Showing 69001 words to 72000 words out of 176868 words
Chapter 24 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel
years.
Sai kuma Raihana da zata iya kai 26 year da d'anta Affan wanda bazai wuce shekara biyu ba.
Cikin maida hankali kan buzun Ummi ta juyo cikin wani yanayi da takeji tun da yammacin yau d'in tace.
"Baba ila ya akayi ne?."
cikin sanyin jiki yace.
"Wasune ke sallama da Hayatuddeen."
mik'ewa Hayatuddeen yayi tare da cewa.
"Muje wata k'il Zakariya ne."
kai ya jujjuya mishi cikin sanyi yace.
"A a bashi bane folisawa ne, sunce Saituddeeen ne ya samu d'an hatsari yana asibiti shine akeson yan uwanshi suje."
wata iriyar zabura Ummi tayi kana ta rumtse idonta da azaban k'arfi sabida wani irin duhu da jirin da ya rufe mata ido a take,
wani irin rawa jikinta ya fara har cikin hanjinta takeji suna hautsinewa zuciyarta kuwa tamkar zata faso k'irjinta ta fito fili sabida tsananin razana da kad'uwa lokaci d'aya wata zazzafar zufa ta yanko mata
hakama Raliyya da Raihana shi kuwa Hayatuddeen gaba d'aya idanunshi ya zazzaro woje.
kusan gaba d'aya a tare suka fito Ummi kam duk jikinta rawa yakeyi tamkar mazari.
Hayatuddin ne yayi saurin isa garesu kana cikin tsananin kad'uwa da firgici yace.
"Ina Hamma Saifuddee ina yake meya sameshi ku kaimu wurinshi waya bugeshi?."
Raihana kuwa kuka takeyi mai cike da fargaba,
ita kuwa Raliyya direbansu taketa rabkawa kira cikin firgici da d'aga murya take cewa.
"Sule taho mu tafi wurin Hamma Saifuddee."
a hamzarce Sule direban ya taso wanda yayi ta bai jima da dawowa ba dan shi yana Ζofan Baba bello lokacin da abin ya faru kuma yayi ta kiran Saifudddeen alamun yana nemanshi baiga amsaba, to sai yayo zaton ko yayi wani wurin ne shiyasa ya dawo shi Ιaya,
Motarnda ke harabar gidan ya bud'e ya shiga tare da jawota zuwa gabansu,
dai-dai lokacin kuma police officer d'in yake cewa Hayatuddeen .
"Shiga mota muje yana asibitin Medical Center ne."
firgici da kad'uwan Ummi ya tsananta jin k'irjinta takeyi yana buguwa da azaban k'arfi wata fargaba da razani ya rufeta,
jiki na rawa ta shiga motar da Sule ya kowa gabanta sam ta kasa furta ko k'ala domin harshenta ya mata nauyi jiki na tsuma ta shiga motar, wonda tuni Raliyya da Raihana sun shiga
shi kuwa Hayatuddeen cikin kaifin basira da zurfin tunani irin nasu na maza yace.
"Ummi kuje, bari in d'auko kud'i zan taho a U.D. d'ina."
jin haka yasa Sule jan motar yabi bayan motar police d'in kana suka fita suka nufi Medical Center Gombe.
Shi kuwa Hayatuddeen , a guje ya koma cikin gida sam bai lura da Affan ba d'an Raihana wacce itama Raihana ta mance da d'an nata sabida firgincin halin da d'an uwanta ke ciki,
to bare kuma Hayatuddeen da Ummi,
cikin sassarfa ya haura matakalan benen har yana take steps bibbiyu,
direct d'akin Hamman nashi ya shiga bayan wasu yan mituna sai gashi ya fito,
yana gyara zaman kud'i a cikin al'jihunshi still bai kula da Affan ba ya wuce yana fitowa harabar gidan ya figi mashin nashi cikin azama ya nufi asibitin.
Su Ummi kuwa bisa jagoran jami'an tsaron suka isa k'ofar d'akin da Saifuddeen yake,
sai dai ba damar shiga kanshi.
suna isowa bakin k'ofar Ummi ta rumtse idonta da k'arfi cikin tsananin hargitsin rayuwa tace.
"B.......
Hmmmmmmm. Wasa farin girgi karfa ku manta na gaya muku labarin sashi-sashine, littafin yana tafe da ababe masu tarin yawa,
Salon Saifuddeenfa salone da zai sanyaku shauΖi bage farfaΙo da tsohuwar soyayya hmmmmmm dafa sauran rina a kaba, ku dai ku biyoni a baya.
By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: πππππππππππππ
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 14*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
πππππππππππππ
~Har lau dai kuna samun garaΙsar free page ne kafin a tsaya ΖoΖarta ka/ki turo kuΙin karantar littafin har Ζarshe~
_Turo katin mtn na Ιari uku kacal ta wannan number 09097853276 ,ko kuma ka/ki turo Ιari ukun ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki_
Cikin tsananin firgici da kad'uwa jiki na tsuma murya cike da taraddadi Ummi tace.
"Bayida rai ko Raihana? Raliya baya numfashi ko!? yamutu ko shikenan Saifuddeen shima yatafi yabarmu inna'lillahi wa'inna'ilaihirraji'un,!sai ta kuma fashe da kuku mai matukar ban tausayi.
jiki a mace tasulale kasa ta ta zauna kan kujerar dake gefen k'ofar cikin muryar kuka mai cike da taradaddadi takefad'in.
"Ya Allah karufamin asiri kakara rufamin, kad'aga kafad'ar wanna bawan naka, Saifuddeen idan katafi kabarmu yazamuyi da rayuwar mu ina rayuwa zatata kaimu Saifuddeen kadawo garemu."
sai ta kuma kalli yadda Raliya ta kife kai jikin k'ofar tana wani irin narkekken kuka,
cikin matsanancin tashin hankali Ummi tamike tsaye kamar anzabureta.
Da sauri su Raihana suka rungumeta suma suka fashe dakuka mai sanyin sauti nan gurin yakacame da koke-koke duk wanda yagansu saisun bashi tausayi.
Dr Adnan dake zaune acikin offece inshi kuwa shima sai sharar kwalla yake time to time sai kuma yamike da sauri jin hayaniya a waje, dasauri yafito.
kana Dr Arabi yamara masa baya,
ganinsu Ummi ne yasa Dr Adnan saurin saida hawayenshi, yanufi inda suke.
A hankali yasa hannu ya Yajanye su Raihana ajikin Ummi,
dasauri Ummi tariko hannunsa tare da zuba mishi ido murya a raunace tace.
Adnan Saifuddeen yarasuko!? dan Allah ka kaini naganshi."
wasu zafafan hawayene yaji nakokarin zubo masa dasauri yamaidasu dan gudun kada takuma shiga wani tashin halin,dukda shima hankalinsa amatukar tashe yake sai dai ya fahimci bata cikin haiyacinta matar da take tsananin jin kunyarshi ko sunanshi bata fiye kira iya gaisuwa ke hadasu sabida fulakun fulanin gaske tunda ya zama surkinta suke kunyar juna, amman gashi yau ciwon Saifuddeen yasa ta mance komai har tana rik'e hannunshi cikin sama musu k'arfin guiwa yace.
"Ummi ki kwantar da hankalin ki.
Saifuddeen yana raye, babu wani abunda yasame shi natashin hankali, illa d'an buguwa kadan kuma duk anyi settling d'in komai yanzu haka yasamu bacci.
Ummi addu'arki kadai Saifuddeen yake buk'ata, kidaina kukanna dan kinsan bazaiji dad'iba idan yatashi ya taddaki ahakan."
da sauri tasa tafin hannunta bisa fuskarta hawayenta tashiga sharewa cikin hanzari, dan tasan abinda yafada gaskiya ne.
Dan a duniya idan dakwai abinda Saifuddeen yafi tsana arayuwarsa, baiwuce ganin bacin ran mahaifiyarsa ba in yaga tana zubda hawaye hankalinshi tashi yake ya birkice mata, tuno hakan yasa ta tsagaita kukan,
dai-dai lokacin kuma
Dr Arabi ya k'araso inda suke nan suka hadu sukayita k'arfafa wa Ummi guiwa, harsaida sukaga tad'an sami nutsuwa kafin, suka juya suka nufi office d'in Dr Adnan kasan cewar shi babban doctor daya ke kula da masu irin matsalar da Saifuddeen yake ciko.
Shi kuwa Hayatuddeen gudu yake akan U.D. d'inshi tamkar zai bar garin batareda bata lokaciba ya'isa Medical Center,
dasauri yafaka mashin d'insa acikin harabar asibitin,
kana yanufi cikin asibitin inda Raliya ta kwatanta mishi.
A tsaye yataddasu Ummi ganinsu tsaye cirko-cirko yasa zuciyarshi bugawa da azaban k'anrfi ido ya tsura musu tare da sassarfa cikin kid'ima ya'isa inda suke,
jikinsa nab'ari ya kalli Umminsu cikin tsoro yace.
"Ummi ina Hamma Saifuddeen?."
kai ta sunkuyar cikin son samawa yaran nata nitsuwa tace.
"Ba matsala fa ka kontar da hankalin ka ya yana bacci ne."
sai ta kuma sa hannu ta share hawayenta kana ta nuna mishi inda su Dr Adnan sukayi tare da cewa.
"Kaje ka Adnan na son ganinka."
ba tare da yace komai ba yabi inda ta nuna mishi kasan cewar yasa ofishin Adnan d'in so kai tsaye ya shiga,
in da ya samu Dr Arabi yana nunawa dr Adnan wasu takardu da sukafi kama da hoton k'ashin bayan mutun da jijiyoyin.
Da sauri ya k'arisa gabansu jiki na rawa yasanya hannunsa acikin aljuhu yaciro kud'ad'en daya d'ebu,ya mik'awa Dr Adnan tare da cewa.
"Ya Adnan gashi dan Allah ayiwa Hamma Saifuddeen duk abinda yadace in bazasu isaba in k'aro wasu, mu dai lafiyarshi muke buk'ata in Allah yasa yanada sauran rayuwa."
cikin kulawa Dr Adnan yace. "Ay an mishi komai duk abinda yadace duk wani taimakon da ya kamata abashi anbashi yanzu dama numfashinsa mukeso ya dai-dai ta,
kuma Alhamdulillahi munsami nasarar ceto numfashinsa yanzu jira muke zuwa gobe muga abinda Allah zaiyi,"
Cikin sanyi Hayatudden yace.
"Ya Adnan ina tsoro, kar mu rasa Hamma Saifuddeen."
kafad'arshi Adnan ya d'an bubbuga kana yace.
"In sha Allah bazamu rasashi ba,
sannan kacewa Ummi kada a gayawa Rahma abinda ya faru a bari in na koma zan san yadda zanyi in gaya mata."
Shiru Hayatuddeen yayi fuskarsa d'auke=da matsanancin damuwa, saikuma yace.
"Ya Adnan yanzu zamu'iya ganin sa?".
girgiza kai Dr Adnan yayi,
tareda fadin.
"No yanzu yana buk'atar hutu so bazai yuwu kugansa yauba."
komawa dabaya Hayatudden yayi yajinginu da jikin garu
tareda dafe kansa da yayimasa nauyi, a hankali ya rumtse idonunsa yanajin zuciyarsa nayi masa kuna wasu zafafan hawaye na zubo mishi,
tausayin Hamman nasa dasu kansu yacike ilahirin zuciyarsa afili yafurta.
"Ya Allah kabashi lfy ka d'aga mana kafad'unshi ka rufa mana asiri."
Tare suka fito wurinsu Ummi bayan sun isane.
Dr Adnan yadubi agogon dake daure a hannunsa, kana yadubi Ummi cikin girmamawa yace.
Ummi kuje gida dan dare ya fara nisa yanzu inyaso saimu zauna da Hayatuddeen kafin zuwa goben muga abinda Allah zaiyi,
dasauri Ummi tace.
"A a sudai sutafi ni subarni anand'in nakwana."
Raihana ce tace.
"Ummi muma bazamu iya tafiya ba tareda munga farkawarsa ba."
kai ya jinjina dan yasan dama hakan bamai yuwuwa bane, dan yasan k'auna da shak'uwar da ke tsakanin ahalin,
dan haka saiya kyalesu yace su shiga office inshi, kana shi ya koma office d'in Dr Arabi.
ya rasa meyasa tun d'azu Rahma keta kiranshi gaba d'aya sai ya rasa me zaice mata lokacin daya amsa kiran nata dan a zatonshi ko taji abinda ya farune,
ita kuwa Rahma cikin sanyin jikin da takeji tunda yamma tace.
"Ya Adnan kana lafiya kuwa inata kiranka baka amsawa?."
numfashi ya d'an fidda kana yace lfya lau Rahma meya hanaki bacci har yanzu?."
gyara konciyarta tayi tare da cewa.
"Ji nake zuciyata nata tsinkewa gabana nata fad'uwa shine nace bari in kiraka inji lfyarka."
cikin son sama mata nitsuwa yace.
"Kiyi baccinki ni lafiyata lau, in kuma wani abu kikeso ki gaya min gsky Baby in dawo in miki kona 30 minutes ne in dawo bakin aikina."
cikin jin kunya tace.
"A a ni bance wlh."
da sauri yace.
"Kin ce mana tunda du du du fa bayan sallan isha na baro gida kuma wuni mukayi tare amman yanzu har kwadayinki ya tashi ko?."
da sauri tace.
"A a wlh to kayi zamanka, kaga saida safe."
kafinma yayi mgna ta katse kiran.
Ance bacci b'arawo ne mesace idon kowa,
to yaudai baisami damar sace idanun wanna ahalin ba.
Acan d'aya sashin kuwa cikin New G. R. A.
Hargida police d'in da aka had'ashi da Zaliha yakaita, abakin makeken gate d'in gidansu tatsaya,
kana yafita amotar tayimasa godiya yatari abin hawa yatafi,
dasauri tafita takoma gefen driver tunkan takarasa zama tadanna horn dan har'alokacin amatukar tsorace take,
da gudu maigadi yataho dan jin yadda aketa danna hon ba sassauci da sauri ya wangale mata get d'in,
da sauri ta kutsa hancin motarta cikin farfajiyar gidan nasu da gudu,
asakar farfajiyar gidan tayi parking tafito,
maigadi nakokarin rufe get
wata lafiyayyiyar mota mai azabar kyau da tsananin shek'i ta danno hancinta cikin gidan,
Zaliha kuwa har tajuya zata shige cikin gidan,
ganin shigowar motar yasata tsayuwa, yayinda gaba d'aya zuciyarta da tunaninta ke can wurin kelyawan mutumin daya taimaketan
har aka faka motar tana nazari asannu akabude marfin motar yazuro kafafunsa yafito,da murmushin sa yanufi inda Zaliha take,
itako kwabe fuska tayi tareda langwab'ar dakai gefe,
yakaraso inda take waro idanu yayi ganin galashin motarta afashe cikin mamaki
yace.
"Hatsari ki kayine Zaliha?." cikin muryar shagwaba ta tura baki tare da yarfa hannu tace.
Ya Ahmed ba y'an kalare bane na taddasu a hanyata ta dawowa sunata fad'a shine suka fasamin gilashin mota, badon a mota nikeba nima da sun fasa min kai."
takarasa maganar kamar zatayi kuka dan tausayin Saifuddeen da ta baro suna shirin kashewa,
dasauri Ya Ahmed d'in nata yace.
"Ina dai ke basu ji miki rauniba ko?."
kai tagyad'a masa tare da cewa.
"Amman dai ai sunyiwa motata illa ai."
cikin kula da shak'uwa yace. "To Alhamdulillahi da Allah yasa akan motace ba kan 'yar kekyawar k'anwata aka fasaba,
gobe ida Allah yakaimu zamuji kizabi motar da kikeso.
Amman fa mai sauk'in kud'i Hajia na sanki baki san zafin neman kud'iba sai son ayi ta kashesu ba sassauci."
bayanshi tabi tare da cewa.
"To Ya Ahmed duk yadda kace hakan za'ayi."
shi kuwa Ahmed motar tata ya d'an kalla tare da cewa.
"Wannan d'in za'a gyara sai a saida ta in cikata miki ki samu sabuwa koda wacce bata kai wannanba,
ki samu ta zuwa aiki."
tsalle tarikayi tareda rike hannunsa,
tana fad'in.
"Na gode Ya Ahmed Allah ya k'ara bud'i rabbi ya k'arawa Baba Malam daraja da lafiya da tsawon rai."
murmushi yayi cikin tsananin jin dad'in addu'arta ga mahaifin nasu ya rik'o hannunta suka shige cikin gida.
Wani babban parlour suka shiga wanda yake wadace da tsananin tsabta, wasu manyan kujerune na alfarma ke zagaye da fad'in parlour kana sai wani tattausan carpet mai tsananin taushi sai can gefen dama wasu manyan kanta guda biyu da suke cike da tarin Qura'anai da sauran littafai kama daga na addini dana boko harda su baibul wanda.
sai wani babban tv dake manne da jikin ginin, kana gefen hagu kuma dinning area wanda yasha gyara,
sai kuwa wata kujera dake tsakiyar parlour wacce tafi kama data sarakuna sai wani stoll na glass dake gaban kujerar.
wani dottijone mai tsananin kyau fari k'al k'al dashi yake zaune bisa kujerar nan ta tsakiyar parlour, bisa dukkan alamu alwala yayi yanzu, duk da anyi sallan isha koda yake hakan baya rasa nasaba da kasan cewarshi baya zama ba tare da alwala ba.
zaune yake kana ya mik'e k'afafunshi bisa stoll d'in hannun shi had'e wuri d'aya yana murzasu kana yana d'an karkad'a k'afafun nashi,
a hankali yake motsa labbanshi bisa dukkan alamu tasbihi yakeyi kasan cewa d'abi'arsa ce duk abinda yake bashi hanashi ambaton Allah.
can gefenshi kuwa wata kekyawar matace mai d'an ma dai-dai cin tsawo da jiki, bona ce ta jona jikin soket d'in wuta kana tasa wani turaren wuta mai dad'in k'amshi,
labulayen parlour ta sassake sabida yanayin hazo,
kana ta rage gudun fankan, sannan ta kashe A, C gaba d'aya.
cikin nitsuwa dottijon ya juyo ya kalli k'ofar parlour inda yaji muryar yaran nashi,
amsa musu sallamarsu yayi tare da basu izinin shiga.
a tare suka shigo gabanshi suka zauna cikin cikar tarbiya sukace.
"Barka da dare Baba malam."
cikin son yaran nashi yace.
"Allah ya muku Al'barka."
cikin tsananin jin dad'i Ahmed yace.
"Amin Amin Baba malam mun gode."
murmushi yayi dan yasan yadda Ahmed ke tsananin jin dad'i in ya mishi addu'a,
ita kuwa Zaliha cikin nitsuwa sanin a gaban Baba malam suke ta kalli Hajia Aisha mahaifiyar Ahmed kenan wacce suke kiranta da Mamy, cikin logob'ar da kai tace.
"Mamy yunwa nakeji."
cikin nitsuwarta ta matso inda suke kana tace.
"Ke kinada tsiya ne komai aka dafa kice bai mikiba, sai kije kitchen ki dafawa kanki dan ni dai tuwo nayi."
a hankali ta mik'a tare da cewa.
"Baba malam saida safe."
ido ya d'an juyo ya kalleta kana yace.
"Allah ya bamu Al'khairi kada ki konta bakiyi al'wala da adduba kada kiyita jin kid'e-kid'enan da kike sawa a gidan radionku."
cikin sanyi tace.
"Toh". kana ta juya ta fita.
Ahmed kuwa murmushi yayi sanin an d'aureta tunda an hanata shan kid'a,
nan sukayi ta hira da mahaifinshi da mahaifiyarshi,
ita kuwa Zaliha kai tsaye parlour Mamanta ta nufa,
gefen wata mata mai d'an k'iba da alamun rashin fara'a a fuskarta gefenta ta zauna da gani matar k'abilace ba hausa fulani bace sam bata da fara'a
cikin sauk'e numfashi tace.
"Mama barka da dare."
murya can k'asa a dak'ile tace.
"Sai yanzu kika dawo ko can d'akin uwar taki kika je."
konciyarta ta gyara bisa 2 str kana tace.
"Nida ya Ahmed ne kuma wurin Baba malam muke."
kai ta gyad'a kana tace.
"To tashi kije kici abinci Zulaihat ta muku awaran kuskus."
jin haka ta mik'e da sauri ta nufi dinning table, gefen washing hand baby ta nufa hannunta ta wonke sannan tazo ta zauna tanaci suna d'an hira da Mamansun.
Kad'an ta ci ta mik'e jiki a mace ta nufi d'akinta
tazo gab da bakin k'ofarsu Zaheera taji Zulaihat nata hayaniya alamun tana tarfawa Zaheera rashin kunya,
kai ta kauda ta wuce d'akinta dan bata cikin yanayin jin dad'i bare konciyar hankali.
Tana shiga ta cilla woyoyinta bisa gadonta kana ta zame ta durkusa a k'asa tare da kife k'irjinta bisa gadon pillow ta jawo tare da d'aurashin kanta a hankali ta rumtse idanunta sai kuma tayi saurin bud'esu da sauri sabida ganin tamkar yanzu ake sokawa Saifuddeen wuk'a a bayanshi kife kanta tayi cikin pillow ta saki wani irin zazzafan kuka mai sanyin sauti, ta jima tana kukan a hakan tayi baccin da baifi 45 minutes ba ta fara mafarki tana jujjuya kai da karfi ta saki ihu tare da cewa.
"Mu gudu kada su kasheka kazo mu gudu wayyo ya Ahmed sun kashe minshi."
sai ta kuma mik'e da sauri sabida farkawan da tayi,
kai ta kife bisa gadon tana wani irin kuka mai cike da tausayi da rauni,
sai ta kuma mik'ewa da sauri kai tsaye bathroom ta nufa al, wala tayi kana ta fito nafilfili tayi tayi wanda duk cikin sujjadanta shi take yiwa addu'a ranar da a haka ta kwana batayi bacciba wonkan da yake al'adar rayuwarta ma kafin tayi bacci amman yau bata Toshiba.
Washegari damisalin karfe 6:00 Am, Dr Adnan yafito daga room d'inda Saifuddeen yake,dukda sanyin asuba irinta hunturu dakuma