Showing 96001 words to 99000 words out of 176868 words
Chapter 33 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel
ruwan hawayen nashi tare da shafa hannun nata a fuskarta kamar mai shafa mai.
idonshi ya bud'e tare da tsareta dasu,
ita kuwa da sauri ta juya ta fuskanci Hayatuddeen,
sai kuma tayi saurin kauda kanta ganin Hayatuddeen yana d'aga mata girarshi tare da cewa.
"Kin yi sa'a kin samu tabarrakin hawayen hammana."
allura ta ciro ta had'a kana ta mishi allurar sannan tasa hannu zata b'allo mgnin ta bashi sai kuma ta tsaya jin Hayatuddeen na cewa.
"Kada ki b'are mgnin bazai sha abin hannunkiba in ba wonke hannunki kikayi ba."
ba tare da tace komaiba ta juya ta d'au goran ruwan dake gefenshi sannan ta d'an matso jikin window ta d'an bud'e window ta wonke hannunta sannan ta juyo tazo ta bashi mgnin sannan ta juya zata fita tare da cewa.
"Ka fito ka barshi yayi bacci."
jin haka Hayatuddeen yabi bayanta,
suna fita sukayi kicibis dasu Dr Adnan da Ahmad.
nan ya juya ya shiga dasu Ahmad d'in.
Sama-sama suka gaisa sannan suka fito suka tafi gida.
Shida dai-dai Ayuba ya iso dasu Rahma cikin asibitin kai tsaye ya musu jagora d'akin da Saifuddeen ke ciki.
Suna shiga suka samu Ahmad da Adnan.
da Sauri suka k'aroso gaban gadon cikin rauni fuska cike da hawaye Rahma ta kamo hannushi tana cewa.
"Allah sarki d'an uwana ciwo bai mana adalciba k'addarar ka tayi mana mugun bugu a rayuwarmu."
Raihana kuwa ta kasa mgna sai kuka, dan dama duk ta fisu rauni da sauri hawaye Rahma cema mai d'an k'arfin hali.
Ahmad kuwa da sauri ya kamo hannun Raliya da ta kife kanta bayanshi tana kuka tare da cewa.
"Ya Ahmad shikenan Hamma Saifuddeen ya k'ara samun wata nakasar wai bazai sake tashi tsayeba."
Jawota gabanshi yayi tare ruggumeta yana shafa bayanta,
Ya Adnan ma hannun Rahma ya kamo tare da cewa.
"Da nasan haka zakizo kisa k'annenki a gaba kina kuka kina karya musu zuk'ata da na hanaki zuwa,
kalli kafin ku shigo munata hira dashi daga zuwanku kun birkitashi."
a hankali ta rink'a jujjuya mishi kai tare da share hawayenta.
sai kuma duk suka juyo suka kalli bakin k'ofa Hayatuddeen ne da Amina suka shigo a tare,
ganin yayunshi yayi saurin isowa tsakiyarsu ganin yadda Raihana keta kuka ya sashi kamo hannunta cikin sanyi da yanayinshi yace.
"Allah sarki Adda Raihana kiyi shiru,
kinga ya Adnan yana rarrashin matarshi Ya Ahmad ma yanata lallab'a matarshi ke kuma sun shareki dan sunga Ya Saminunki baya kusa, to kiyi hak'uri d'an uwanki zai rarrasheki kema ki daina kuka kinga zakusa Hammanmu tashin hankali."
duk da kuka sukeyi saida suka d'an murmusa,
Amina kuwa da sauri ta iso hannu tasa ta d'auki Affan dake kan gado kusa da Saifuddeen.
sai kuma ta bisu da idanu a cikin ranta take cewa.
"Allah kenan mai kyauta da k'ari su kuma duk ahlinsu kyawawane tamkar larabawa."
A zahiri kuwa cikin sanyi ta gaidasu ganin Rahma da tsohon ciki ne ya sata jawo kujerar kusa da ita sannan tace.
"Ga wurin zama ki zauna."
da sauri Adnan ya zaunar da ita sannan ya kalli Raihana da har yanzu ta gaza tsaida kukanta cikin kula yace.
"Raihana kiyi hak'uri."
kai ta sunkuyar jin Saifuddeen ya kamo hannunta da sauri ta matso kusa dashi,
hannunshi yasa ya share mata hawayenta sannan ya mata alamun tayi shiru.
kai ta gyad'a tare da cewa.
"Hamma Saifuddeen Ya jikin?."
Hayatuddeen ne yace.
"Jiki kam Alhamdulillahi da sauk'i."
Raliya ce ta kalli mijinta cikin rauni tace.
"Ya Ahmad wai gobe zaku tafi?."
Kai ya gyad'a mata kana yaja hannunta suka fita harabar asibitin
taxi suka shiga kai tsaye hotel mafi kusa ya kama musu a cewarshi wai zai rarrashi matarsa ya sama mata nitsuwa.
hakama Ya Adnan ma ya d'auki Rahma suka tafi,
Raihana kuwa nan suka zauna ita da Hayatuddeen da Amina da take ruggume da Affan tana shafa suman kanshi,
amman sai mutsu-mutsu yakeyi alamun gajiya
ganin haka sai ta shiga bathroom wonka ta mishi sannan ta fito inda ta samu,
sunata hirarsu da body language,
cikin kula tacewa Raihana,
"Gashi a bashi nono."
hannu tasa ta karb'eshi tare da cewa.
"Sannu ngd matuk'a Allah ya saka."
murmushi tayi tare da cewa "Amin Amin."
ita kuwa Raihana Hayatudden ta kalla tare da cewa.
"Autanmu mik'o min hand bag na in sa mishi pampers da kaya."
da sauri ya mik'o mata Jakarta d'in,
pampers ta fara sa mishi sannan ta samishi kaya,
tuni kuwa yana shan mama kafin ta gama sa mishi kayan ma yayi bacci.
ita kuwa Amina allura tayiwa Saifuddeen tare da bashi magungunanshi,
tana gamawa ta juyo ta kalli Raihana da taga Saifuddeen na mata mgnar kurame,
sai kuma taji Raihana na cewa.
"To."
sai ta kuma mik'o mata Affan tare da cewa.
"Please sis mik'a mishi Affan."
karb'an yaron tayi sannan ta matso kusa dashi ta kontar da yaron kusa dashi.
murmushi tayi tare da cewa.
"Tab amman suna kama kam kamar d'anshi."
Murmushi Raihana tayi tare da cewa.
"Haka babanshi ma ke cewa wai kamar Hamma Saifuddeen ne ya haifeshi."
Hayatuddeen ne ya d'an sosa k'eya tare da cewa.
"Da yayi k'aton kai kuma sai ace dani yake kama."
dariya Amina tayi tare da cewa.
"Ai kaima ba k'aton kaine da kaiba gashinka ne ba irin nasuba sun fika gashi mai sulb'i naka nada d'an tauri gashi ka tarashi da yawa."
daga nan sukayi d'an hira sannan Amina tace.
"Ni zan tafi naga Dr Aliyu na kirana, saida safenmu."
mik'ewa Raihana tayi tare da cewa.
"Muma yanzu zamu tafi."
Hayatuddeen kuwa cikin d'an d'aga sauti yace.
"Gobe zakizo da wuri ko kafin mu tafi?."
juyawa Amina tayi ta kalleshi sannan tace.
"Aikin dare ne dani ai anan cikin asibiti zan kwana gobenma sai bayan azahar zan koma gida dan akwai aikin da zamuyi."
sunkuyowa yayi ya ciccib'i Affan ya sab'a a kafad'unshi sannan ya kalli Hammanshi tare da cewa.
"To Hamma saida safe."
kai ya gyad'a mishi kana ya kalli Raihana da take gyara mishi mayafin jikinshi tana mishi sannu.
suna gab da fita masu kwana dashi suka shigo,
dan haka suka fita da sauri dan sunce suyi maza su tafi dan ya kamata ace yayi bacci yanzu.
Suna fitane Hayatudeen ya mik'awa Amina wayarshi tare da cewa.
"Yauwa samin number ki."
karb'a tayi tasa mishi number ta sannan ta mik'a mishi wayar tasa,
daga nan sukayi sallama ita tayi office d'in doctor Aliyu,
su kuma Ayuba ya d'aukesu suka tafi gidan Ya Rabi'u.
Ya Adnan kuwa yana zaune shida Rahmanshi yaji shigowan sak'o a hankali ya jawo wayar tashi yana dubawa yaga alert ne cikin mmki ya zaro idanu ganin kud'in har naira million uku a hankali yace.
"Jonapwd, k'ungiyarsu ishaq ne kenan fa to kud'in meye wannan?."
da sauri ya amsa kiran ishaq da ya shigo wayarshi yanzu cikin kad'uwa yace.
"Salamu alaikum ishaq wannan kud'in fa?."
cikin nitsuwa yace.
"Tallafin k'ungiya ne kan jinyar cutar Saifuddeen, a wurin adda Rahma na samu account number ka, da zan tura a account d'in Saifuddeen to nasan ay yarda ayi amfani da kud'in in ya yardama nasan in ya dawo zaice zai maidawa k'ungiya kud'inta, Shiyasa nake neman al
'farma kada ku gaya mushy,Ya Rabi'u ma ya turawa Ahmad one million zaku d'an rik'esu dan hidimar da yawa shima Ahmad saida ya Rabi'u ya nuna b'acin kafin ya amince da kud'in."
sosai ya Adnan yayita godiya yayinda shi kuma da al'jihunshi ya biya kud'in jirgin shida su baki d'aya.
Rahma kam har kuka tayi tanayi musu godiya.
Washe gari k'arfe tara dai-dai duk suna cikin asibitin dan k'arfe tara da rabi jirginsu zai tashi.
Suna cikin d'akin masu kula dashi sun canza mishi kaya sun gyarashi,
Dr Adnan kuwa yana office d'in Dr Aliyu,
yana bashi duk wasu takardun binciken lafiyar da sukayi mishi.
Rahma, Raihana, Raliya, Hayatuddeen, Ahmad, Ya Rabi'u kuwa duk suna wurin Saifuddeen d'in
Amina ce ta shigo cikin nitsuwa tazo ta bashi magungunanshi sannan ta had'a sauran ta kullesu a leda tare da mik'awa Dr Adnan daya shigo yanzu,
yana cewa.
"Rahma ku fito ku tafi Ayuba na jiranku,
zai fara biyawa kaduna ya sauk'i Raihana ku kuma zai wuce daku gombe,
Raliya ki kula da Ummi sosai."
Ahmad ne ya kalleta tare da cewa.
"Goggo Dada ma taje tana can dan gaba d'aya Ummi bata cikin nitsuwa shiyasa nacewa Goggo Dadan taje ta d'an d'ebe mata kewa na kwana biyu."
kai ta jinjina tare da cewa.
"Allah ya kaiku lfy ya bada sa'an aikin da za'ayi mishi."
Amin Amin sukace baki d'aya,
sannan Adnan ya kalli Rahma cikin kula yace.
"Please ki kula da kanki kada kiyi ta kuka,
kinga kinada larurar da ba'a son kina yawan shiga damuwa,
kiyi ta shan mgninki kan lokaci,
nima Next two weeks zan dawo in Allah ya yarda."
kai ta gyad'a kana ta mik'awa Saifuddeen hannu sukayi musabaha tare da cewa.
"Ka yafe min d'an uwana ban saniba ko in haihu lfy ko akasin haka,
in Allah yasa da sauran ganawarmu to Allah ya had'amu kan Al'khairi in kuma baka dawo ka sameni a rayeba,
amana da tarbiyar su Faruq tana gareka."
ina Raliya kam juyawa kawai tayi ta fita,
hakama Raihana sai dai ita tana kuka ta fita,
ita kuwa Rahma shafa fuskarshi tayi tare da juyawa tabi bayan k'annenta,
tana isosu ta shiga mota Ayuba yaja suka tafi.
Su kuwa Hayatuddeen ne ya had'e woyoyin Hammanshi ya zurasu a jakar system d'in shi sannan yabi bayan Ya Ahmad da Dr Adnan dake biye da bayan Nurses guda biyu da suke rik'e da d'an k'aramin gadon da ake d'aukar masu irin larurarshi.
Cikin motar asibiti suka sashi,
Ya Adnan ne ya shiga sannan driver ya shiga suka tafi Airport.
Ahmad da Hayatuddeen kuwa Ya Rabi'u ne ya d'aukesu a motarshi sukabi bayansu,
k'arfe tara dai-dai suka shiga cikin international airport Abuja.
Bayan duk matafiya sun shiga kowa ya zauna mazauninsa, 9:30 Am jirginsu ya d'aga zuwa k'asar India cikin babban birnin New Delhi.
Bayan lokaci mai tsawo suna ratsa gajimare jirginsu yayi sauk'an ank'ulu cikin Indara Gandhi international Airport Delhi.
Bayan duk an fito ma'aikatan lfy na cikin jirgin suka fito da Saifuddeen wanda yana bacci. Ahmad da Dr Adnan da Hayatuddeen suna biye dasu a baya har gaban wata motar asibiti,
nan suka shiga kai tsaye driver yaja suka tafi,
kusan tafiyar awa d'aya da rabi sukayi sannan suka isa cikin harabar wanni tamfatsetsen asibiti mai tsananin azabar kyau da d'aukar hankali,
suna fitowa Ahmad da kanshi ido ya zaro tare da cewa.
"Tsarki ya tabbata ga ubangijin talikai mai sammai da k'assai."
Dr Adnan da kanshi kyawun asibitin yayi matuk'ar girgizashi,
Auta kuwa a hankali Hayatuddeen ya zuro k'afafunshi daga cikin motar,
fitowa yayi tare da d'aga kanshi ya zaro idanshi da k'arfi ya kalli can! can!! can!!! Saman bene na k'arshe inda ya zubawa rubutun sunan shahararran asibitin da duniyar New Delhi ke ji dashi.
*SUPER SPECIALTY SAFDARJUNG HOSPITAL* da sauri ya dawo da kanshi k'asa a hankali yayi wani irin s...!
BY
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:53 PM - Ummi Tandama: πππππππππππππ
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 20*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
πππππππππππππ
Sassanyan ajiyan zuciya yaja a hankali,
ido ya lumshe tare da bud'esu ya juya ya kalli gabas da yamma kudu da arewa, a fili yace.
"Gari banban Allah d'aya."
Ahmad ne ya juyo ya kalleshi tare da cewa.
"Ko wanne wuri da irin kalar ni'imar da Allah yake musu."
da sauri suka juyo suka kalli ya Adnan dake ce musu.
"Ni zan shiga ciki zamu isa wurin Dr Acash prasat zan kama mana layi,
duk dai Dr Aliyu ya mana hanyar ganinshi a watannan to dole sai munbi layi.
So kai Ahmad ga can taxi ku shiga sai ku duba mana hotel nan kusa mu samu masauk'i."
cikin gamsuwa da hakan Ahmad yace.
"To ba matsala bari mu d'auki kayan mu."
Shi kuwa Hayatuddeen da sauri yabi bayan nurses da suka fito da Saifuddeen dake kan gado,
yana isa ya bawa Saifuddeen hannu tare da cewa.
"Zamuje nan kusa, ya Adnan zai shiga ciki da kai."
kai ya gyad'a mishi alamar sai sun dawo hakama Ahmad yazo ya salla meshi sannan Dr Adnan yabi bayansu, suka nufi cikin ainihin asibitin,
tafiya kad'an sukayi suka ratsa cikin wani babban corridor mai girma,
tafiya yar kad'an suka isa bakin wata babbar k'ofa,
suna bud'ewa wasu nurses d'in suka karb'eshi,
kana wad'an nan suka juya sukayi baya,
su kuma wannan da suka k'arbeshi sai suka canza mishi gado suka d'auranshi kan irin k'ananun gadajen tura marasa lfyn,
sannan da sauri Dr Adnan kuwa ya mik'a d'aya daga cikinsu wata takarda,
bayan ya karb'a ya duba sai ya juyo ya kalli d'aya nurse dake tura gadon yayi mishi mgna cikin indiyancin.
Sai kuma suka canza hanya suka fuskanci wani ratsetsen gini mai azabar kyau amman shi ba benaye bane.
suna isa harabar wannan wurin wasu nurses d'in suka karb'eshi kana suka basu wannan takardar da takeda tambarin National Hospital Abuja,
a k'asa kuma ga sa hannun Dr Aliyu,
can gefe kuma ga shaidar transfer zuwansu wannan asibitin da.
shi dai Dr Adnan binsu yake a baya.
A hankali suka bud'e wata k'ofa mai girma suka shiga Dr Adnan na biye dasu a baya,
yana sa k'afarsa cikin Reception d'in nasu yayi wani irin ajiyan zuciya dan wani azabebben sanyi da ya cika wurin,
gaba d'aya reception d'in cike yake mak'il da mutane duk da girmanshi sai dai duk ana zaune bisa tsari ba hayaniya,
shi kuwa Saifuddeen kanshi ya d'an juya ya kalli gefen hagunshi da damanshi,
jerin gadaje ne a gefen hagunshi mutane na konce a Kai,
d'aya gefen kuwa kekunan weelchair ne a jere wasu na zazzaune a ciki.
gefen gadajen aka tura gadon da Saifuddeen ke kwance,
sannan nurse d'in ya yafito Adnan kana suka nufi gaban inda nurses ke zaune suna bada kati dama masu bud'e folda
suna isa suka mik'awa d'aya daga cikin matan dake wurin takardar,
mgna suka d'anyi cikin yarensu da Adnan baya ji ya dai ji suna kiran Nigeria,
sai kuma nurse d'in da aka kira da Divia ta juyo ta kalli Adnan tare da mishi tambayar ina fayel nasu na asibitin da aka turosu nan cikin turanci.
Da sauri ya mik'a mata fayel d'in amsa tayi sannan ta had'a da takardar da wannan d'in ya bata,
juyawa tayi ta d'auko polder sannan ta bud'e wanna fayel d'in kana ta d'auki biro ta fara rubutu a saman poldern sai kuma ta fara bud'a fayel d'in nan ta d'anyi 'yan rubuce-rubuce sannan ta mik'awa Adnan hand card data zaro cikin polder d'in,
amsa yayi ya duba kasan cewarshi Dr ras ya gane rubutunsu na doctors da yafi kama da jagwalgwale,
kai ya jinjina ganin bata saurari tambayarshi sunan mara lfy da shekaru ba duk ta samesu cikin fayel d'in da suka zo dashi.
kai ta sunkuyar kana ta matso kusa da system d'in dake gabanta a hankali ta fara sassarafashi,
daga bisani ta d'ago kai tace mishi yaje ya zauna za'a nemeshi.
Gefen da Saifuddeen yake yaje,
nan ya samu yana bacci dan ya samu irin sanyin da jikinshi ke buk'ata, kasan cewar masu larurar cutar lakar jiki suna da yawan jin zafi, shiyasa suΖe matuΖar so da jin daΙin wurin dake wadace da tsabta da sanyi,
fita yayi daga cikin wurin hanyar da suka bi sukazo ita yabi d'an suna wucewa yaga wani d'an k'aramin masallaci a hanyarsu,
yana isa wurin yayi Al'wala kana yayi sallan azahar da la'asar da niyar k'asaru.
yana idarwa ya mik'e da sauri ya koma.
Still har yanzu yana bacci hakan ne yasa ya koma gefe ya zauna,
yana kallon yadda aketa shiga da fita.
In an d'an jima wata nurse ta fito ta d'ebi wasu polder ta shiga dasu,
hakama wata bisa dukkan alamu likitocin guda uku ne suke duba marasa lfyan,
a hankali ya fara kallon rubutun dake saman k'ofofin office d'in na forko ansa Dr Biru Sahastara Dubbe,
sai na tsakiyar da akasa Dr Acash prasat,
sai na k'arshen da aka saka Dr Abdul Malik Khan.
kai ya meda ya jingina da kujera dan ganin dare ya rufa,
kuma da yawa sunata fita.
Da sauri ya d'ago kanshi jin motsin bud'e k'ofa ta tsakiyar nan,
ido ya zubawa saman aljihun rigar mutumin inda aka rubuta Dr Biru S D,
ga kuma nurses guda biyu suna biye dashi a baya yayinda wani kuma yake rufe k'ofar office d'in.
Bai gama nazartan mutuminba ya kuma hango an bud'e d'aya k'ofar ido ya zubawa saman al'jihun rigarshi inda aka rubuta Dr Malik Khan.
tafiya yakeyi cikin nitsuwa kanshi d'auke da hular tab'a kaji hadis Ιin nan,
bisa dukkan alamu nurses dake binshi a baya ma,
musulmaine,
yana isowa tsakiyar Reception d'in sai ya d'aga hannunshi duka biyu ya fiskanci mutanen dake gefen damanshi yace.
"Assalamu laikum."
kad'an daga ciki da suka kasance musulmai ne suka amsa da.
"Wa alaikassalam."
sai ya kuma d'an tsayawa tare da kallon marasa lafiyan kana yace.
"Lah ba'as d'uhuru in sha Allah."
sai ya kuma juya gefen hagunshi in da ya kuma yi musu sallama,
kasan cewar Adnan ne kad'ai musulmi a layin shiyasa shi kad'ai ne ya amsa da.
"Wa alaikassalam."
cikin kula ya kalli Adnan tare da mishi murmishi ya tambashi shi d'an wacce k'asar ce. Cikin jin dad'i Dr Adnan yace.
"Nigeria."
sunanshi ya tambayeshi ya gaya mishi sanna ya kuma tambayarshi su sabbin zuwa ne ko,
dan duk wad'an nan sauran sun kai kwana huΙu zuwa biyar suna bin layi,
kuma ba'a fara k'arb'an sabbin zuwa ba.
mik'ewa Dr Adnan yayi ya matso kusa dashi cikin nitsuwa da iya sarrafa harsher ya mishi bayanin da zai fahimta sosai a matsayinsu na doctors kuma kusan duk abu d'aya suka karanta,
ya k'ara da mishi bayanin doctor daya turosu da kuma sani Dr Acash prasat.
Kai ya jinjina cikin gamsuwa sannan ya tamb'ayeshi ina mara lfyan,
da sauran ya nufi gadon Saifuddeen binshi yayi a baya cikin k'are mishi kallo yake tambayarshi wai Saifuddeen ba d'an Nigeria bane ko.
cikin sakin fuska Dr Adnan yace mishi cikekken d'an Nigeria ne.
kai ya rusunar ya