Showing 162001 words to 165000 words out of 176868 words

Chapter 55 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

buga da ƙarfi,
hanyar fita ya kuma nuna mata,
da sauri tace.
"Dan Allah, dan darajar ma'aiki kayi haƙuri ka buɗi baki muyi magana."
Ido ya rumtse dan ya rigada ta haɗashi da Allah.
Itama sanin in dai ta haɗashi da Allah zai saurareta ne ya sata yin hakan.
cikin kaushin murya da haɗe fuska zuciya na tafasa murya a zafafe yace.
"Kije ki kwashi kayan da kika watsar ɗin ki maidasu ɗakinki ki ajiyesu yadda kika samesu."
da sauri tace.
"Dare yayi fa."
A kausashe yace.
"Baza kuma su kwana a waje ba."
Cikin sanyin jiki tace.
"To bari in ƙira Habu yazo ya kwashesu."
A ƙufule yace.
"Waya fito dasu?."
Kai ta juya tare da cewa.
"Ni ce."
Cikin bada umarni yace.
"To kije ki maidasu kizo muyi maganar."
Bata da zaɓi dan ta san kaɗan kenan daga halinshi dole taje a daren ta kwashi kayan,
ta maidasu cikin ɗakinta,
tana gamawa a gajiye ta koma ɗakin nashi,  a kwance ta sameshi cikin maida numfashi tace.
"Na maidasu. Ka tashi muyi maganar."
Kai ya jujjuya tare cikar haiba da isa da gidanshi yace.
"Maganar ai na gamata babu wani wanda zan aurawa ɗiyata Zaleeha sai Saifuddeen,  kuma babu wani mahaluƙin da ya isa  hanani sai ubangijin daya halicceni!."
Yana faɗin haka ya gyara kwanciyarshi tare da rufe ido alamun bacci zaiyi.

Cikin tsananin takaici haɗi da ƙunci tace.
"Ni kuwa Wallahi ƴata bazata auri gurgu kuma kurma ba, ɗiyata bazataje ta zama majinyaciya ina kallo da idona ba, sannan bazan taɓa bari takashe rayuwarta wajen kula da nakasasshe ƙaskantacce ba, Allah ya sauwaƙa ma, ni dai ajinina ban haifawa nakasashshe matar da zai aura ba ehe!!."
Tana gama faɗin haka ta juya ta fita a fusace.
Gyara kwanciya Baba Malam yayi tare da rufe idanunsa, sunayen Allah Kawai yake ambata acikin ransa.
***

Washe gari kuwa Zaleeha daga gidan hajja Inna ma'aikatarsu ta nufa, bayan ta gabatar da shirinta na mushaƙata kai tsaye gidansu kuma ta nufa.

A harabar gidan tayi kiciɓis  da ya Ahmad,
cikin shaƙuwarsu ta nufi inda yake, da alamun cewa shima yanzu shigowarsa cikin gidan.
hannunshi ta kamo tare da cewa.
"Ya Ahmad nayi kewarku kwana biyu bana nan ko kuyi cikiyata."
murmushi yayi tare da cewa.
"Muma munyi kewarki, kin san inata shirin tafiyarmu ne,
naso in wuce da Lubna amman Mamy tace wai in bar miki ita."
tsalle tayi cikin jin daɗi tace.
"Yessss! My mamy kai amman ko naji daɗi sosai!!."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ato ai dama amare yan jin daɗine."
Sam bata kawo komai a rantaba da jin furucinsa,
sai sakin hannunshi da tayi lokacin da sukazo dab da ƙofar Mama,  cikin alamun gajiya da kuma yunwa dake damunta tace.
"Yauwa Ya Ahmad bari inje inyi wanka sai inzo muyi hira,  ka cewa Aunty Lubna ta gasa min abin daɗi yunwa nakeji, please  ko roasted fish nema nasamu idan nazo."

"To." Kawai yace tare da juyawa yayi side ɗin Mamy.

Ita kuwa Zaleeha da sallama ta shiga,
da sauri ta kutsa kanta cikin parlour'n,  saboda hango Mamanta na zaune fuskar nan a kumbure alamun tsananin fushi,
da sauri ta durƙusa agabanta cikin tsoro tace.
"Lafiya kuwa Mama? Meya sameki? baki da lfy ne?." Duk tayi mata tambayar cikin kulawa, irin wacce ke tsakanin Ƴa da Uwa.

Cikin tsananin takaici Mama ta watsa mata harara tare da cewa.
"Ae naji ke har dariya ma kike ko? yayinda ni kika barni ina nan baƙin ciki da ɓacin ranki zasu haɗu su kasheni!."

Cikin zaro ido haɗi da tsoro tace.

"Na shiga uku Mama me nayi miki?."

A hasale Mama tace.
" kikamin ko kikayiwa kanki."
Sai kuma ta miƙe tsaye tare da watsawa Zaleeha wani  irin mugun kallo.
Sannan tayi cikin bedroom ɗinta, wanda idan  ba doleba, sam  bata son shigarsa, saboda idan taga wannan kayan ji takeyi kamar ta faɗi ta mutu, tsabar baƙincikin dake cika zuciyarta.

Da sauri Zaleeha ta bita,
a gaban Maman  ta tsaya, cikin raunin murya tace.
"Mama kiyi haƙuri in na miki laifine ki gaya min Wallahi bazan sakeba!."

Azafafe ta nuna mata tarin akwatunan wanda ita sam bata gansuba sai yanzu cikin kakkausan murya tace.
"Kinyi asara Zaleeha, Wallahi kinyiwa kanki sakiyar da ba ruwa, ki rasa wanda zaki zaɓa duk cikin masoyanki sai wannan banzan nakasasshen da baya ji baya magana, uwa uba kuma baya tafiya, ki zaɓeshi matsayin miji har zaki bashi dama ya turo iyayenshi su kawo tarkacensu harda su sadaki,
wato kin maidani shasha naje inata haushi ashema ban saniba kece kika amince mishi sai ɗazu Habu yake sanar min."
Mama fa bata tsagaita da masifaba bare tasan halin da Zaleeha ke ciki.
sai Zahira ne ta zaro ido da ƙarfi ganin yadda Zaleeha tasa hannu da tsananin ƙarfi ta kama kanta,
yayinda tuni kunnuwanta sun toshe tun lokacin da Mama tace mata an kawo sadakinta kuma wai ga kayan aurenta a gabanta,
sannan wai da yardarta uwa uba kuma wai da wancan ginannen taɓon ne da Allah ya ƙawatashi da kyan sura,
daga nan bata kuma jin zancen Mama ba, sai rumtse idanunta da tayi tare da  cilla wani irin gigitaccen ƙara mai tsananin ƙarfi, haɗe  da cewa.
"Ƙarya ne banice na turo shiba, bana sonshi! bazanyi aureba Wallahi, bazan zauna da kowaba sai wanda ya taimakeni!!." 
Sai ta kuma buɗe idanunta, wanda sukayi jazir ta kalli tarin akwatunan, wani irin gigitaccen ƙara ta saki wanda yasa,
Ahmad, Habu,Aunty Lubna da suka nufo parlour'n  maman tun ihunta da sukaji na  forko  ya sasu shigowa a guje,
suna shiga ita kuwa zaliha ta yanki jiki ta faɗi sumemmiya.

Da sauri Ahmad ya tarota ta faɗa jikinshi,
cikin rawan jiki murya a hargitse yake ɗan jijjigata tare da marin kumatunta yana faɗin.
"Zaleeha!  Zaleeha!! Ki tashi Zaleehaaa!!!."
Sai ya kuma kalli Zahira daketa kuka tana cewa.
"Shike nan ta mutu, tace muku bata son auren ba wanda take so ku barta ta jira wanda takeso anƙi gashi yanzu baƙin ciki zai kasheta.
Mama kuwa da sauri ta juya ta nufi falon Baba malam tana shiga tasa kuka tare da cewa.
"Shike nan baƙin ciki zai kashe min ƴata,
in ta mutu ai kowa ya huta sai a kaiwa shashashan musakin gawanta."

Shiru Baba malam yayi sai murmushin da yakeyi, Mamy kuwa da sauri ta miƙe zata nufi side ɗin Maman,
dan da fari da suka jiyo ihun Zaleeha sunyi zaton ko uwarce ke dukanta, shiyasa data yunƙura zata je Baba malam ya dakatar da ita.

A can ɗakin Mama kuwa a kiɗime Lubna ke cewa Ahmad.
"Hubby a sume take fa,  ko dai da gaske al'jani ne ya taima keta shine yau zasu baiyana kansu? Hubby mu kaita wurin Baba Malam!." Tafaɗi maganan cikin tsananin ruɗewa.

Yunƙurawa  Ahmad yayi da ita a jikinshi,  fita yayi da matsanancin sauri ya nufi parlour'n Baba Malam,
a bakin ƙofa sukayi karo da Mamy.
Cikin tsoro da firgitan ganin Zaleeha kamar gawa Mamy tace.
"Malam da gaske Zaleeha ba lfy."
Shi kuwa Ahmad a gaban mahaifin nasu ya direta tare da cewa.
"Baba malam al'janine fa a jikin Zaleeha da gaske danfa kawai taji batun auren ne yasa ta suma."
Habu ne yaja wani dogon tsaki tare da cewa.
"Ya Ahmad meyasa kake yarda wai Zaleeha iska gareta?."
Cikin tsawa yace da Habu.
"To in ban yarda tanada iskaba meya sumar da ita?
please Baba malam ayi mata ruƙiyya ko al'janin zaiyi magana."

Cikin takaici Habu ya juya gaban fridge ɗin dake gefenshi, buɗewa yayi tare da ɗaukan goran bottle water  mai ɗan karen sanyi,
kana ya juyo marfin gorar ya murɗa kana ya ziraro da bakin gorar dai-dai saitin fuskar Zaleeha ya fara tsula mata ruwan sanyin.
Wani irin wawan ajiyan zuciya taja, me ɗauke da azaban ƙarfi kana ta fizgo numfashinta da wani zazzafan kuka,
cikin kuka mai cin rai ƙuna da kuma tsananin tsoro take cewa.
"Bana sonshi Ya Ahmad ka gayawa Baba malam wallahi bana sonshi na tsaneshi!."
Sai ta kuma kamo hannun Ya Ahmad ɗinta da tuni ya fara zubda hawaye, cikin kuka taci gaba da cewa.
"Ya Ahmad ka gayawa Baba malam mana,
ka faɗa mishi cewa gurgu nefa haka kuma kurma ne, kace mishi bana sonshi na tsaneshi,
wallahi in aka aura min shi zan mutu wlh ya Ahmad mutuwa zanyi!!!." Taƙare maganar cikin wani irin kukan fitar hayyaci.

Habu ne ya watsa mata wani zazzafan harara tare da cewa.
"To ki mutu mana! In kin mutun sai me? Ko kina zaton mutuwarki zaisa muma mu mutu ne?."
Faɗawa  jikin Aunty Lubna dake raɓe agefe  tana zubda hawaye tayi, cikin kuka da raunin murya tace.
"Wayyo Allah na Aunty Lubna ki taimaka min ki faɗa musu inada wanda nake so, kice musu wlh bana son musakin can."
Cikin rauni Ahmad ya kalleta murya  a tausashe yace.
"To meyasa kika ce mishi kin amince dashi ya turo iyayenshi tunda kin san bakya sonshi?."
cikin kiɗima da gigita tace.
"Wallahi ban faɗaba wlh ƙarya yake min, to shida kurmane ta inama zaiji abinda zance mishi?."
cikin hatsala Habu yace.
"Ba text messages kika tura mishi ba, da wayarki."
Miƙewa tayi a hargitse ta kalli Mahaifinsu da ya zuba musu ido, yana murmushin ganin ƙuruciyar yaran nashi, ba abinda ke sashi murmushi kamar yadda Ahmad yake taya Zaleeha kuka kamar yaro,
yana jin daɗin zafin Habu dan yasan Habu Baban ya Aminu ya gado yayan Baba malam kenan,
cikin kuka Zaleeha tace.
"Wallahi ƙarya yake min ni bani da number shi ma."
Mama ce tayi kaffa tare da jan dogon tsuka.
Habu kuwa falon Mama ya koma,
jim kaɗan sai gashi da wayar Zaleeha riƙe a hannunshi,
cikin takaici ya cire wayar a key dan yasan komai na wayar,  hakan kuma tsarinshine dan bincikar woyoyin ƙannenshi yasa su duk yasan komai na wayarsu.
kai tsaye inbox nata ya shiga ai kuwa text biyar ya duba, ana shida sai ga text ɗin gama number shi da Saifuddeen yayi seven da My happiness.
Cikin zafin rai ya nuna mata wayar tare da cewa.
"Meye wannan?".
Ido ta zaro gaba ɗaya, ganin abinda ke rubuce da kuma haƙiƙa ita ta rubuta, kuma ta turawa number da aka sawa suna da my happiness, sai kawai ta miƙe ta koma can gefe nesa da mahaifin nasu ta fara buga tsalle tare da yarfa hannu tare da kurma ihu kana tana cewa.
"Sharri! Sharri!! Sharri!!! Sharrine yayi min wallahi ƙarya ne ni bana sonshi!!!."

Ganin yanda takeyifa yasa Baba malam yin wani murmushi mai kama da dariya.
Saura kuma gaba ɗaya ido suka zuba mata.
Habu kuwa belt ɗin ƙugunshi ya zaro tare da yin kanta.
ai fa tana ganin haka ta juya a guje tayi cikin gidan, shi kuma ya mara mata baya a guje,
radadada kake jinsu a guje.
ganin yadda Habu ya bita yasa Ahmad binsu da gudu hakama Aunty Lubna da Zahira.

Zaleeha kuwa gudu take da iya ƙarfinta dan tasan Habu ba mutunci ne dashi ba. In ya kama duka kamar mara imani.
Kai tsaye ɗakinta ta shiga cikin sa'a ta samu ta maida ƙofar garam ta rufe,
tun kafin ya iso,
ganin haka yayi kwaffa ya juya tare da cewa.
"Yar iska kawai da ki tsaya mana."
Ita kuwa a cikin ɗakin wani irin fitininan nen kuka tasa da iya ƙarfinta, tana kuka da surutai cewa.
Ita dai bata sonshi ta tsaneshi zata mutu in an aura mata shi.
Ahmad kuwa da Lubna rarrashinta sukayi tayi da bata baki amman ina.
ranar haka ta kwana a rufe tana kuka da al'washin ciwa Saifuddeen zarafi.

Mama kuwa sosai taji daɗin abinda Zaleeha tayi,
ta kuma yi niyar yaƙi da wannan auren.

Ƙarfe takwas dai-dai na safiyar ranar asabar Zaleeha fito cikin d'akinta inanun ta a kumbure tayi ja alamu tayi kukan  mai yawa.
gefen Mamanta ta zauna cikin sanyi tace.
"Ina kwana Mama".
"Lfy."
ta bata amsa a tak'aice.
kai ta d'an sunkuyar ida nunta cike da hawaye tace.
"Mama wlh k'arya yake min sharri ne, ni bance ina sonshi ba." kai Mama ta gyad'a mata cikin alamun gamsuwa tace.
"To yanzu ya zakiyi?."
cikin k'arifin hali tace.
"Zan yi mgnin abun in sha Allah shida kanshi zai dawo yace ya fasa."
Cikin jin dad'in Mama tace.
"Ke dai ki kafa ki tsare cewa bakya sonshi ni kuwa zan san abinda zanyi a kai."
To tace kana ta kira Zahira tare da cewa.
"Je parlour Baba Malam ki d'auko min wayata".
Juyawa tayi ta nufi bedroom d'in Mama tare da cewa.
"Gashi nan na d'aukoshi tun jiyan ai."
Amsar wayar tayi kana ta koma d'aakinta.
Ita kuwa Mama murmushin jin k'arfin guiwa tayi tare da cewa.
"Bazaki auri gurgu ba kam ko kina sonshi zan hana kuma wlh bazan bari kiyababanki boyayya kan arennamba dole zanyiwa boka bayanin yadda nake son yasa ki bijirewa wannaɓin da BAban naki ya miki, don ko sama zata had'e da k'asa zaki auri Abdussalam dan shine dai-dai dake."
Tana kaiwa nan ta kira wayar Abdussalam yana d'agawa suka gaisa kana tace mishi,
ya had'o komi da komai na aure ya turo iyayenshi Zaleeha ta yarda dashi.

Jin haka yasa Abdussalam jin k'arfin guiwa nanfa yaci gaba da shirya lefenshi dai-dai da matsayinshi.

Ita kuwa Zaleeha konciya tayi kan gadonta sannan ta fara rubuta text kamar haka.

```Kai baka cancanci inyi makasa sallama ba, domin ita sallama ta masu amincine ba mak'aryata azzalumai irinka ba. nace maka bana sonka na tsaneka bazan soka ba har abadan,
dan haka kayi maza ka turo wad'anda ka aiko suka kawo wannan tarkacen suyi maza su zo su kwashe gaiyar dukiyarka```
murmushi tayi lokacin da ta tura text d'in a ganinta ta k'unsa mishi bak'ak'en maganganu.

Saifuddeen kuwa yana zaune bisa kujerar wheelchair d'inshi Amman a dinning table,
Ummi na had'a mishi tea yayinda yake cin soyayyan doya da kwai,
jin wayarshi dake cikin al'jihunshi ta bashi wani alamun sak'o ya shigo kamar bazai duba ba,
sai ya kuma zaro wayar ganin number tane ya sashi yin murmushin mugunta dan yasan,
Kwanan zancen.
ganin yanata murmushi Ummi yin murmushi dan farin cikinsa shine nata.
Raliya kuwa da Hayatuddeen suma murmushin suke tayasu.

Bai bud'e text d'inba saida ya koma side d'inshi sannan ya bud'e ganin abinda ta rubuta ne yasashi yin maganar zuci.
"Hmmmm wasa farin girki, yarinya kinga ta kanki." a zahiri kuwa yi yayi kamar baiga text d'inta ba bare ya bata amsa.

Ita kuwa ganin shiru-shuru bai maida mata martini bane yasa da azahar ta sake tura mishi wani text d'in wanda yafi na safe zafi.

Shiru ba amsa har dare, ganin haka ta kuma tura mishi wani text d'in.

Har kusan k'arfe d'ayan dare tana jiran amsa amman cib ba amsa.

Washe gari haka da asuban fari ta kuma tura mishi wani zazzafan text ,
Still ba amsa.

Abu fa ya isha Zaleeha yau kusan kwana uku kenan ba amsa,
kuma bata fasa tura mishi bak'ak'en maganganu ba.

A gidan kuwa babu wanda ya sake mgnar auren Baba malam kuwa duk nacin Mama bata jin ta bakinsa.

Habu kuwa shida Zaleeha hararace a tsakaninsu.

Zahira kuwa munafuka yar koren Mama ce.

Aunty Lubna kuwa ita ke hillace Zaleeha,
har take mantar da ita batun wani aure.

Ita kam Zaleeha ta fara sakewa dan ganin baya maida mata amsa sai take zaton yayi mubaya'a ne,
koda wasa bata shiga d'akin Mama dan bata son ganin jerin akwatunan.

Ya Ahmad yanata shirin gobe zai tafi.

Suna cikin hira ya kalli Zaleeha da ta d'an sake a hankali yace.
"Ke Zaleeha kayan d'aki dana kitchen na wanne k'asane kikafi so kikega sunada ink'anci.
cikin rashin fahimtar mgnar tashi tace.
Gada je dai da kujeru Dubai komansu nada ink'anci da tsari.
Kayan kitchen kuwa na Chaina sunfi kyau." murmushi yayi tare da salonta yadda gaba d'aya hankalin ta na kan wak'ar da takeji a wayar Lubna, har tana cewa.
"Yauwa Aunty Lubna tura min wannan wak'ar mana ina sonta tamin dad'i."
To Lubna tace tare da yiwa mijinta signal alamun sam fa Zaleeha bata gane komai ba.

Mama kuwa a sashinta ta kira yayarta Ruda ta shaida mata abinda ke faruwa,
Jin haka yasa Ruda cewa cikin satin nan zata shigo gombe.

Maryam kuwa duk abinda akeyi bata saniba.
shiyasa har ta kira Anty Aisha k'anwar mama ta shaida mata an kawo lefen Zaleeha biki kuma 27 next month.
Itama tace zata zo ganin lefe.

Saifuddeen kuwa Ishaq kadai ya gayawa abinda Zaleeha ke rubuto mishi nan Ishaq yace mishi ya barta sai tazo har inda suke,
dan yasan zata zo.

Ya  Ahmad ya tafi harkan aikinsa, tunima ya bar k'asar.
in da ya bud'a bakin aljihunshi yake kashewa Zaleeha mahaukatan kud'ad'e na ban mmki wurin saya mata dukkan abin buk'atan amare.

Tafiya dai ta mik'a a lissafin yau saura mako d'aya ne auren.
tuni shirye-shirye sun kankama ta gefen ango da amarya.

Da hantsi misalin k'arfe 11:15 Am Zaleeha ta shigo d'akin Mama wanda lokacin kenan ta fito daga d'akinta da shirin zata wuce wurin aikita, jin
muryar Yayarta Maryam da Anty Aisha da Ruda yasa ta nufi d'akin a hankali ta shiga bakinta d'auke da sallama.
sai kuma tayi turus a baki k'ofar ta tanya cikin tsananin kad'uwa da firgita,
ido ta zubawa Maryam dake tsakiyar akwatunan ta bubbud'esu gaba d'aya tana nunawa Any Aisha kayan,
Yayinda Mama kuwa da yayarta Ruda suke kan gado fuskokin nan nasu tamkar suyi ruwan jini kuma tuni sun barbaɗe ƙofar falon Mama da maganin da Ruda ta kawo wanda aka basu tabbacin in dai Zaleeha ta tsallakashi tofa bazata lamunci zaɓin mahaifin nataba zata tashi hankalin kowa har sai an janye batun auren.
cikin sanyin murya Anty Aisha take cewa.
"Allah ya sanya al'khairi yasa gidan zamanta kenan iya rai da mutuwa."
Maryam ce tace Amin Amin.
sai kuma suka juyo suka kalli Ruda dake cewa.
"Tir da addu'arki Aisha bakinki ya sari guntun kashi,
kifa kalli wannan zuk'ek'iyar budurwa ki fasalta zamanta da gurgu kuma kurma musaki mara amfani kice Allah yasa gidan zaman tane.
Ke kuma Maryam da yake baki da hankalin da kishin yar uwarki harda wani cewa Amin."
ita kam Zaleeha tamkar an dasa tane a wurin ta kasa tantance abinda kunnuwanta ke jiye mata daga bakin Maryam dake cewa.
"Addu'a ita ta dace da Zaleeha tunda dai wannan abun yin Allah ne,
ko ana so ko ba'a so in Allah yayi ita matar Saifuddeen ne dole taje gidanshi,
kuma ke Mama kin san halin Baba malam me amfanin bad'i babu rai,
yak'in da babu nasara ai gwara yin mubaya'a du du dufa auren nan saura sati d'aya ne rak."
Da sauri Zaleeha tasa tafin hannunta ta dafe k'ahon zuciyarta dake gab da tarwatsewa,
idanunta ta rumtse da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login