Showing 81001 words to 84000 words out of 176868 words

Chapter 28 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

wasu k'ofofi d'aya k'ofar tana gab da k'ofar shigowa office d'in wanda bisa dukkan alamu bathroom ne,
sai gefen dama da k'ofofi guda uku ke jere bisa dukkan alamu office din shugabannin k'ungiyar ce,
kana gefen k'ofofin sai akayi wani dan steps guda biyar in ka haura wani d'an madaidaicin table ne na farin gilas mai ruwan garai-garai sai kujera d'aya rak a gaba kana sai d'aya a bayan table d'in sai tarin na'urai wanda sun kai bakwai.
sai gefen hagu nanma haka tsarin yake sai dai shi sai ka d'an ratsa cikin wani corridor mai d'an fad'i.

Tana shiga wannan mutumin daya bude mata k'ofar yace.
"Barka da zuwa Zalihan nakasassu."
murmushi tayi kana taja kujera ta zauna tare da cewa.
"Ya Ishaq fa baya nanne?."
ba tare data jira amsarshi ba taci gaba da cewa.
"Ya naji ma'aikatan naku shiru yau ba mutane?."
bisa kujerar gefenta ya zauna tare da cewa.
"Ishaq yana Abuja, mutanen mu kuma duk suna fad'ar jiha sunje kai gaisuwa ga mai martaba."
mik'ewa tayi taku biyu zuwa uku ta nufi gaban firij,
tsayawa ta yi jin abinda Sani ke fad'in.
"Ayyah kiyi hak'uri ban kawo miki abin shaba, sorry dawo ki zauna zan kawo miki."
cikin yanayin sabo dasu tace.
"Wai ku anya kuwa ku makafi ne? yanzu ya akayi kasan gaban firij na nufa?."
murmushi yayi tare da d'an kaikaice kunnenshi irin yadda makafi keyi kana yace.
"Motsinki da takun tafiyarki ne ya ganar dani inda kika nufa,
ke har yau kin kasa barin mmki kan lamarinmu, abinda baku saniba ku.
Mu nakasassun munada experience sama daku masu gadara da cikekkiyar halitta."
murmushi tayi bayan ta dawo ta zauna,
robar faron ta bud'a bayan ta sha kana tayi hamdala dan ta ɗanji tafasar da zuciyarta keyi ya ɗan ragu aje goran tayi sannan tace.
"Toh Ya Sani ni zan wuce tunda ciyaman bainan,
wata k'il sai next week, zan shigo, dama zan tattauna da sune a shirin da za'a haska a tasharmu na Farin Wata, dan yace min wannan karon da kurame zan tattauna, to gashi Malam Ishaq bai sanarmin bama a kan baya nan da ban zoba."
"To ba matsala, Allah ya kaimu lokacin, wannan karon kam hirar da kurame za'ayita?."
ya k'arishe mgnar cikin neman k'arin bayani tare da
mik'ewa yabi bayanta kana suka fito tare har gaban motarta,
sannan tace mishi.
"Eh shiyasa dole su sai a tasharmu ta TV za'ayi hira dasu. Yace min da wani babban abokinshi zamu zanta wanda shine Garkuwar asusunku, da nike ta cewa ku fasa ku bani in canza mota, kukak'i, saida kuka bari yan kalare suka fasa min glass, sannan Ya Ahmad na ya canzamin, kuma a kanku motata ke mutuwa kullum ina yawon binku da k'wak'ulo baiwarku."
dariya yayi sosai kana yace,
wannan asusun namune mu yamu."
itama murmushi tayi kana ta shiga mota sannan suka sallami Juna.
Daga nan ya koma ciki.
Ita kuma ta ja mota,
kai tsaye hanyar Vision fm Gombe ta nufa, sanin ana jiranta yasa take sharara gudu kamar babu gobe kana dama d'abirta ne bawa mota wuta,
tana isa harabar maikatar tasu tayi parking kana ta fito sauri-sauri gudu-gudu ta shiga cikin ainihin wurin kai tsaye d'akin tace murya ta nufa,
tana shiga tazo dai-dai masauk'in bakinsu,
taji abokin aikinta Rabeel na cewa.
"M.B. S Dukku, sai yanzu ne, ya mutanenki?."
bata kai ga amsa mishiba taji muryar d'aya daga cikin abokan aikin nata ta bayanta tana cewa.
"M.B Dukku, sai yanzu tun d'azu Abdulsalam da tawagarshi ke nan ya kasa ya tsare sai raba ido yake ta ina zaki fito bai saniba kina can cikin mutanen ki Nakasassu."
tsaki taja tare da cewa.
"Na damu dashi, in yayi ya haƙura ya bari d'an marasa zuciya kawai."
jin wani ya kuma kiranta yasa tace.
"Kai dan Allah ku barni in huta ni dai ba dama ku barmin suna ya huta, daga mai cemin Zalee sai me cemin B M Dukku sai masu cewa M,B,S Dukku irin Rabeel har Dukkun kawaima zai kirani,
sai yawan kiraye-kiraye kamar makaf.."
sai ta kuma yi shiru bata k'arisa ba.
su kuwa Dariya sukayi baki d'aya, kana Maigado tace.
"Yoh meyasa kikayi shiru? ki k'arisa mana ai mutanenki ne, ga kuma Rabeel d'an had'i kina fad'i zai yad'aki a shirin *Mu daku* ya sanar musu."
ɗan wani guntun murmushi tayi tare da cewa.
"Ai duk had'inshi bazai ci nasara a kanmuba dan sun san Zaleeha tasuce."
dariya suka kumayi dan Zaleeha ta kowace ita kowa natane tanada fara'a da farfar da jama'a kana ga kaud'i da rakad'i awani sashin kuma tanada tausayi da mutunci, kana tana da white blood tanada kwarjini, da shiga rai shiyasa duk inda ta shiga sai tauraronta ya haska sai yawan tsiwa. tsoro kuma tamkar farar kura. sai dai Raveel ya kula kwana biyun nan bata cikin haiyacinta da nitsuwarta.
Zaleeha fara ce k'al irin farin fulanin Dukku.
Wanda dukkan mazaunin gombe ko ince dukkan wanda yasan jamar Dukku yasa fulanine, kana fulanine da sukayiwa sauran tsashi na Gombawa zarrawa a fagen kyau ilimi wadata kiwo noma,
duk wanda yasa mahaifin Zaleeha Malam Bashir Sulaiman Dukku muddin yaga Zaleeha to tabbas zai san ita d'in jininshi ce, haka yasa take tsananin kama da Ya Ahmad d'inta duk da ubane ya had'asu,
Zaleeha kekyawace irin first class d'innan Kana babbar yarinyace yar gidan babban mutun mai daraja, wanda k'asarmu ke al'fahari dashi
sannan taurarinta na haskawa tutarta na kad'awa kasancewarta ga ilimi ga asali ga haiba ga kyau uwa uba ga kud'i, sannan ga kwarjini bugu da k'ari yanayin aikinta yasa ta zama so popular
ita ba doguwa bace kana ba gajeraba, irin dai tsaka-tsakin nance,
tanada jikinta dai-dai da shekarunta yar sumul da ita, tana shek'i tamkar tarwad'a, kana tana da asalin gashi na fulanin asali,
wanda babu surki gashinta har bisa kafad'unta bak'ine sitik kana yanada yauk'i da sulbi,
duniyar Gombawa da ma sauran inda aka santa sunanta na haskawa kasan cewarta maikaciyar gidan radio ne yasa muryarta ta sanu wa Al'ummar gari musamman matasa domin shirinta na mushaƙata yanada farin jini, kana fuskarta ta kasance sanenniya sabida aikinta daya shafi sashinsu na TV,
Duk na miji mai rai da lfy in yaga Zaleeha sai yayi sha'awar ta zama matarshi kana in kasan gidan data fito dole kayi sha'awar had'a zuriya dasu sabida ko ba komai ana zatawa damuna sanyi,
yayinda ita kuwa Zaleeha ta tarkace babin maza ta watsa a gefe, bana ce da ita ruwan idoba, to amman har yau mahaifinta da Ya Ahmad tare da Ya Aminu sun gaza gane dalilin daya hanata tsaida gwaninta, duk da gashi k'anwarta mai bin k'aninta Zakariyya ma ta kai aure hakama mai bin mai binta itama ta fara girma uwa uba tayi karatunta har ta d'an kwana biyu da fara aiki.
cikin Jerin masoyanta kuwa harda Manager d'insu duk da ya bar abin a ranshi ganin yadda wasuma ke neman shiga ta wurinshi kana ga abokin aikinta Raveel bar irinsu Abdussalam.

Da sallama ta shiga cikin d'akin tace murya kafin a kai ga watsa shirin,
tana shiga ta samu Manager nansu zaune bisa kujera yana aiki,
zama tayi a kujerar gefenshi kana ta ajiye system enta sannan ta zaro woyarta,
aikinta ta farayi bayan kamar 4 minutes ya dago ya kalleta ido ya lumshe tare da shak'an k'amshin turarenta murya can k'asa yace.
"Yau ba gaisuwa ne?."
Jawo ababen aikin tayi ganin alamun ya gama kana tace.
"Oga na gaidaka baka ji bane."
hannunshi yasa ya jawo system in nata kana yace.
"Kawo in tayaki aikin."
ba tare da ta kalleshi ba tace.
"Ngd."
shi kuwa Oga ido ya kuma lumshewa kana murya can k'asa yace.
"Haram."
da sauri ta juyo ta kalleshi tare da cewa.
"Me d'in?."
mik'ewa yayi ya dawo gefenta kana ya fara harhad'a mata na'urorin sannan yace.
"Baliga tasa turare ta fita." shiru tayi sabida kunyar data rufeta daga nan shima bai kuma mgnaba,
har suka gama aiki,
sannan ya bata wani d'an k'aramin abu tare da turo mata laptop enta sannan ya kalli fuskar wayarshi yace.
"5:00 pm lokacin shirinki yayi, jeki sashin asashin watsa labaran ki had'a kawai ki tafi gida dare ya farayi."
mik'ewa tayi tare da gyad'a mishi kai, har taje bakin k'ofa taji ya kuma cewa.
"Ki dena sa turare in zaki taho kana da zakisa nik'ab da kin taimakawa wasu mazan daga fad'awa komar da baza'a kulasu ba."
kai ta gyad'a mishi kana ta fita,
kai tsaye sashin watsa shirye-shiryen su ta nufa tana shiga ta had'a program nata kana ta fito, bata koma cikiba kai tsaye ta nufi parking lot nasu ta shiga mota ta tafi,
a bakin Gate ta samu Raveel sarkin tsoka, cikin tsiya yace.
"Kiyi ta gudun masu k'afa da idanu daji da gani dai wataran sai gurgu ya kwasheki."
Harara ta watsa mishi tare da cewa.
"To sai me? mugu mai bak'in baki."
dariya ya kumayi kana yace.
"To ina ga dai Jinnul asheeq ne ya aure mana ke kowa yazo kice bakyaso sai na fara gulmataki a shirin Hasken Addini Baba malam ya taso min ke a gaba tunda kinƙi yin aure."
ganin zai b'ata mata lokaci ne yasa taja motarta ta tafi.
shi kuwa Rabeel murmushi yayi kana shiga motarshi.

ita kuwa Zaleeha
tana isa gida bayan tayi parking kai tsaye parlour Baba malam ta wuce tana mai jin fargabawa dan tasan kwanan zancen.



Abuja kuwa, k'arfe biyar dai-dai Amina ta shiga d'akin da aka meda Saifuddeen.
Domin ta bashi magungunan shi dayi mishi allura,
tana shiga tayi k'asa da kanta, har ta isa bakin gadon,
hannu tasa ta danna woni d'an abu sai kan gadon ya d'anyi sama yadda yana koncene amman kamar a jingine yake yake,
shi kuwa Saifuddeen jin motsin an d'an tab'ashi ne ya sashi bud'e idanunshi a hankali,
ido ya zuba mata ganin ta zubawa fuskarshi idanu,
amman ita bazata gane idanunshi a bud'e sukeba dan ya regesu sosai zakama yi zaton bacci yake,
shima kanshi ta tsakankanin gashin idanun nashi yake kallonta,
ita kuwa d'an hararanshi tayi kana ta kalli saitin mararshi sannan ta juyo ta kalleshi tare da tura baki tace.
"To Ayu sarkin jaraba, wasu in sun samu larurar daka samu basu sak'e mik'ewa da wuriba wasu kuma har abadan bazama su sake miƙewaba, amman da yake kai Ayune ana tab'aka kad'an kake mik'ewa ka razanani, to wlh allura zan maka a hannunka in ka kuskura, kamin irin na d'azu wlh bazan sake zuwa inda kakeba,
mutun baida lfy ma sai hegiyar fitina."
sai ta kuma kalleshi tare da cewa.
"Gashi Aunty Batulu tace min wai kai kurmane, to ni Amina yanzu taya zanyi in tasheka, bayan kuma nasan wannan abun naka ana tab'aka zai tashi kamar wani maciji."
Takaici ne sosai ya cika Saifuddeen a ranshi yake cewa.
"Kaji fitsarerriyar yarinya, tana k'are min tanadi, dan taga sirrina."
shiru yayi da tunanin nashi jin ta d'an zira mishi allura take a damtsen hannunshi
rumtse ido yayi da dan zafin allurar shigan ruwan allurar a jikinshi
saida yaji ta zare allurar sannan ya bud'e idanunshi dai-dai lokacin ita kuwa ta kalli fuskarshi.
ganin ya tsareta da idanune sai jikinta ya fara tsuma cikin yin k'asa da murya tace.
"Wannan matarshi ta shiga uku, mutun ana tabashi sai ya canza yanayi."
Sai ta kuma kalleshi tare da tsuke fuska tace.
"Gaka da jaraba gaka da k'aton joyst...!

A harabar asibitin kuwa, biyar dai-dai na yamma Su Ummi suka shigo asibitin,
kai tsaye office d'in Dr Aliyu Abban Farida da Ishaq suka nufa bisa jagorancin Dr Adnan.

Kana Ummi kuma da Hayatuddeen kuwa haggo inda Dr Batula yasa suka nufi inda take da alamun itama yanzu ta shigo asibitin,
da sauri suka nufi inda take.

Sukuwa su ishaq suna shiga cikin tamfatsetsen office d'in Dr bayan sun gaggaisa kana sun tambayi mai jiki,
Dr Aliyu ne yayi gyaran murya tare da fuskantarsu cikin nitsuwa yace.
"To Alhamdulillahi mun dai yiwa Saifuddeen iya abinda zamu iya mishi, sauran aiki kuwa yafi k'arfinmu tunda bamu da kayan aikin shi, so dole in dai anason yayi rayuwa cikin salama sai an fiddashi woje domin ceto rayuwanshi da mutuwar konce."
cikin tsananin kad'uwa da fargaba tare rashin gane me Dr yake son sanar dasu Ahmad ya zuba mishi idanu baki na rawa yace.
"Dr ban ganeba ban fahimci maganarka ba meya samu d'an uwana? me matsalar shi? yana raye kuwa? wani hali yake ciki? wani irin ciwone da babu kayan aikinshi anan k'asar tamu? , Dr zai worke kuwa!?."
gaba d'aya ya rude haka ya sashi jerowa Dr Aliyu tambayoyin a firgice.

Cikin taushin lafazi da iya magana tare da kwanatar da hankalin dangin mara lfy irin na sahihan doctors Dr Aliyu ya dafa kafad'an Abban Farida tare zuba mishi idanu kana a hankali yace.
"K.....!


*Ohohoho muje zuwa dai wannan lamarin littafin da salo na ban mmki da tsuma zuciya yake tafe, shauƙi bege ƙauna mai ratsa jikin maranci hmmm abin dai sai wanda ya bi littafin zai gane*



By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAKASA BA KASAWA BACE*

*PAGE 17*

NA

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



*Wannan shafi gaba ɗayanshi. Sadaukarwa ga Umar ibrahim Wambai, Allahu rabbi ta baka lfy dama dukkan al'ummar musulmai*


_Kada dai ku mance har yanzu Free page kuke samu, wanda ana gab da rufeshi ga masu akwai da niyar biyan kuɗin karantawa, turo katin Mtn na ɗari uku rak ta wannan no 09097853276. Ko kuma ka/ki turo ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, kana sai ka/koyi screenshot kids turo min shaidar kin biya ta wannan no 09097853276_


"Ka kwantar da hankalin ba komai, domin dukkan tsanani yana tare da sauk'i, kuma Allah ya sanar damu bai halicci ko wanni ciwoba saida ya halicci maganinshi, sai dai in har ba'a daceba ko kuma ba'a gano mgnin ba! amman ba ciwon da bashida mgnin."
gaba d'aya shiru sukayi domin kalaman Dr Aliyu ya sakarmusu fargabar da tasa jikinsu yin sanyi.
Shi kuwa Dr Aliyu juyawa yayi ya kalli Dr Adnan cikin kula yace.
"Naga alamun kamar wad'annan duk yayunshi neko, ina Mamanshi?."
a hankali Dr Adnan yace.
"Ummi da k'aninshi Hayatuddeen suna woje."
"Je ka shigo dasu." cewar Dr Aliyu,
shiru sukayi baki d'aya,
sai kuma Dr Adnan yace.
"Sir har yanzu mahaifiyarshi bata san sahihin raunin daya samuba,
muna tsoron ta sani kada ta shiga wani halin."
gyaran murya Dr Ayman yayi kana yace.
"Dole tasan matsalar d'anta dole ku duka Dr yayi muku bayani da kanshi, domin ciwonshi ciwone mai buk'atar tallafi da kulawan yan uwa da abokan arzik'i, ciwone da zai girgiza al'jihun ahlin shi, ciwone da d'ole sai an muku bayaninshi yadda za'asan hanyoyin kula dashi,
so kada ku damu jeku kirasu, Dr zaisan yadda zai musu bayani ba tare da ta firgitaba bare ta shiga wani mawuyacin hali."
jin haka yasa Ahmad mik'ewa jiki a sanyaye ya fita.
Jim kad'an suka kuma shigowa tare shi yana gaba Hayatuddeen na binshi a baya, kana Ummi na biye dasu.
inda ya tashi ya nunawa Ummi ta zauna kana Hayatuddeen ya tsaya gefenta.
Ganin haka Dr Ayman ya jawo wasu yan kujeru guda biyu ya baiwa Ahmad da Hayatuddeen. Bayan duk sun gaggaisa, Dr Aliyu ya fuskanci Ummi da kyau, cikin bada k'arfin guiwa yace.
"Maman Saifuddeen, kin shiga kin ganshi kuwa?."
cikin tsoron da tunda Ahmad ya kirata ta shigeshi cikin sanyin tace.
"Ban ganshi ba bai ganniba, bansan wani hali yake cikiba, dama akan Dr Batulu zata kaimu yanzu mu ganshi sai kuma akace kana kirana."
cikin bata k'arfin guiwa yace.
"Ba matsala zuwa anjima zaki ganshi."
ajiyan zuciya ta sauk'e tare da gyad'a kai alamun gamsuwa,
sai kuma tace.
"Dr me ya sameshi ne?."
gyaran murya yayi kana yace.
"Ki kontar da hankalin ki, zan miki bayanin matsalarsa dan ku shawarta yadda za'ayi jinyarshi."
kusan a tare sukace.
"Muna jinka Dr meke damunshi!?."
kanshi ya d'an kauda daga garesu kana ya bud'i baki a hankali cikin nitsuwa da taushin lafazi irin nasu na Doctors ta yadda bazasu firgita yan uwan majin yaciba yace.

*"Spinal Cord Injury (cutar laka)."*
da sauri Ishaq da Ahmad suka rumtse ido da tsananin k'arfi,
yayinda Hayatuddeen kuma ya zazzaro idanunshi woje, zuciyarshi sai harbawa takeyi a 360.
Ummi kuwa da bata gane menene hakanba bata wani damuba,
sai cewa tayi.
"Menene hakan?."
Dr Adnan kam tuni ya sunkuyar da kanshi yana jin wasu zafafan hawaye na tsastsafo mishi,
shiko Dr Aliyu fuskantansu yayi da kyau kana yaci gaba da cewa.
*"Spinal cord (Laka)* wani yanki ne na ci gaban k'wak'walwa da aka sauk'o da shi zuwa gadon bayan d'an adam domin sadar da sak'o daga k'wak'walwa zuwa ga sauran sassan gaggan jiki, da kuma daukar sak'o daga jiki zuwa k'wak'walwa."
numfashi ya fidda ganin duk sun nitsu suna sauraronshi kana yaci gaba da cewa.
"Ciwon laka wanda ake cewa *"Spinal Cord Injury (SCI)*" a turance matsalace da ke faruwa sakamakon raunata ko katsewar laka da ke cikin kwaroron k'asusuwan gadon baya saboda dalilai da dama...

Alamomin ciwon laka sun dogara ne da inda rauni/ciwon ya faru.

Misali, idan raunin ya faru a wuya,(Cervical Injury) to daga wuya zuwa k'asa ne zai sami matsala, wannan ya had'a da hannaye, gangan jiki, k'afafuwa, da dai sauransu!...

Haka nan idan raunin a dai-dai wani k'ashi daga k'asusuwan gadon baya ne, (Thoraxic) to daga nan har zuwa k'asa matsalar za ta faru."

Duk shiru sukayi kowa da irin fargabar dake ransa
Shiko Dr Aliyu cigaba yayi da musu cikkeken bayani cutar anitse yake cewa.
"Idan raunin daga k'ashin k'ugu ne, (Lumbar) to daga k'ugun har zuwa k'asa da 'yan yatsun Mutum za su sami matsala.

Bugu da k'ari, matsalolin ciwon laka sun sake dogara da girman ciwon/ raunin da lakar ta samu.
Gwargwadon raunin da lakar ta samu gwargwadon injury din da jikinsa zai sa mu.

Misali, a wani lokacin lakar tana tsinkewa gaba d'aya ne. A

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login