Showing 108001 words to 111000 words out of 176868 words

Chapter 37 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

akwai matsala amman bata kulaba,
saima ta k'ara d'aga muryarta ta gaurayeta da muryar mawak'a har nata yana d'an d'ara na radio take cewa.
*"Bani bada rancen k'auna bazanyi aroba!.*
*Na dad'e ina rarrafe cikin masu soyayya!.*
*Gashi nayi fincinkawau misalin gudun barewa!.*

Hakafa tayi ta sakin wak'ok'i masu jijjiga zuk'atan masoya wanda duk yaji yasan abin daga cikin zuciyarta ne.
Koda akazo dan a shiga a ankarar da ita sai aka samu ta kulle k'ofar, a k'arshe dai saida tayi 35 minutes tana caccanza wak'ok'i wanda a zahiri ma program nata 30 minutes ne.
Saida taga kuka zaici k'arfinta ne ta mik'e da sauri ta fita.
A bakin k'ofar ta samu Raveel da manager da Aminiyarta Bilkisu maigado dama wasu maikatan nasu.
ido suka zuba mata ganin hawaye har kan habarta,
sannan kuma ta wucesu da sassarfa,
kai tsaye parking lot nasu ta nufa tana shiga motar a guje ta bar aharabar ma'aikan nasu.

Maigadoce tayi sauri ta shiga cikin d'akin dan gabatar da shirinta.
Raveel kuwa da sauri yabi bayanta,
shi kuwa manager ko motsi ya gazayi.

Shida saura minti goma ta isa bakin gate d'in gidansu,
tana k'ok'arin danna hancin motarta cikin gidan taga wasu tsala-tsalan motoci guda uku suna fitowa a jere, bisa dukkan alamu manyan mutanene masu kamala,
dan haka ta d'an tsagaita,
Suka fita ido ta d'an zaro dai-dai lokacin da mota ta ukun ta iso inda take murya na rawa tace.
"Abdussalam, kuma da iyayenshi a gidanmu." da sauri ta zaro ido...!


A can Mumbai babban birnin k'asar India kuwa.
Hayatuddeen ke zaune gefen Saifuddeen,
yana yanke mishi farcen kafafunshi ne ya d'an d'ago kanshi sannan ya zaro wayarshi daketa ringing a cikin al'jihunshi da sauri yayi picking call d'in sabida ganin number k'asarshi Nigeria kuma video call ne,
yana d'aga yayi murmushi tare da zazzaro ido ganin Amina ce nurse d'innan da take kula da Saifuddeen lokacin da suke Abuja,
fuska a sake yace.
"Amina kece?." hararanshi ta d'anyi tare tsuke fuska sannan tace.
"Amina gatsal babu karanta min Aunty."
Dariya ya d'anyi tare da cewa.
"Ke nafa fiki tsawo."
"To dai ai tsawon ka fini ba shekaru ba. "
ta bashi amsa cikin wasa.
murmushi yayi sannan yace.
"To idan dai kina son in ce miki Aunty to ki dage ki k'ara tsawo."
ido ta lumshe tare da fidda sassanyan nufashi kana tace.
"Ina Hamma Saifuddeen? Ya jikinshi? Da sauk'i sosai ko? yana tashi zaune da kanshi?."
kai ya liggob'ar tare da cewa.
"Wayyo Allah na to wacce tambaya d'aya nasan zan amsa miki?."
cikin zak'uwa tace.
'"Duka zaka amsa min."
murmushi yayi kana yace.
"A ina kika samu wannan number tawa?."
"Kai dai me ruwanka da inda na samu number kawai gaya min ya jikin Hamma."
cikin halinshi na tsokana yace.
"In baki gaya min inda kika samu number taba yasee bazan baki amsoshinkiba."
Da sauri tace.
"Dr Aliyu na tambaya shi ya bani dan Allah nuna min shi."
murmushi yayi tare da kallon Saifuddeen dake konce amman a jingine in ka ganshi kamar a zaune.
Da sauri ya dawo saitin Saifuddeen d'in dan ganin yana tambayarshi da waye yake mgn.
Dai-daita fuskokinsu yayi da fuskantar wayar yadda zasuga juna da kyau,
kana yace.
"To gashi ina shine amsar tambayoyinki."
yana fad'in haka ya mik'e ya koma wurin kafafun Saifuddeen yaci gaba da yanke mishi k'ummarshi.

Ita kuwa Amina cikin wani irin yanayi mai cike da farin cikin ganinshi tayi mishi wani tattausan murmushi murya can k'asan mak'oshi tace.
"Fatabarakallahu hasanil Kalil'in."
sai kuma ta lumshe ido tare sake bud'esu fuskarshi ta zubawa ido na tsawon 37 second a hankali tace.
"Wallahi a duk iya tsawon rayuwata ban tab'a ganin wani mahluk'in da *Saje* yayi mishi kyau koda kwatankwacin rabin yadda Saje yayi maka kyauba."
sai ta kuma tonkoshe kanta bisa kafad'anta na dama tare da cewa.
"Darajar sajen wannan kekyawar fuskartaka yasa idanuna gaza barin kallonka,
Hamma Saifuddeen kana kallon kanka a madubi kuwa, ? antaba ce maka kai kekyawa ne kuwa?. "
Shiru yayi ko numfashi a hankali yake fiddawa yayinda ya zubawa motsin bakinta ido yadda yana gane duk abinda take cewa,
kana yayi dib ya nuna mata sam baya gane komai.
ita kuwa a zatonta Hayatuddeen ya fitane gashi shi kuma kurmane hakan yasa taci gaba da fadin sirrin zuciyarta .
"Saje ya maka kyau in nace maka kyau ina nufin zazzafan kyawun da in dai mutun ba farin sani yayi makaba, in dai irin gani ɗaya zuwa biyu ne to wlh-wllhi bazai taɓa ganekaba duk yadda ya kai da rik'e kamanni!. in dai ba'ance mishi kai bane
Da kana jina da sai in ce maka.
Dan Allah da darajar iyayenmu dan alfarman anabi da Qur'an kada ka sake aske sajen fuskarka ka barshi dan soyayyarka da manzonmu saje da gemu alamace ta nagarta, kaikuwa managarci ne please kada ka aske min sajen nan."
Cikin wani irin yanayi ya rumtse idanunshi da k'arfi jin tana cewa.
"Ina sonk...!




Hahahaha wasa farin girki

BY
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:53 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

        *NAKASA BA KASAWA BACE*


*Page 22*

*NA*

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


_FREEE PAGE SUN ƘARE DAGA PAGE 22 IN KA/KIN SAKE GANI PAGE ƊIN A WASU GROUPS ƊIN SUNA YAWO DAI TO BABU SHAKKA NA SATANE, ƁARAYI ZASU FITAR BANI BA_

*FREE PAGES DAI SUN ƘARE KAT DAGA YAU SHINE ƘARSHEN FREE PAGE DAGA WANNAN FAPE 22 ƊIN AN ƘARE FREE PAGE, BIYA ƊARINKI UKU KACAL DAN CI GABA DA KARANCE LITTAFIN DAGA FORKO HAR ƘARSHE, TURO KATIN MTN NA 300 KACAL TA WANNAN NUMBER 09097853276 KO KUMA KA/KIYI MIN TRANSFER TA ASUSUNA NA JAIZ 0005388578 JAIZ BANK AISHA ALIYU GARKUWA, SAI KA/KI TURO SHAIDAR BIYANKI TA WANNAN NO DAI 09097853276. IN KA/KINSAN BAKI BIYA ƘUƊIN KARANTA LITTAFINBA NA ROƘEKI DA ALLAH KADAMA KI NEMA BARE KI KARANTA*


_AKWAI KAYAN GYARA NA MUSAMMAN GA MASU BUƘATA AMARE DA UWAR GIDAYE, INA BADA SAYAN ƊAƊƊAYA KO SARI, akwai abubuwa masu zafi da inƙanci kamarsu. Sumin, tartai na ƙasar chadi, akwai tsumi mai riɗi na sokotawa, akwai zumar gembu membila, akwai garin daka na mallaka da garin maɗi mai haɗe mace daga ciki akwai sa buzu kuwa, akwai garin sakayawa da garin da ba'a baiwa mai kishiya akwai ɗan batta akwai gimbiyar mata da kwanon ƙasaitacciyar mace akwai garin carmazaƙwoi akwai na gyara nono da mgnin narkanwa akwai butar sirri, akwai garin yaji na maza da kuma sabulan gyara jiki da mayuka akwai jigidar sirri kana akwai magungunan sanyi masu inƙanci, da dai sauransu.... sayan na gari maida kuɗi gida, duk inda kike ina aika kaya, inada reshena a Gombe Yola da kuma Sokoto da mai buƙata ka/ki tuntuɓeni ta wannan numɓer 09097853276,_




Ina son kabar sajennan afuskar ka, saboda ya matuƙar yi maka kyau sosai. irin kyan da ban tab'a ganin saje yayiwa fuskar wani d'a namiji kyau ba. Lumshe ido tayi tare yin k'asa da murya tace.
"Kayi kyau fuskarka ta zama mai cikekkiyar kyau da haiba."
Yanayin yanda ta faɗi maganar cikin  shauƙi shiya sanya Hayatuddeen dake gefe sakin dariya tare da cewa.
"Dagaske ashe sajennan yayi masa kyau? karki damu bazamu bari ya aske ba! tunda kin yaba, dan da alamu dai kin ƙyatsa ko".
Wani irin tsananin kunyane ya rufe Amina don sam bata taɓa kawowa aranta cewa Hayatuddeen na nan ba duk zatonta ya fita ne.  Hannayenta tasanya ta rufe fuskarta da sauri tare da datse ƙiran tana murmushi mai cike da tsantsar nishadi da farin cikin gani Saifuddeen.
Shima Hayatuddeen dariya yakeyi sosai musamman yanda yaga Hamman nashi yayi jigum yana kallon bakinta tamkar wani me ɗaukan karatu ko k'ibta idon bayayi, saidai ya rage girman idanun nashi,
tabbas yayi imani cewa Amina batasan da cewa Hammanshi na fahimtar maganar mutunba idan yana kallon bakin me maganar ba, tabbas da batayi wannan katoɓarar ba.
Shikuwa Saifuddeen idanunsa ya mayar ya rufe yana mejin yanda heart ɗinsa ke beating, sam yarasa ma tunanin me zaiyi hakan yasa yanemi ƙaƙalowa kansa bacci.

***
A nan Nigeria kuwa Zaliha jiki asaluɓe haka kuma zuciyarta ɗauke da mamakin ganin Abdussalam da iyayensa acikin gidansu ta tura hancin motar tata cikin gidan.
Tana gama dai-dai-ta parking ta ɗauki ƴar jakanta me kyau tare da buɗe murfin motar ta fito. 
Kaitsaye ɓangaren Mamy Hajiyar Ya Ahmad ta nufa, da sallama ɗauke abakinta ta kutsa kanta cikin falon, Mamy dake zaune akan kujera ta amsa mata sallaman nata fuska ɗauke da murmushi.
"Mamy sannu da gida". tafaɗa tana me nufar inda makeken fridge ɗin dake cikin falon yake.
"Yauwa Zaliha ya wajen aikin naku?".
cewar Mamy data maida hankalinta ga tv.
"Alhamdulillah". tabawa Mamy amsa tana me ƙoƙarin kafa bakinta ajikin goran ruwan data ɗauka acikin fridge, dawowa cikin falon tayi tare da kwantawa akan kujera kana ta lumshe gajiyayyun idanunta wandanda suke cike da zallar zazzafar soyayyan Saifuddeen, wanda kullum take k'ara narkar da zuciyarta.
Zahira ce tashigo cikin falon daɗan sauri, ganin Zaliha kwance yasanya taɗan tsaya tare da cewa
"Laaa Adda Zalee dama kina nan?".
Harara Zaliha ta wurga mata tare dacewa.
"Da bananan ai bazaki ganni ba!".
  dariya Zahira tayi tare da cewa.
"Dama kina da baƙo a BQ yanajiran dawowarki".
Idanu Zaliha ta ɗan zaro cike da mamaki tace.
"Baƙo kuma wajena yazo?". 
Mamy dake jinsu ne tayi murmushi tare da cewa "Bak'ofa akace miki ba dodoba, kike wani zaro ido Abdussalam ne yazo".
Jitayi gabanta ya faɗi don sai yanzune ma tatuno ganin da tayi musu shida iyayensa a lokacin da zata shigo cikin gidan, fuska ta kwaɓe tare da langwaɓar da kanta gefe, murya asanyaye tace.
"Ayya Mamy mekuma yazoyi?".

"Me kuwa zaizo yi idan ba abun da bakyaso ba, kullum muna miki faɗa akan kifitar da tsayayye guda ɗaya amma kinƙi, to dai Abdussalam kam yagaji da wainasa da kikeyi yaturo iyayensa sun nema masa izinin zuwa zance awajen mahaifinki, ko tantama banayi kuma nasan ya amince musu!"
Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tsaya amaƙoshin Zaliha, take haushin Abdussalam ya cika ranta, meyasa zaiyi mata haka batare da ya tsaya yaji ta bakinta ba? ɗan ƙaramin bakinta ta turo gaba tare da komawa ta kwanta.
"Tashi kije ko bakiji Zahira tace nemanki akeyi ba,
Kije ki sameshi ku fuskanci juna, inafa gaya miki Zaleeha kada ki bari ki k'ure Malam kinfa sanshi kaifi d'aya ne zafa kiyi kuka a sanda babu mai lallashinki".
Mamy tafaɗa cike da kulawa,
cikin turo baki gaba Zaliha ta-tashi daga kwancen da take tare da ɗaukan hand bag ɗinta tafice, sashinsu ta nufa fuskarnan tata babu fara'a ko kaɗan,  harta kusa kaiwa ɗakinta taji muryar mahaifiyarta inda take cewa.
"Da kika dawo tun ɗazu kika tsaya shashancinki bakisan cewa kina da baƙo bane?".    bakinta taƙara turowa gaba tare da cewa.
"Ni agajiye nake yaje sai wani lokaci kawai".
  kallon bata da hankali Mahaifiyarta ta tayi mata tare da cewa
"Zaki shirya kije ki samesa ne ko ko sai na ɓata miki rai yaro yazo yana son ganinki kice yaje sai wata rana shi bawan gidanku ne, ko kin mance shi d'an wanene?".  
ganin yanda mahaifiyarta ta ta haɗe fuska ne yasanya ta buɗe ɗakinta ta shige tana me guna-guni acikin ranta, kayan jikinta ta rage tare da faɗawa bathroom, haka tayi wanka ranta duk acushe, koda ta fito sama sama ta shafa lotion ajikinta, riga da sket na wani purpule ɗin material tasanya, sosai kayan suka amshi jikinta sukayi ɗas. kallon kanta tayi amadubi, tabbas ita kanta tasan cewa kyawunta ya zarce misali, sannan tanada diri irin wanda ke ɗaukan hankalin maza,  yanda takeji aranta yasanya bata jin zama ta iyayin kwalliya akan fuskarta, saidai kuma abun da batasani ba shine ko babu kwalliya akan fuskarta tauraron kyawunta haskawa yake, farfumed ta fesa ajikinta me daɗin ƙamshi kana ta ɗauki wani purpule ɗin mayafi tayafa ajikinta, normal flat shoe ta zura aƙafanta kana ta murɗa handle ɗin ƙofar tafice, BQ ta nufa inda tuni tasake sanja yanayin fuskarta.

  Sallama tayi can aƙasan maƙoshinta haka ta tura kofar katafaren falon tashiga. 
duk da cewa sautin sallaman nata baifito sosai ba amma yaji sautin acikin kunnuwansa, lumshe idanunsa yayi sakamakon wani daddaɗan ƙamshi daya kawowa hancinsa ziyara, ahankali ya amsa mata da "Wa'alaikissalam!"    Cikin takunta me ɗauke da nutsuwa taƙaraso cikin falon tare da zama akan wata kujera dake nesa da wanda yake kai. 
Murmushi Abdussalam yayi tare da cewa
"Barka da dawowa gimbiyar mata, kiyi haƙuri kindawo kuma na hanaki hutawa".   ɗan satan kallon inda yake tayi tare da ɗauke kanta gefe, sanin cewa ba lallai tayi magana ba yasanyashi cigaba da cewa
"Kiyi hakuri nima zazzafar soyayyarki ce take hanani hutawa, ita ke ingizani wurin kafa naci.
Haƙiƙa yau ina cikin farinciki kasancewar nasamu izinin zuwa wajenki daga wajen Malam.
Ina sonki Zaliha ina miki so me tsanani, tabbas kina da wata irin baiwa ta musamman wanda duk wani ɗa namiji idan yaganki dole zaiji wani abu dangane dake, burina bazai wuce naga na sameki amatsayin mata ta ba, dan Allah Zaliha ki amincemin ki duba girman soyayyar danake miki!". yaƙare maganar cikin yanayi na kwantar da murya.
wani murmushi Zaliha tayi wanda ya sake bayyana asalin kyawunta, bakomai yasata murmushin ba kuwa face jin ta tsuniyar da Abdussalam keyi mata akan wai yana fatan tazamowarta mata agaresa,  lumshe kyawawan idanunta wanda ke masifar jan hankalin maza tayi tare da jingina bayanta da jikin kujera,  hoton kyakkyawar fuskarsa ne ke yawo acikin idanunta koda yaushe, wani irin azababben so da shauƙin ganinsa ne suka dirar mata alokaci guda, take yanayinta ya sauya wani irin sanyi taji na shiga jikinta,  ƙwaƙwalwarta ne ta tuna no mata lokacin data kalli cikin idanunsa, tsikar jikinta ne taji yatashi yayinda taji zuciyarta na bugawa da sauri-sauri ji take kamar tayi ta shelanta duniya tana sonshi tana kuma nemanshi da buƙatar ganinshi. 
Abdussalam kuwa ganin tayi shiru kamar ma bata cikin hayyacinta yasanyashi ƙiran sunanta murya asanyaye yace.
"Zaliha!".
Ƙiran sunanta dayayi shiyayi sanadiyar dawowarta cikin sense ɗinta, ahankali ta buɗe idanunta da suke  cike da shauƙin ganinsa, sam bataso Abdussalam ya katse mata tunaninta ba, kasancewar ayanzu tunaninsa shiya zame mata abincin ruhinta, miƙewa tsaye tayi tare da duban Abdussalam daya ƙafeta da ido.
"Zanshiga gida!". ta faɗa ataƙaice.
Murmushi yayi tare da cewa. "Idan muna tare banaso kiyi nesa dani".
Bakinta taɗan taɓe tare da cewa.
"Saida safe".
Bata tsaya jin wani abu daga bakinsa ba tasakai tafice daga cikin falon, shiru Abdussalam yayi tare da bin bayanta da ido, jin soyayyarta yake tana ratsa ko ina na jikinsa, jiki asanyaye haka ya ɗauki makullin motarsa shima ya fice daga cikin falon.
  Itakuwa Zaliha tana kaiwa part ɗinsu kai tsaye ɗakinta ta wuce, kwanciya tayi luf akan gado tare da hugging pillow, idan da ace za a fasa zuciyarta to tabbas za'atarar da tarin begensa acikinta, wani irin abu takeji dangane dashi na musamman, sake rungume pillow'n tayi tare da sakin wata sassanyar ajiyar zuciya, a hankali take cewa.
"Ina kake? Me sunanka? Meyasa ka taimakane duk da ban sankaba baka sanniba? wani hali kake ciki? Me sukayi maka? Kana ina?." sai kuma ta kife kanta tare da sa kuka mai cike da rauni.


*Mumbai*
Yau tun safe su Hayatuddeen suke asibitin kasancewar yaune ranar da zasu gana da manya manyan likitotin guda hud'u da sukazo musamman dominsu.
Alhamdulillah ƙarfe biyu dai- dai suka samu ganawa da Saifuddeen, sunyi masa duk wani abun daya dace, sosai suka bincikesa suka kuma bashi duk wani iya taimakon da zasu iya, wanda kuma suke sa ran In sha Allah watara komai zai dai-dai-ta.

Bayan wata ɗaya.
Alhamdulillah acikin waƴannan kwanakin da suka gabata abubuwa da yawa sun faru ciki harda zuwan Mudassir, wanda ya shaidawa Ahmad kasuwarsu na buk'atarshi dan haka in jikin Saifuddeen da sauk'i to yayi k'ok'arin dawowa 9j.
kana sosai Saifuddeen ke samun sauƙin.
Zuwa yanzu yakan iya juyawa da kansa ya kwanta ta ɓangaren damansa, in yana rigingine kuma yana iya juyawa hagunshi, sannan yana ɗan iya motsa wasu gaɓɓai dake jikinsa, kuma acikin kwanakin da suka gabata ne.
Dr Akash prasat da Dr Malik khan sukazo har Mumbai ɗin suka duba jikinsa,yayinda agefe kuwa yake samun kyakkyawar kulawa daga wajen Dr Anan mehta da kuma Dr Mahesh khurana da kuma sauran nurses ɗin, sosai yakejin dadin zamansa a asbitin don suna ba sa kulawa ta musamman sosai yake jin canji a jikinshi,  duk da cewa jinya yake amma hakan baisanya kyawunsa gushewa ba, saima wani hasken fata da ya ƙara sabida tsananin hutu da kula da zama wuri mai kyau da ya samu, yayinda wani irin kekyawan saje yasamu mazauni akan kyakkyawar fuskarsa, zaman sajen akan fuskarsa ba ƙaramin ƙarawa fuskarsa kyau yayi ba, domin duk kyan namiji in dai fuskarsa ba saje tofa tsirara take bata da sutura.
    Ganin jikin nasa da sauƙi yasanya Dr Adnan da Ahmad suka shirya akan zasu dawo gida Nigeria. 

Yau da ƙarfe uku na yamma jirginsu zai tashi hakan yasanya tun safe suka kammala shirya kayansu tsab inda zasu bar Hayatuddeen, dan kuwa zuwa yanzu jikin Saifuddeen sai dai ace Alhamdulillah.  Hayatuddeen ne yaturo ƙofar ɗakin ya shigo hannunsa ɗauke da wasu manya manyan leda guda biyu, wanda jikinsu ke ɗauke da tambarin *Inorbit

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login