida ya kacame da shirye-shiryen tarban Hamma Saifuddeen...!


To AL'amarin Zaleeha fa ya girmama,
Domin har Ruqquya saida aka mata dan duk an d'auka gamo tayi.
Shi kuwa Baba Malam ya sani sarai babu wani gamo,
ba iska a jikinta sai dai zallan iskanci inji Kakarsu da fad'i.
Maryam Zahira kam su dai a dole Zaliha gamo tayi,
Zeyada kuwa da Zakariyya da suke wurin Hajja Inna suma mgnar kakarsu suka bawa amanna Zaliha bata da wani iska sai zallan iskanci.

Ya Ahmad d'inta kuwa wanda kwanan suka dawo Nigeria shida matarsa dan watansu bakwai a Istanbul.
kasan cewarshi mai nitsuwa da hak'uri da k'aunar kannenshi suna dawowa da kwana d'aya ya taho gombe.

Shiyasa yau gaba d'aya Baba Malam ya tarasu,
ya jaddada musu cewar Zaleeha fa tanada sauran dama na mako biyu ta fidda miji cikin tarin masoyanta,
in kuwa ta sake mako biyun nan ya cika bata tsaida gwaniba to tabbas shi zai mata zabi kuma tayi kuka da kanta.
Koda aka tashi taron bayan Ya Ahmad d'in nata tabi suka shiga parlour Mamy gabanshi ta durk'usa cikin zubda k'walla tace.
"Ya Ahmad ina sonshi, bayan shi babu wanda nakeso dan Allah ka bawa baba malam hak'uri ya rufa min asiri kada ya rabani dashi."
Hannunta ya jawo ya ajiyeta gefenshi cikin nitsuwarsa yace.
"Kin san a duniya bamu da kamar Baba Malam ko Zaleeha.?"
Kai ta gyada mishi alamar eh,
shi kuwa cikin sanyin yanayinshi yaci gaba da cewa.
"Kin san wayeshi a wurina nida Maryam da Ziyada da Habu,
bama iya jurar ganin b'acin ransa,
bama iya lamuntan duk wani abu da zai tab'a mana daraja da mutuncin mahaifinmu,
Zaleeha koda nace miki ina tare dake namiki k'arya,
zancen gsky bayan Baba malam da Ya Ameenu nake babu yadda za'ayi kiyi ta zaman jiran gaibu,
abinda ni ganima nake Al'janine ,
to tayaya zamu lamunci ki zauna zaman jiranshi.
Kawai dolenki dollen dolene ki Zab'i d'aya daga cikin masoyanki.
Ko Abdussalam ko Managernku ko Raveel ko kuma wannan abokin nawa Al'amin wanda yayi ta nace miki zuwanki Abuja last year. In kuma kinki tsaida gwani da kanki to wllahi Allah kenan Baba malam zai zaba miki cikin su."
kife kanta tayi a kafadarshi tare da sakin nakasasshen kuka tare da cewa.
"Na shiga uku ns, wlh ya Ahmad ina sonshi."
shigowan Ya Ameenu ne yasa ta mik'e da sauri ta wuce side d'insu kai tsaye bedroom d'in Mama ta wuce bisa gado ta fad'a tana kuka.
Cikin takaici Maman ta harareta tare jan dogon tsaki kana tace.
"Shirmen banza kawai ni dai ina gaya miki wallahi ko bakya son Abdussalam sai ya aureki yaro d'an manya jikan sarakuna har zakiyi ta wainashi da me kika fishi kyau ko asali ko gata,
ni dai ina gargad'inki kada ki bari Malam ya miki zaben tumun dare yadda yayiwa Maryam auren dole to bazan lamunci a miki hakaba,
shiyasa gwara ki bar batun wancan aljanin da ya taimakeki ki rik'e Abdussalam yafi miki." wannan shine rana zafi inuwa k'una jin kalaman Mamane yasa ta mike ta koma d'akinta taci ga da koke-kokenta...


Tafiya tayi nisa cikin sararin samaniya, kowa na harkan gabanshi, autan Ummu kuwa jinshi yake a takure.

Hayatuddeen ne ya d'an juyo ya kalli kekyawar matashiyar dake gefenshi. Wacce duniyar Khanywood keji da ita wacce tauraronta ke harbawa a fagen rawa da wak'a.
a hankali yace.
"Asma'u Ahmad Matawalle,"
Sai ya kuma d'an juyawa ya kalleta a hankali yace.
"Masha Allah.
To Ashema tafi kyau a TV da nake ganinta akan a zahiri."
ita kuwa Asma'u tunda ta shigo hankalin ta na kan Saifuddeen dake rik'e da jarida.
kekyawan sajenshi ta zubawa idanu,
babu ko kebtawa,
saida ta kai 2 minutes tana kallon sajen nashi sai ta kumayi wani tattausan murmushin tare da cewa.
"Wannan kamar balarabe. Kuma kamar mara lfy ne dan taga lokacin da Hayatuddeen ya bashi mgni yasha.

Ganin kamar suna Magna ne yasa ta d'an maida hankalin ta gefesu amman cikin hikima bazama suyi zaton su take kalloba,
da k'arfi ta ajiye nannauyan ajiyan zuciya dai-dai lokaci da ta...!




By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:53 PM - Ummi Tandama: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*NAKASA BA KASAWA BACE*


*PAGE 24*


NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡


Da taga ya juyo fuskarsa ya fuskanci Hayatuddeen,
ba zato ba tsammani taji bakinta ya furta.
"Masha Allah. Allah tsarki ya tabbata ga ubangijin talikai da yayi wannan hallitar kana ya wanzar da kwarjini a kanta."
gashin girarshi ta zubawa idanu ji takeyi tamkar ta kai yatsarta manuniya kan zirin girar nashi.
Shi kuwa Hayatuddeen cikin sangarcin da yake zubawa d'an uwan nashi ya kwab'e fuska tare da cewa.
"Hamma na gaji, wlh tafiyar nan tayi tsawo da yawa."
a hankali ya lumshe idanunshi wanda hakan ya basu damar hade gashinsu ya kwanta lib bisa kwarminsu,
harshenshi ya d'an zaro a hankali ya lashi jajayen labbanshi,
damshi yawun daya shafa musu ne ya basu damar Shek'i.
Hannun shi yasa ya jawo Hayayuddeen ya mannashi da k'afad'arshi kana ya fara d'an bubbugawa alamun ya huta.
Duk abinda sukeyi idanunta na kansu.
sam bata luraba da wayarta dake zamewa sai da taji sautin fad'uwan wayar,
wanda ya jawo hankali Hayatuddeen har ya rigata sunkuyowa ya d'auki wayar da ta fad'o a d'an zirin tsakiyar hanyar da ake wucewa.

Wanni lallausan murmushi tayiwa mishi lokacin daya mik'a mata wayar tare da cewa.
"Kud'in ki million d'aya!."
amsar wayar tayi tare da cewa.
"Kud'in me fa?".
Cikin yanayinshi na calikanci dayin wasa da kowa yace.
"Kud'in kalle min kekyawar fuskar Hamma na mana."
Itama dariya tayi cikin jin dad'i tace.
"A a kune dai zaku biya kud'in darajar idanuna da suka kalleshi,
ladan jamin hankali da yayi da kekyawan sajenshi."
ta k'arishe mgnar da d'an k'arfi wai dan ya jita ya juyo.
murmushi Hayatuddeen yayi tare da cewa.
"Hayatuddeen Muhammad Ahmad Dukku."
kai ta jinjina tare da yin fari da ido kana tace.
"Sunan babba ake fara gabatarwa."
gane nufinta ya sashi gyara zama tare da cewa.
"Darajar mai sunan da sunan yafi k'arfin a badashi kyauta har sai in anyi baranshi, to nan muna badawa sadakanshi."
Sosai take matuk'ar jin dad'in hirarta da yaron mai d'an karen surutu da iya sarrafa harshe.
Fuska ta kwabe tare da cewa.
"To ina bara, duk da nasan shima da kanshi ai zai al'fahari da hakan."
cikin tab'e baki yace.
"No shi ba kamar kowa bane, na tabbatar baki taba haduwa da irinshi ba kuma bazaki tab'aba ,
tsadar muryarshi yafi farashin tsadar ruwan sanyi a zazzafar sahara."
hannu tasa ta dake kanta tare da kai kallonta jikin windows d'in jirgin tana ganin yadda suke ratsa gajumare,
a hankali tace.
"Kana ji da Yayankan nan, ji yadda kake rowar sunanshi."
murmushi yayi mai kama da dariya kana yace.
"Saifuddeen Muhammad Ahmad Dukku."
wata sassanyar ajiyar zuciya ta fesar tare da cewa.
"Saifuddeeeeeeeeeeen sunan ya dace da kekyawar halitta."
kai ya gyad'a mata alamun yasan haka.
juyawa tayi ta d'an kalleshi kana tace.
"Asma'u Ahmad Matawalle."
gyad'a kai Hayatuddeen yayi tare da cewa.
"Na sani, ai ko ledan pure water yafi sunanki tsada da, da buya."
ido ta zuba mishi cikin wani yanayi mai wuyar fassara,
sai kuma tace.
"Yaushe kuka shiga India?."
ba tare da ya kalleta ba yace.
"Last year."
da sauri tace.
"Karatu kukeyi a can ne?."
Kai ya jujjuya mata tare da manna kanshi a kafad'an yayan nashi kana yace.
"Jinya dai mukaje."
cikin sanyi tace.
"Ayyah waye mara lfyan."
da hannu ya nuna mata Saifuddeen wanda hankalin shi ke kan jaridar hannunshi.
ita kuwa cikin mmki ta tambayi meke damunshi,
Hayatuddeen aku sarkin zance tuni ya fesa mata labarin ciwon Hamman nashi.
Tuni hawaye ke kwaranyowa bisa fuskarta, harda Ι—an sheshesΖ™a
Da sauri Hayatuddeen ya d'ago kanshi tare da cewa.
"Gsky dole kiyi tacin kud'i a fims da wanna saurin hawayen naki haka."
ina Hayatuddeen fa bazai gane bane, bazai san ya taji Saifuddeen a rantaba.
A hankali dai sukaci gaba da hira har sukayi musayen phone number,
ta kafa ta tsare tana son ta kalli fuskar Saifudddeen Amman ina domin hankalinshi baya kansu.

Abuja
Amina kuwa bakin da tayine ya hanata damar sake kiran Hayatuddeen.

Gombe
Bayan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login