Showing 138001 words to 141000 words out of 176868 words
Chapter 47 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel
Ali, yasan tushensu ya kuma san tarbiyar Saifuddeen wacce kusan shima ya tarbiyantar dashi,
dominko d'alibinshi ne, a wurinsa Saifuddeen yayi hadda bayan sauk'an karatu da yayi a wurin kakanshi.
Yasan Saifuddeen farin sani, yasan sababin ciwon da ya jaza mushi kurumta, yana tsananin son d'alibin nashi sosai, irin soyayyar da malami keyiwa d'alibinshi mai gwazo da ilimi da basira, nakasar da Saifuddeen ɗin ya samu ta k'ara samishi tausayinshi acikin ranshi,
shiyasa koda yaji cewa Saifuddeen ne ke son d'iyar tashi, ya cika da tsananin farin ciki. Wanda ya kasa b'oyuwa akan fuskarshi.
Haka kawai Ahmad yaji yana mugun son Saifuddeen, saboda ganin yadda jin sunanshi kawai yasa mahaifinshi farin ciki.
Sai Kuma suka meda dubansu kan Bappa Ali da yayi gyaran murya kana yace.
"To koda ya shaida mana, yana sonta, ya nemi da muzo mu nema mishi izinin gabatar da kanshi a gareta,
in ba'a tsaida mata mijiba,
to shine dalilin zuwanmu dan sama mishi izini daga bakin iyayenta, kamar yadda shari'a ta tsara mana."
Malam Adam ne yayi murmushi kana yace.
"To Alhamdulillahi ba'a rigada an tsaida mata mijiba,
kana dama duk masu zuwa gareta bata tsaida gwaniba,
fatanmu in yazo ta ganshi su dai-dai ta tsakanin su."
Sosai Aminu ma kejin dad'i dan tabbas yasan wanna mutane ne masu mutunci wala Allah Zaleeha ta amince dashi,
dan yana sane da shak'uwarta da Saifuddeen.
Shi kuwa baba malam kai ya jinjina musu alamun.
"Eh abinda amininshi ya fad'a hakane a ranshi.
Ajiyan zuciya mai nauyi bappa Ali ya sauk'e tare da gyara zamanshi,
kana ya fuskancesu da kyau sannan yace.
"To amman fa wani hamzari ba guduba,
kasan Saifuddeen yanada larurar nakasa,
kunaga hakan bazai zama matsala ba?."
Gyara zama baba malam yayi kana yace.
"Uhumm Aliyu kenan, to me a cikin nakasa? ai ita NAKASA BA KASAWA BACE,
kuma ai ko wanne d'an adam bai san k'arshensa ba."
Malam Adam ne ya karben zancen da cewa.
"Hak'k'un don duk d'an adam ba'a gama mishi halittarsa ba har sai randa ya kwanta dama."
Cikin d'an jin dad'i, da kwarin guiwa bappa Ali yace.
"Malam Bashir, bayan kuramtanfa Saifuddeen ya kuma samun nakasar spinal cord injury! shekara d'aya daya gabata."
Da sauri Ahmad da Aminu suka d'ago kai suka zuba mishi idanu, cikin alamun tambaya,
shi kuwa Malam Adam cikin son samun k'arin bayani yace.
"To kuma zaiyi aure? Ya yanayi tsaurin cutar, kunfa san cutar lakar jiki ba k'aramar nakasa bace."
Baba Malam ne ya d'ago kanshi tare da girgizawa abokin nashi kai.
tuni tausayin Saifuddeen ya cika mishi zuciya, sai dai ya sani su Baffa Ali sun san abinda sukeyi, in har cutar ta Saifuddeen ta tsananta bazasuyi yunk'urin nema mishi aureba.
Shi kuwa Baffa Ali wayarshi ya zaro kana ya shiga Gallery d'inshi, sashin pictures d'in Saifuddeen ya shiga,
wanda sunfi hamsin kuma duk Hayatuddeen ke tura mishi su,
Aminu ya mik'awa wayar tare da cewa.
"Gashi nan zaune a kan wellchair d'inshi."
Da sauri Aminu ya amashi wayar ya fara kallon hotunan shida Ahmad.
gaba d'aya jikinsu yayi sanyi ganin k'addara da k'udurar ubangiji a kan wanna kyakkyawan hallita,
gashi da cikar haiba,
tuni Ahmad baisan yana zubda hawayeba, ganin wani hoton Saifuddeen dake zaune bisa sofa, Umminshi na zaune kan hannun kujerar ta rik'e mishi haba shi kuwa ya d'an raba jikinta duk suna dariya,
Hayatuddeen kuwa na gefe bisa wellchair d'in Hamman nashi, yana kallonsu yana turb'una fuska waifa shine auta,
Ahmad kuwa mijin Raliya, na tsaye kan Hayatuddeen d'in yana mishi dariya,
Raliya ce ta d'aukesu hoton da yayi masifar kyau.
Hannu yasa ya sharte hawayenshi tare da mik'awa malam Adam wayar, bayan ya gama kallon hotunan ne wanda wasu Saifuddeen Yana kan sallaya, wasu kuwa yana tura welchair d'insa,wasu kuma yana konce kan gado ko 3 sitter, sam bazaka tab'a yarda yanada matsalar spinal cord injury ba.
mik'awa Baffa Ali wayar yayi, tare da maida hawayen tausayin Saifuddeen da suka cika masa idanu, kana a hankali yace.
"Shin zai iya aure har ya iya kusantar mace har in Allah ya nufa su samu haihuwa!?."
Wani sassanyar ajiyar zuciya Baffa Ali yayi kana ya, musu duk cikekken bayanan da doctors sukayi musu ya k'ara da cewa.
"Likitoci sun bamu tabbacin cewa zai iya aure harma da haihuwa, domin nakasarsa bata shafi jijiyoyin mazantakarsa ba.
Kuma ko jiya da sukaje suka sameni da batun saida na kuma tambayarshi batun lafiyarshi.
Ya bani tabbacin shifa baida matsala ko kad'an."
Jin haka yasa Baba malam yin murmushi tare da cewa.
"Alhamdulillahi, na bawa Saifuddeen dama yazo ya gabatar da kanshi a wurin Zaleeha, in dai tayi mishi to in sha Allah Zan bashi ita."
Wani matsainacin farin cikine ya rufesu baki d'aya,
Aminu da Ahmad ma sun aminta da Saifuddeen, domin suma ai basu san k'arshensu ba.
Malam Adam ne ya gyara zama tare da cewa.
"An bashi dama yazo ya gabatar da kanshi, fatanmu Allah ya dai-dai-ta tsakaninsu."
"Amin Amin." Sukace baki d'aya kana,
daga nan suka ɗan taɓa hira, daga bisani su Baffa Ali suka mik'e da niyar tafiya,
Har bakin gate wurin motocinsu, Baba malam da abokinshi Malam Adam dasu Aminu sukayi musu rakiya.
Kai tsaye gidansu Saifuddeen suka nufa,
Wanda yake zaune a falon side ɗinshi shida Ahmad da kuma ishaq,
hira suke amman gaba ɗaya hankalinshi baya kansu, duk tunaninshi naga su Baffa Ali,
tsoro yakeji kar suje ace musu anyi mata miji.
Ahmad ne ya kalleshi tare da cewa.
"Wai mene sai kayi wani shiru, in ma an bada ita, ai akwai wasu matan."
Hararanshi yayi tare da girgiza mishi kai, kana ya mishi alaman "Itace muradin zuciyarshi, kuma abincin ruhinshi."
mik'ewa Ahmad yayi cikin yin dariya kana yace.
"To nama jiyo muryar Baffa Ali a parlour ku taho muje muji dame suka dawo."
Kusan a tare suka fito,
yayinda Saifuddeen yaketa musu kallon nazartar fuskokinsu.
Murmushi yayi ganin Dirankadi na cewa Ummi.
"Alhamdulillahi tafiya tayi kyau, abuma duk namune."
wani irin sassanyan ajiyan zuciya Ummi tayi tare da cewa.
"Gidan mutunci ne ko?."
Da sauri baffa Ali yace.
"D'iyar Bashiru nefa d'an abokin babanmu,
kin tuna malamin su Saifuddeen na islamiya?."
Da sauri Ummi tace.
"La Bashir kam ai bazan mantashi ba,
lokacin da muke karatu su sunyi sauk'a, kusan sune manyanmu a wurinsu muke biyawa in kawu baya kusa."
Cikin dariya malam Ashiru yace.
"Ato baki mance mu ba ashe."
Kai ta gyad'a cikin jin Kunya dan tuno k'uruciya.
Dirankadi ne yace.
"To Zaleeha d'iyarshi ce ai?."
Ahmad ne yace.
"La Zaleehan Malam Bashir ce? D'alibar Saifuddeen lokacin in bashine zai bata haddaba sam bata tab'a iya kawoshi dai-dai."
Sai ya kuma juyawa ya kalli Saifuddeen da ya kauda kanshi kamar ba shiba.
Baffa Ali ne ya shafa kanshi, tare dayi mishi cikekken bayanin irin tarbar da suka samu, da irin karra masu da akayi, da kuma basu izinin ya fara zuwa zance duk sanda ya shirya.
Wani irin tarin farin ciki yakeji a ransa, a fili kuwa sai hannu ya bawa Dirankadi da Malam Ashiru tare da yi musu alamun godiya da jinjina.
sosai Ummi ke lura da irin yadda fuskarsa ke cike da farin ciki,
Amman kunyarsa ta boye hakan.
Sosai sukaji daɗi daga nan Ahmad ya ɗauki su Baffa Ali ya maidasu Dukku,
Ishaq kuwa yabi babanshi suka tafi.
Bayan duk sun fitane,
Saifuddeen ya sarrafa whellchair ɗinshi har zuwa gaban Ummi dake tsaye,
yana isa inda take ya ruggumeta cikin farinciki da salama.
Murmushi tayi itama tare da tallafo haɓarshi cikin son abinda ɗan nata keso tace.
"Allah ya sanya al'khairi a cikin wannan lamarin naka,
Allah ya shige maka gaba ya tabbatar maka da ingantaccen farin ciki!!."
A saman lips ɗinshi ya amsa da "Amin Amin my Ummi."
Sai ya kuma sarrafa whellchair ɗin nashi ya nufi falonsa.
Ummi kuwa da sauri ta haura sama, inda Hayatuddeen ya tasa Raliya a gaba ala dole sai ta share mishi d'akinshi.
A parlour ta samesu ita tana shara, shi kuwa yanata zuba mata surutu, hannunshi rik'e da pillet d'in kifin margi special yanaci yanata zuba mata zance, kana yana watsar da k'asusuwan a bayan inda ta share.
Cikin gajiya tace.
"Wlh na gaji Ummi autanki zai samin ciwon baya dana kunne, duk inda na share yana b'atawa kuma ya cikamin kunne da surutu kamar kabari."
Baki ya turo gaba tare da cewa.
"Ummi wai dan ina bata labarin wata mawaƙiya, Asma'u Ahmad Matawalle ce da take son Hammana kamar ta mutu, ɗazu muka gama waya da ita wai in gaisheki."
Cikin mamaki Ummi tace.
"Mawaƙiya kuma?."
"Eh" Yace yana lumshe ido tare da kurb'ar juice d'in dake hannunshi.
Kauda zancen Ummi tayi da cewa.
"Su Baffanku sun dawo harma sun koma."
Cikin tsalle Hayatuddeen ya diro daga kan firijin da yake zaune tare da wurga kwalin juice d'in yace.
"An bawa Hamma na ita ko yaushe ne auren?."
Cikin dariya Ummi tace .
"Oh ya Allah ka kimtsa min autana ya zama nitsastse kamar Saifuddeen."
Jin Raliya na cewa.
"Ummi an bashi izini zuwa zancen?."
Cikin gyad'a kai tace.
"Eh an bashi sosaima suka samu karramawa, d'iyar Malaminshi nefa Malam bashir, wanda kuma yake shirin Hanyar tsira na gidan radion vission FM."
Tsalle Hayatuddeen ya kumayi tare da cewa.
"Yanzu kuwa zan tafi gidan Adda Rahma inje musha hira."
Kafinma su ankara tuni ya fice abinsa.
Nan Raliya ta samu daman gyara mishi ɗakin nashi.
Ummi kuwa falonta ta dawo ta zauna taci gaba da karatun da takeyi.
Shi kuwa Saifuddeen dake zaune akan lumtsuma -lumtsuman sofan dake falonshi, gyara zamansa yeyi.
Wayarshi ne a hannunshi da alamu hira yakeyi da ishaq.
"Kai yaro kaji dai ko mun samu karɓuwa.
Yanzu yaushe zamuje ne dan gabatar da kanmu?."
Cikin tsokana Ishaq yace.
"Sai next week ko?."
Da sauri ya rubuta mishi.
"Kayi hauka ne, ai zuciyata zata narke kafin nan."
Dariya sosai Ishaq yayi kana yace.
"To yaushe zamuje?."
Cikin gyara zamanshi yace.
"Anjima da yamma zamuje, kafin nan Ahmad ya dawo."
Dariya Ishaq ya kumayi kana yace.
"A a sarkin sauri, gsky ka bari sai gobe da yamma.
Dan yau zata gabatar da program ɗinta na mushaƙata."
Badan ya soba sai don dole haka ya haƙura.
6:00 pm. Zaleeha ce ke cikin ɗakin watsa shirye-shiryen su.
Zamanta ta gyara bisa kujerar da take kai, tare da ɗan rage sautin waƙar da tasa, kana cikin irin muryarsu na ma'aikatan gidajen radio tace.
"Assalamu alaikum, al'ummar jihar gombe da kewaye, barkanmu da war haka sannunmu da sake saduwa cikin shirin Mushaƙata, tare dani Zaleeha Bashir Sulaiman Dukku."
Sai kuma ta ɗan dakata tare da ƙara sautin waƙar nan ta. Nura M Inuwa mai taken.
"Kaso a soka yafi ƙawance cika taso a soka kanaso."
sai kuma ta ɗan range sautin tana mai bin waƙar, yadda ake iyajin muryarta dana mawaƙan na tafiya atare.
Raveel dake ɗakin kula da shirin dake fita, dariya yayi domin yasan dashi da manager akeyi.
Ita kuwa Zaleeha tuni shauƙin sonshi ya rufeta, saboda zafafan waƙoƙin so da take sakawa.
Cikin shauƙi ta katse wata waƙan Nura M Inuwa mai taken.
"So makaho ne, kamar walƙiya ya kamani, gashi na zautu al'umma sunata nunani!."
Sai kuma ta yi magana a hankali, inda tace.
"Da fatan dai kuna jin daɗin waɗan nan zafafan waƙoƙin da muke kawo muku daga tasharmu ta Vission FM.
Ku gyara zama domin jin waƙarmu ta ƙarshe sakamakon ganin lokaci na hararanmu.
Sai ta kuma saki wata zazzafar waƙa mai tsuma zuciya, inda jarumar ciki ke cewa.
"Zo muyi zance masoyi na kajiya."
Sai ta kuma sai-sai-ta waƙar tare da dai-dai-ta muryarta data waƙar tana bin baitin.
"Karda ka kauce, kasa ai mini dariya.
Saida na tace na zaɓo ka guda ɗaya, babu irinka aduk faɗin duniya."
Sosai akejin muryarta na tafiya da sautin waƙar.
Dai-dai lokacin kuma Baba malam da Ya Ahmad da Aminu, suna gidan Inna wacce ya samu tana jin radio.
Cikin kaɗa kai tace mishi.
"Ka jiko Bashiru ka haifi zabiya mawaƙiya,
Kaji da kunnen ka ko,
Yanzu aka gama gabatar da shirinka na masu imani, Kajita ko ita kuma amara zabiya kantalla mai son kiɗe-kiɗe da raye-raye kamar jikar dujjal."
Shiru baba malam yayi cikin jin kiɗan da Zaleeha ta ƙure ta haɗe da muryarta yana hawa mishi kai.
Kai ya jujjuya dai-dai lokacin da take bin waƙar inda ake cewa.
"Kai d'aya gaiyya mazaje kubi baya.
Babu irinka na duba duk nahiya!."
Cikin takaici Ahmad yasa hannu ya kashe radio'n, dan ya lura ran mahaifin nasu ya ɓaci sosai da sosai, shi kuma sam baya ƙaunar duk abinda zai ɓata mishi rai ko ya taɓa ƙimarshi.
Ita kuwa Zaleeha cikin Shauƙi ta gama gabatar da shirinta kana ta fito.
A bakin ƙofa suka haɗu da Bilkeesu mai gado, dan zata shiga gabatar da shirin labaran duniya.
Cikin kula tace.
"Kadafa ki manta Dukku, gobe da yamma zamuzo gidanku nida Rashida zamuje gidan Adama ta haihu muyi mata barka."
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Ba matsala sai kunzo dama gobe ba inda zanje."
Daga nan sukayi sallama,
a bakin motarta ta samu Raveel dariya ya mata tare da cewa.
"Gani nazo muyi zance kar ai miki dariya, ni d'aya gaiya na isheki a duniya, dukka buƙatunki zanmiki ba inkiya."
Murmushi tayi dan dama ai Raveel natane yanada abin dariya dasa mutun Shauƙi.
Motarta ta shiga tare da cewa.
"Kafi kyau a hakanka ka zauna matsayin abokina."
Murmushi yayi tare da rufe mata k'ofar motar.
Kai tsaye gidan Addanta Maryam ta biya dan tace mata,
Yau awaran couscous takeso tayi mata.
A dinning table suka zauna tana cin awaran da aka soya da ƙwai.
Sai miyan tarugu damn albasa da dusan kifi.
Cikin kula Maryam tace.
"Kina addu'o'in da na baki ko?."
Kai ta kaɗa mata tare da cewa.
"Inayi Addana inata rok'on Allah ya baiyana minshi ya kawo minshi gareni in har shidin al'kairi ne a gareni."
Cikin sanyinta da haƙuri tace.
"Yauwa yar uwata, ki kuma rage jin kiɗe-kiɗe ki yawaita jin karatun Al'Qur'ani. Ƙinga inma aljanine kamar yadda mama ke faɗi zai rabu da ke."
Kunun ayan dake gefenta ta kurɓa tare da cewa.
"Mutun nema my Adda na, ina sonshi, ina son abuna."
Murmushi maryam tayi kana tace.
"Allah ya tabbatar miki da al'khairi!."
"Amin Amin." Tace tare da miƙewa, ta ɗauki kular da Maryam ɗin ta cika da awaran tace a kaiwa Aunty Lubna da ya Ahmad.
cikin kula Maryam tace.
"Ki tsaya kiyi salla mana."
Kai ta jujjuya tare da rataya hand bag ɗinta kana tace.
"Kin san baba malam baya son in kaiwa dare a waje."
Kai ta gyaɗa mata kana ta rakata har wojen motarta.
Bayan anyi sallan ishane, Ya Habu ya shigo falon Mama inda ya samu Zaleeha da Zahira da Aunty Lubna suna hira,
cikin yanayinshi na rashin sakin fuska dan shi ya gadi rashin fara'ar Mama amman shi yanada mutunci fuska a haɗe yace.
"Ke Zaleeha kije Baba malam na ƙira."
Da sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
"Ya Habu meya faru?."
"In kinje ai zakiji."
ya bata amsa ataƙaice,
jin hakane yasanya ta miƙe da sauri tare da zumbula hijabin sallanta, wanda yake har ƙasa ta nufi parlour'n Baba malam ɗin.
A bakin ƙofar parlour'n tayi kiciɓis da ya Ahmad, cikin sauri ta kamo hannunshi tare da cewa.
"Please ya Ahmad muje ka rakani dan Allah!."
Murmushi yayi sannan yace.
"To muje."
Shiru sukayi baki ɗayansu a gaban mahaifin nasu,
yayinda Aminu ke gefe riƙe da wani littafi.
Ganin shirun yayi yawane murya na rawa tace.
"Baba malam gani."
tsareta yayi da ido kana yace.
"Na ganki ai, ke nake jira inji ko kin fidda tsayeyye kamar yanda na umurceki."
Kai ta jujjuya a hankali kana tace.
"A'a."
Murmushin girma yayi tare da cewa.
"To ba matsala, ni na zaɓa miki,
zai zo gobe ki ganshi, in ya miki shike nan, in kuma bai mikiba ba dole na baki kwana biyar daga goben sai ki kawo wanda kike so,
In kuma har kwana biyar ya cika baki kawoba to tabbas zaɓina ya zama naki."
Da ƙarfi ƙirjinta ya wani irin wawan bugawa, take tsoro mai tsanani ya rufeta,
da sauri ta rumtse ido jin Ya Aminu na cewa.
"Gobe da yamma zaizo kuga juna kada kije ko ina."
Kai ta ɗago da nufin zatayi magana kenan.
Baba Malam yace.
"Tashi kije sai da safe, Allah ya muku al'barka."
Da kyar ta iya cewa.
"Amin. " kana ta miƙe ta fita.
Kafinma ta isa falon tuni hawaye sun ɓata mata fuska.
kai tsaye ɗakinta ta nufa.
Da sauri Aunty Lubna tabi bayanta tsaye ta sameta ta kifa kai jikin gini tana rera kuka.
Kamota tayi suka zauna kan gado.
Cikin sassauta lafazi tace.
"Meyasa bazaki zama jaruma ba wurin tinkarar matsalarki abu kad'an ki fara kuka."
Cikin zubda ƙwalla ta gaya mata abinda Baban nata ya gaya mata.
Gyara zama tayi tare da share mata hawayenta kana tace.
"To ai da sauƙi tunda har yanzu dai an baki damarki,
ki kuma dage da addu'ar Allah ya kawoshi gareki kafin kwanakin da Baba malam ya faɗan su cika.
Kuka ba naki bane addu'ace ta kama ceki."
cikin jin ƙarfin guiwa ta gyaɗa kai.
Haka dai tayi ta rarrashinta har ta sake.
Sannan ta fita ta koma side ɗin Mamy, inda ta samu tuni Mamy ta tafi wurin Baba malam.
Ɗakin da take sauƙa idan sunzo ta shiga, nan ta samu Ahmad ɗin na yiwa yaransu addu'a.
yana gamawa suka dawo parlour'n Mamy nan yake bata labarin komai a kan Saifuddeen, shiru tayi a ranta tana cewa nakasasshe kuma? a fili kuwa lafewa tayi jikin mijinta.
A can wurin baba malam kuwa sosai yayiwa Mamy bayani sanin tanada nisuwa kuma Alhamdulillahi don ai ita tasan Saifuddeen farin sani.
Ita kuwa Mama Allah-Allah takeyi girkinta yazo, ta shigar da batun Abdussalam a wurin baba malam, akan zata ce mishi Zaleeha ta amince dashi.
Washe gari da yamma ƙawayen Zaliha Bilkisu da Rashida suka zo,
inda tuni itama ta shirya,
har zasu fita Ahmad yace
kada su fita su bari sai gobe in yaso suje,
ya fake da yasan Rashida ta iya zana lalle yace ta zanawa Lubna.
Sosai suke ganin daraja da girman Ya Ahmad ɗin, dan haka ba musu suka amince.
Nan Rashida ta fara zanawa Aunty Lubna lalle,
ita kuwa Zaleeha kamar ta mutu dan baƙin ciki, dan tasan abinda yasa Ya Ahmad ɗin nata yayi musu haka.
Bilkeesu kuwa gyara kwanciyarta tayi tana kallon film d'in Sanam Teri Kasam da ake haskawa a tashar MBC Bollywood.
Biyar dai-dai Ahmad ya shigo tare