Showing 147001 words to 150000 words out of 176868 words

Chapter 50 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

mata ba, da tunani kala-kala acikin ransa harsuka iso gaban tangamemen gate ɗin gidan,  horn Sule driver yayi inda take maigadin gidansu Zaleehan ya wangale musu gate,  acikin compound ɗin gidan Sule driver yayi parking motar,  daidai lokacin Ya Aminu ya fito daga ɓangaren Mamy hango Saifuddeen dake ƙoƙarin fitowa amota da yayine yasanyashi ƙarasowa garesu.

Da turarenta mai azababben ƙamshi ta feshe gaba ɗaya jikinta, wani ɗan siririn mayafi mai kalan kayanta ta yafa daga kan wuyanta zuwa ƙugunta, yanayin yanda dogon baƙin gashinta ya kwanto akan gefen wuyanta shi ya matuƙar ƙara ƙawata ado da kuma kyawunta, wani takalmi mai uban tsini ta sanya aƙafafunta, cikin takunta mai nuna tsantsar aji, ƙasaita, wayewa, da kuma jinkai tafito zuwa falo, nan ta iske Mama da kuma Zahira suna hira, duban tsab Mama tayi mata fuska shafe da toka tace.
"Sai ina?."

Zama tayi akan hannun kujera tare da ɗan turo bakinta gaba murya acushe tace.
"Makay zanjeni yin shooping".
Baki Mama ta taɓe tare da gyara zamanta ta fuskanci Zaleehan, fuskarnan tata sam babu alaman fara'a tace.
  "Ya kukayi da banzan gurgun da yazo wajenki jiyan?."

Lokaci guda yanayin fuskar Zaleeha ta sauya kala domin tunowa da baƙin cikinsa da tayi, cikin bayyana tsantsar tsanarsa da tayi tace.
  "Na musu bana sonshi." 
Ƙwafa tayi tare da ɗan gyara zamanta tacigaba da cewa.  "Wai harni wani banzan MUSAKI zaizo yace yana son ƴata hmm!."
Murmushin jin daɗi Mama tayi tare da ci gaba cewa. 
"Ae ni banga laifinsa bama, dama ni tuncan wannan ɗan iskan aikin naki na Babu maraya  ne, ko Nakasa ba kasawa bace ko mene yake da suna, sam ba ƙaunarsa nake ba, amma dayake ke uwar taurin kaine haka kike zuwa cikin nakasassu musakai kita washe haƙora kina naɗan muryarsu wai ke adole mai tausayi ƙaunarsu, to ai gashinan kin fara ganin sakamako tunda dai har Kurma kuma gurgu yasamu daman biyoki har gida da maganar soyayya.

Hannu Ya Aminu ya bawa Saifuddeen suka gaisa amutumce, nan Ya Aminu dakansa yayiwa Saifuddeen jagora zuwa BQ, shikam har acikin ransa ya yaba da nutsuwa da kuma haiba haɗi da kwarjini irinta Saifuddeen, koda Ya Aminu yayi masa jagora zuwa BQ cewa yayi dashi bari ya ƙira masa Zaleehan, cikin body language Saifuddeen yace "To."
Tare da yiwa Ya Aminu'n godiya.

Ɗan ƙaramin bakinta taƙara cunowa gaba, tare da gallawa Zahira dake ta dariya ƙasa ƙasa najin cewa wai kurma kuma gurgu yazo wajen yayartata da ƙoƙon barar soyayya, baki Zaleeha ta buɗe don kaftawa ƙanwartata rashin mutumci shigowan Ya Aminu ne yasanyata saurin haɗiye maganan dake ranta, dan da tayi niyan aunawa mayataccen gurgun zagine, kana daganan saita ci mutumcin Zahira dakeyi mata dariya.
Duban Zaleeha Aminu yayi fuskarnan tasa sam babu alaman annuri akanta, cikin tsare gida yace.  
"Ke Zaleeha kije kina da baƙo a Boys Quaters."

Wani irin faɗuwa gaban Zaleeha yayi, cikin sarƙewar murya tace.
"Ni...Ni kuma Ya Aminu?."
Harara Ya Aminu ya watsa mata cikin yanayinsa na rashin fara'a agaresu yace. "Da akwai wata Zaleehan agidannan ne bayan ke? ko kuma aduk gidannan akwai ƙatuwar gantsamemiyar budurwa sama dake? Maza tashi kije Saifuddeen ne yana jiranki banason shashanci!." 

Idanu Zaleeha ta zaro, lokaci guda jikinta yasoma ɓari kamar mai aljanu, sam ta manta da cewa Ya Aminu ne agabanta cikin tsananin ɓacin rai tace.
"What! Mayataccen gurgun nanne yaƙara dawowa, aikuwa saidai ya shekara don babu inda zanje!!".
Taƙirasa maganan cikin rufewar ido.

Cike da mamaki Ya Aminu ya matso inda take azafafe, cikin tsananin ɓacin rai yace "Me kikace? Maimaita nasakeji don banji da kyauba!".

Shiru Zaleeha tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa, wani irin tafarfasa ranta keyi mata, ji take kamar ta kurma wani uban ihu ko zatasamu salama acikin rai da zuciyarta.

Jin tayi shiru batace komai bane yasanya Ya Aminu daka mata tsawa cikin faɗa yace "Kintashi kinjene ko saina ɓaɓɓallaki anan wajen shashashar yarinya da batasan ciwon kanta ba!!."

Jikin Zaleeha narawa ta-tashi da sauri har ƙafafunta na harɗewa haka ta nufi hanyar fita daga falon tuni wasu irin hawayen baƙin ciki sun cika idanunta, fuuuu haka Ya Aminu ya fice daga cikin falon,  tsuka mai ƙarfi Mama tayi cikin baƙin ciki da takaicin Mijin ƴartata Maryam wato Ya Aminu tace. "Wallahi indai akan Zaleeha ne babu wanda ya isa yayi mata dole, idan kuwa har dolennema za a mata tofa lallai saidai in akan Abdussalam, amma wallahi babu wani matsiyacin gurgu daya isa nahaifi ƴa kuma ya aure ta."
ƙwafa Mama tayi tare da cewa.
"Duk zanyi maganinku ne ae dani kuke zancen!."

Zaleeha kuwa ko gabanta bata gani da kyau saboda tsabar hawayen da suka cika idanunta, wani irin ɗaci na ɓacin rai takeji a maƙoshinta,  cikin ranta wata irin wutar masifa ne ke cinta, yayinda wutan tsanarsa ke ƙara ruruwa acikin zuciyarta,  tana kawowa bakin ƙofan da zai sadata da babban falon BQ ɗin ta tsaya cak,  ƙoƙarin shanye hawayen dake cikin idanunta tayi,  da wani irin ƙarfi ta bugi ƙofan falon, cikin takunta mai ɗauke da isa da kuma tsantsar rashin mutumci ta kutso kanta cikin falon.
Idanunsu ne suka sarƙe acikin najuna domin dama tuntuni idanunsa akan ƙofar shigowa falon suke.
Wata uwar harara mai ɗauke da tsantsar tsana, Zaleeha ta watsa masa, cikin takunta dake nuna tsantsar rashin mutumcin da takeji dashi ta ƙaraso cikin falon, ƙwas-ƙwas haka sautin takun takalminta ke amsa gaba ɗaya ilahirin falon, sam idanunta ya rufe da tsana, haɗi da masifar dake cinta arai, cike da son ƙuntata masa ta tsaya kusa dashi tare da sanya hannayenta ta kama ƙugunta,  amasifance tace.
  "Waikai wani irin maye ne? ina tunanin tun a jiya nasanar dakai cewa bana sonka na tsaneka!".
ɗan shiru tayi tare da dubansa sama da ƙasa da sauri ta janye idanunta daga nashi dan wani irin bugu da zuciyarta keyi a duk sanda suka had'a ido,
tabbas yayi kyau sosai acikin idanunta amma masifane kawai ke ɗawainia da ita, cikin gatsali tace.
"Oho wato kazone don ka nunamin naci da kafiya irintaku ta kurame ko?  to bari kaji duk bala'in nacinka bazan taɓa sonka ba, na tsaneka wallahi natsani ganin fuskarka, waima shin kai bakasan cewa kai nakasashshshe bane? gurgu, kurma, sannan kuma maye" ɗan numfasawa tayi tare da sake matsowa kusa dashi cikin son ƙunsa masa baƙinciki tace.
  "Kakalleni da kyau koda a iya fuskata aka tsaya kai kasan niba matar yara bace, bare kuma irinka wanda bazai taɓa amfanata da komai ba, ginannen taɓo mai kama da dutsi!".
Taƙare maganar tana jujjuya masa idanu tare da murguɗa baki, wai ita ala dole hakan masifa takeyi.
Tunda tashigo cikin falon yake kallonta har kawo yanzu, wani irin sanyine yaji yana ratsa zuciyarsa, sosai abubuwan Zaleehan ke bashi dariya, duk acikin abubuwan da ta faɗa babu ɗaya wanda bai fahimci me tace ba sai dai ya gane tana tsoron kwayar idanunshi, acikin ransa yace.
"Ginannen taɓo ko, hmmm zakisha mmki!."
Ƙawataccen murmushine ya bayyana akan fuskarsa,  cikin tsananin takaici Zaleeha ke kallonsa, zuwa yanzu kam yakaita bango don yagama ƙureta ahatsale tace. 
"Kayi dariya zama kayi kuka da waƴannan fitinannun idanun naka masu kama dana zuri'ar mayu, wallahi-wallahi, idan baka rabu dani ba nice nan ajalinka, me yasa bazaka gane cewa na tsaneka bane? Meyasa bazaka kalli wutar tsanarka dake ruruwa acikin idona ba? kaduba kaga na tsaneka nace, na tsaneka!!!".
Cikin tsananin ƙaraji take maganan yayinda hawaye suka cika idanunta, jitake kamar taje ta ɗauko wuƙa ta caccaka masa.
Dai-dai lokaci Sallaman Kaltume mai aikin gidan nasu ya ratsa kunnuwanta,  amatuƙar harzuƙe tajuyo tana kallon Kaltume,  ƙarasowa cikin falon Kaltume tayi hannunta ɗauke da wani babban tray wanda samansa ke ɗauke da bottle water dakuma kayan marmari dangin su Apple da Inibi, akan babban table ɗin dake tsakiyan ɗakin Kaltume ta ajiye tray ɗin, dubanta takai ga Saifuddeen wanda yake kallonta, aladafce tace dashi "Ina wuni ranka shi daɗe!".
Murmushin daya bayyana cikar haiba da ƙwarjininsa yayi inda ya gyaɗa mata kai alamar.
"Lafiya"
Nan Kaltume ta miƙe tafice daga cikin falon aranta tana me mamakin tsananin kyau irin nasa take cewa.
"Duk yanda akayi balarabe ne shiyasa banji ya amsa gaisuwata ba, dadukkan alama baisan ma menace ba, gsky Aunty Zaleeha tayi sa'an miji".

Kaltume na fita Zaleeha tasaki wani mugun murmushi tare da cije laɓɓanta, ahankali ta ƙarasa gaban table ɗin da tray ɗin kayan marmarin yake, ɗaukan tray ɗin tayi tare da juyowa ta kalli Saifuddeen turamasa tiran kusa dashi tayi, ranta aɓace tace.
"Dama nakasassu irinku sunfi buƙatar irin waƴannan abubuwan hala shiyasa kazo nan don kaci ko? Mayunwaci gasunan saikaci ae!".
Tafaɗa tana me tura masa gaba ɗaya tray ɗin,
cikin wani irin yanayi ya rumtse idanunshi da azaban k'arfi, jin zuciyarsa na tafarfasa,
sai kuma ya bud'esu da sauri. Juyawa tayi daniyar barin falon, cikin zafin nama da tafasan zuciya Saifuddeen ya damƙo hannunta tare da hankaɗata kan kujeran dake kusa dashi,
mamaki ɗauke akan fuskar Zaleeha ta zaro idanu tana kallonsa cike da tsoro, domin sam ita batasan ya akayi ba sai jinta tayi akan kujera, cikin zafin nama ya ƙaraso dakekensa har gabanta, ƙafansa ɗaya yasanya ya tokare gefen kujeran yanda babu yanda za'ayi ta iya tashi.
Wani irin horo yashiga yi mata da idanunsa wanda duk rashin kunyarta take kasa kallon cikinsu,
da sauri ta sunkuyar da kanta yayinda k'irjinta ke duka uku-uku,  ga wani iri abu da taji ajikinta, cikin haɗe fuska da tattaro d'an guntun jarumtarta da ragwowar tsiwartata tace.
"Miye hakane dahalla Malam, ni ɗagamin ƙafanka na wuce idan ma maitan nakane yatashi kurwata kur kaci kanka!".
Tafaɗa tana me ƙoƙarin miƙewa tsaye,  da sauri Saifuddeen yasanya ƙafarshi ya tokari guiwanta, da tashi guiwar da azaban k'arfi.
da sauri ta yarfa hannu tare da cewa.
"Wayyo Allah na, mugu'azzalumi, karya min k'afa zakayi ka maidani gurguwa irinka ko?."
bai kulata ba sai k'ara datse mata guiwarta da yayi da tasa guiwar har takai suna iya jiyo hucin numfashin juna, yayinda daddaɗan ƙamshin turarensu ya cakuɗa waje ɗaya, ahankali yashiga yawo da idanunsa akan jikinta, wani irin yaaarrr haka yaji a jikinsa alokacin da idanunsa suka sauƙa kan tudun ƙirjinta, tuni tsikar jikinsa suka soma mimmiƙewa yayinda yaji wani irin feeling ya dirar masa alokaci guda,  idanunsa ya ɗauke daga kan ƙirjin nata tare da sauƙesu akan laɓɓanta, wani irin yawu ya haɗiya amaƙoshinsa tare da ɗan lumshe idanunsa, jiyake kamar ya jawota ta faɗa jikinsa,  yanajin kamar ya ladabtar da ita tahanyar bawa kyawawan laɓɓan  bakinta professional kiss, ahankali idanunsa suka ɗan sauya kala daga farare zuwa yanayin bacci, cikin wani irin salo yasanya hannayensa inda ya tallafo haɓarta, idanunsu ne suka dire acikin najuna da sauri tayi ƙasa da idanunta cikin faɗa tasanya hannunta ta buge hannun nasa daya taɓa haɓanta, cikin son koyan rashin kunya murgud'a mishi baki tace. 
"Ɗan iska kawai!, ai bama sai ka gwadamin a zahirance nagani ba.
Duk wanda yaga waƴannan munafukan idanun naka yasan kai ɗan iskane!!". taƙare maganar tana murguɗa bakinta, wayarta dake hannunta ce takawo haske, cireta a key tayi tare da k'ok'arin duba waye mata flashing,
sam ba zato ba tsammani taji Saifuddeen ya wafce wayar daga hannunta, rai aɓace ta ɗago ta dubesa cikin gatsali tace.
"Bani wayata tunda bada kuɗin Nakasassun guragu na saya ba!".
Ƙin bata wayar yayi gashi gaba ɗaya yayi mata ƙawanya da jikinsa, sannan kwarjininsa ya cika mata ido.

Saifuddeen kuwa number'nsa ya sanya acikin wayan inda ya danna dialing, take wayarsa dake cikin al'jihun gaban rigarsa ta soma ƙara, ganin numbern ta yafito acikin wayarsa ne yasanyashi katse ƙiran kaitsaye wajen text messages ya nufa,  sannu ahankali ya rubuta kalamai masu hikima inda yayi sending zuwa phone ɗinsa, saida ya tabbatar da cewa saƙon yashiga wayarsa sannan ya maida idonshi kanta.

Itakuwa Zaleeha cikin ƙufula take binsa da harara, ganin yanda ya tsareta da idanune yasanya a hatsale ta wafce wayarta dake hannunsa, miƙewa tsaye tayi tare da watsa masa harara cikin yanayi na tsanarshi tace.
"Kada ka taɓa manta cewa bana sonka, sannan kuma na tsaneka tsana mafi mufi, cigaba da kusantata tamkar kusantan ajalinka ne!".
Tana kaiwa nan azancen nata ta tsallake ƙafarsa ta wuce.
Da kallo Saifuddeen ya bita harta ɓacewa ganinsa, murmushi yayi tare da cije laɓɓansa, cikin zuciyarsa yace.
"Kin gama naki daga yau ɗin saura nawa ƴan mata yanzu lokacina ya fara."
cikin nutsuwa ya shiga tura kekensa har ya fice daga cikin falon, koda ya kawo compound ɗin gidan nan ya iske Ya Aminu wanda fitowarsa kenan aɓangaren Baba Malam, ganin Saifuddeen yasanya Aminu cewa.
"Har zaku tafi?"
Kai Saifuddeen ya jinjina masa fuskarsa ɗauke da murmushi alaman.
"Eh". kana cikin body language ɗinsa yace "Yanason gaisawa da Baba Malam idan yana gida."
Murmushi Aminu yayi don sam baigane me Saifuddeen ɗin ke nufi ba, kasancewar ba sosai yake gane body language ba.
Ganin cewa Ya Aminun bai gane me yake nufi ba, yasanya shi zaro wayarsa daga al'jihu inda yayi rubutu ya miƙawa Ya Aminu'n, amsan wayan Ya Aminu yayi, koda ya karanta saƙon murmushi yayi, cikin yabawa da hankalin Saifuddeen ɗin yace.
"Masha Allah, aikuwa Baba Malam na ciki muje sai namaka jagora."

Ya Aminu ne yayiwa Saifuddeen jagora har zuwa cikin haɗaɗɗen falon na Baba Malam.

Ganin Saifuddeen yasanya fara'ar dake kan fuskar Baba Malam ƙara faɗaɗa, cikin farin ciki yace.
"A'a ɗalibina Saifuddeen kaine ke tafe, Masha Allah sannunka da zuwa."
Murmushi Saifuddeen yayi cikin hikima da ladabi yagaishe da Baba Malam ɗin, fuska asake Baba Malam ya amsa tare da tambayansa ya bayan rabuwa, nan suka ɗan taɓa hira tsakanin Baba Malam da Saifuddeen, yayinda Ya Aminu ke sa musu baki, Ya Ahmad ne yashigo cikin falon na mahaifinsa, ganin Saifuddeen ya sanyashi faɗaɗa fara'arsa inda suka gaisa amutumce. Nan suka sake ɗan taɓa hira wanda Saifuddeen ke ɗansa baki ta hanyar body language ɗinsa.
Wayarsa yaciro inda ya miƙawa Ya Aminu, bayan yashiga text message saƙon da ya tura da kansa ta wayarta ya bayyana akan screen ɗin wayar tasa, koda Ya Aminu yakaranta saƙon murmushine ya faɗaɗa akan fuskarsa cikin jin daɗi ya miƙawa Ya Ahmad, Ya Ahmad ma yana karanta saƙon yasaki wata nannuyar ajiyar zuciya sosai hakan yayi masa daɗi, amincewa da auren Saifuddeen da Zaleeha tayi, abun farin ciki ne agaresu, domin samun nagartaccen namiji kamar Saifuddeen amatsayin suruki cikin zuri'arsu abun alfaharine sosai.
Miƙawa Baba Malam wayar Ya Ahmad yayi, koda Baba Malam yakaranta saƙon da aka rubuta kamar haka.
_"Ni ZALEEHA NA AMINCE DA AURENKA Hamma SAIFUDDEEN SABODA HAKA KATURO MAGABATANKA WAJEN BABANA DON ATSAIDA MAGANAR Aurenmu."_

Wani irin ingantaccen farin cikine ya cika zuciyar Baba Malam jin cewa Zaleeha ta amince da Saifuddeen takuma tsai dashi a matsayin gwaninta, cikin tsananin farin cikin daya kasa ɓoyuwa akan fuskar Baba Malam ya ɗago ya kalli Saifuddeen wanda ya sunkuyar da kansa ƙasa, cikin zuciyarsa yace.
"Nawa wasan ya soma Zaleeha daga gobe idanunki zasu fara kuka kamar yadda kikasa Ummina kuka, kuma Insha Allah ni da kika ƙira Ginannen taɓo kuma dutse, niɗin nanne zan-zamo mijinki!."

"Masha Allah, Haƙiƙa naji daɗin kasancewar haka sosai Saifuddeen, saboda haka ni mahaifin Zaleeha na baka Zaleeha sannan koda yaushe kashirya kana iya turo manyanka su kawo sadaki don atsaida ranar auren ku da ita!."

Wani irin tsananin farin cikine suka cika zuƙatan Ya Ahmad da kuma Ya Aminu, shikuwa Saifuddeen faɗan farin cikinsa ma ɓata lokaci ne, domin kallon fuskarsa kaɗai da ƙwayoyin idanunsa sun isa sanardakai farin cikinsa.

Cikin aminci da salama Saifuddeen ya miƙa godiyarsa ga Baba Malam harma dasu Ya Ahmad, nan sukayi sallama cikin mutumta juna har bakin mota Ya Ahmad da Ya Aminu suka raka Saifuddeen saida sukaga ficewar motarsa acikin gidan kana suka juya suka koma wajen Baba Malam don su tattauna yanda bikin zai kasance...

A cikin mota kuwa wani irin murmushi Saifuddeen yayi tare da sake jingina bayansa ajikin kujeran motar, lumshe idanunsa yayi yana me tunano haɗaɗɗiyar surar jikinta, tabbas yaƙudurta aransa cewa zai shayar da ita ruwan mamaki, aduk sanda ya aureta kuwa saiya nuna mata cewa NAKASA BA KASAWA BACE...!





By
*GARKUWAR FULANI*


             *NAKASA BA KASAWA BACE*

                            *PAGE 29*

                             *NA*
           *AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Daga Gidansu Zaleeha kai tsaye unguwar tudun wada suka nufa wato gidan Baba Bello,  aƙofar ɗan madaidaicin gidan na Baba Bello Sule driver yayi parking motar, both ya buɗe inda ya cirowa Saifuddeen kekensa, buɗe murfin motar Saifuddeen yayi, inda dakansa  ya yunƙuro ya hau kan keken nasa.
Yana gama dai-dai ta zamansa akan keken,  Jafar almajirin Baba bello yafito daga cikin gida, ganin Saifuddeen yasanya Jafar sakin murmushi cikin kulawa yaɗan rusuna tare da cewa. "Hamma Saifuddeen sannu da zuwa."
Murmushi Saifuddeen yayi masa tare da jinjina masa kai alaman.
"Yauwa."
Cikin sauri Jafar yajuya ya koma cikin gida, nan ya iske Baba Bello dake zaune yasanar dashi zuwan Saifuddeen,  cikin hanzari Baba Bello yazura takalma aƙafansa,  inda kai tsaye yanufi hanyar fita daga cikin gidan.
Fuska ɗauke da fara'a Baba Bello ya tarbi Saifuddeen,  nan yayiwa Saifudeen ɗin iso zuwa cikin ɗakinsa dake hanyar soro.
Bayan sun zauna ne Jafar ya kawowa Saifuddeen ɗin ruwa acikin wani babban plastic jug,   kofin ruwan Saifudeen ya ɗauka tare da kaiwa bakinsa, tuno da yanda Zaleeha ta turs masa kayan fruits gabanshi ga kuma tsoronshi cikin ƙwayar idanunta tono hakan ne yasa yayi,  yasanyashi sakin murmushi, ɗan kaɗan yasha ruwan gudun kada Baba Bello yaji ba daɗi, cikin kulawa Baba Bello ya dubeshi kana yace.
  "Sam ban tsammaci zuwanka ba Saifuddeen, ai da nasanya Innar ku (Matar Baba Bello) tayi maka kwaɗon zogale da tumatur, gashi kuma yanzu batanan taje kitso."
Murmushi Saifuddeen yayi tare  da sadda kansa ƙasa, cikin body language ɗinsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login